NAFEESAT 1-END

NAFEESAT Page 21 to 30

Fitowar ta kenan daga wanka taji wayan ta tayi ƙaran shigowar Text, kallo ɗaya tayi wa wayan ta ɗauke kai ta nufi gaban dressing mirror, zama tayi kan stool tana tsane gashin kanta, bayan ta gama sai ta ɗau handrayer ta soma busar da dogon baƙin gashin nata me tsananin santsi, sabida santsin sa ne ma ba ta yin kitso sai dai ta riƙa gyarawaAjiye handrayern tayi bayan ta gama ta soma shafa Lotions ajikin ta, tana gamawa tayi Light makeup a baby face ɗin ta, sai ta miƙe ta ciro kayan ta tasaka

Doguwar riga ce robber kalan ruwan hanta, babu kwalliya a rigan ko ɗaya sai dai wuyan V yake dashi wanda aka saka masa bakin less white colour, haka ma dogon hannun a ƙarshen an saka masa bakin less, Hula ta saka fari wanda ya kasance na rigan ne, tayi kyau sosai kasancewar ta kyakykyawar

Wayan ta kawai ta ɗauka ta fito Parlour.

       Fadila na zaune tana cin abinci at the same time tana latsa wayan ta

She Sit on the One sitter next to Fadila on the Two sitter

Ɗan kallon ta kawai tayi sai ta ɗauke kanta ta mayar kan plasma t.v dake aiki babu me kallo, shiru tayi na ɗan wani lokaci sai kuma ta ɗago wayan ta ta soma latsawa

Da text ɗin da ya shigo wayan ta ɗazu ta fara cin karo, har zata wuce kuma sai ta ga kamar da number akayi mata Text ɗin wanda ada azaton ta MTN ne su kayi mata

Buɗe wa tayi da mamaki take kallon text ɗin, har sake murza idanuwan ta tayi tana sake ƙura manyan idanun nata, jikin ta na rawa ta soma karanta wa:

_”Aslm alaikum ya ke kyakykyawa abar so ga kowa, za kiyi mamakin ganin wannan text ɗin nawa aduk lokacin da ya riske ki, amma ba abun mamaki bane domin an ce me son ɗan tsuntsu shi ke bin sa da ji fa, Ɗahira na daɗe da ƙaunar ki cikin zuciya ta, sai dai har yanzu na kasa fitowa fili na sanar miki, ba don komai ba sai don ban san ya zaki amshe Ni a matsayin Masoyi ba, but know that I love you and I will continue to love you until my breath goes out, I Love You .. I love You with all my heart.”_

        _MASOYIN KI✍️_

           Ta maimaita text ɗin ya fi sau biyar, gaba ɗaya ta ruɗe domin abin da bata taɓa gani bane a gare ta, tunda take babu wanda ya taɓa nuna yana son ta kuma babu wanda ya taɓa tura mata text da sunan masoyin ta, hakan ne ya saka ta shiga wannan ruɗun tare da bugawar zuciya me tsanani

Zumbur ta miƙe ta nufi ɗakin su

Fadila tabi bayan ta da kallo cike da mamakin sauyawan ta lokaci ɗaya, amma sai dai bata ce komi ba ta maida hankalin ta kan wayan ta.

      Tana shiga ta nufi kan gadon ta ta zauna, sake ɗago wayan nata tayi ta sake karan ta text ɗin

“Anya wanda ya turo text ɗin nan ba mistake yayi ba?” Tafaɗa cikin sanyin murya tana bin wayan nata da kallo

Ƙure Numban tayi da idanu ko za ta san me irin shi but ko kaɗan bata taɓa ganin ma irin Numban ba, domin kuwa sabon Numban da MTN suka fito dashi ne me 091

Har ta latsa da ninyan kira taji ko wane ne sai kuma ta yanke da sauri don bata san me zata ce ɗin ba ko da an ɗauka, zuciyarta ta bata shawaran kar ta sake ta kira wataƙil mistake ne aka yi, kuma be kamata ta kira ɗin ba, da haka ta’ajiye wayan ta kwanta tana tsira wa waje ɗaya idanu cike da tunani

Da sauri kuma ta tashi zaune tana faɗin, “amma kuma ya kira suna na ai, Of course I am. This text is for me, but who is it?”

Duk yanda taso yin tunanin gano wanda zai iya mata amma ta kasa, koma wa tayi ta kwanta tana ajiyan zuciya.

           ⚫⚫⚫

  Yana kwance saman kujeran sa yana faman latsa wayan sa yana murmushi

Wayan ce ta soma ringing hakan ya saka ya dakata da abinda yake yi yana kallon baƙuwar Numban da aka kira sa, shiru yayi na ɗan wani lokaci kafin yayi peacking call ɗin ya saka a kunne

Daga can ɓangaren muryan mace ce ta doki dodon kunnen sa

“Aslm alaikum”.

“Wa’alaikis salam”. Slowly he gets up and sits up

She smiled and said, “Do you know who Dr. Al’ameen Abubakar Al’ameen is?”

Baffa da yayi tsimi yana sauraron muryan ta sai be ce komi ba

Hakan ya bata damar ci gaba da faɗin, “My name is Dr. Ayush Abdulkarim and I work at your Family Hospital.” Sai kuma tayi shiru tana tunanin abinda zata ce

Baffa yace, “to Allah yasa dai lafiya? But I don’t know you.”

She smiled and said, “Yes, you will never know me because I have just started working at the hospital, but idan har ka bani dama zan iya bayyana maka kai na domin mu san juna, tunda ina son alaƙar mu tayi nisa ne, that’s why.” so I asked for your number and I called you “.

Shiru yayi cike da mamakin ta

“To me zai sa ta so ƙulla alaƙa dashi?..”

Be gama guntun tunanin sa ba ta katse sa da faɗin, “I’ll meet you tomorrow insha Allah, I’ll come to your office. Byee Take care.” Bata jira me zai ce ba ta kashe wayan

Shi kuma ya ciro wayan yana kallo, ya jima a haka yana tunani kafin ya’ajiye wayan ya miƙe ya shige toilet don ɗauro alwala.

⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫⚫

       Dariya suka kwashe dashi har da tafa wa

“Wow gaskiya kin yi ƙoƙari Ayush, amma kina ganin zaki iya jawo hankalin shi gare ki har ya manta da wancan shashashan?”

Murmushi me ma’anoni da dama Ayush ta saki tana kallon Shakira tace, “ke dai ki zuba idanu ki gani, da zaran mun haɗu ma zan sanar masa ina ƙaunar sa don ma ya sani tun yanzu”.

Dariya Shakira tayi tace, “Thanks.. sai kuma mu jira muga shirin namu zai yi aiki ko kuwa..”

“Idan ma bazai yi ba sai mu sauya salo”. Ayush tafaɗa itama tana dariyan

Jinjina kanta Shakira tayi cike da jindaɗi sannan tace, “Is it tomorrow when we meet?”

“Yeah insha Allah”. Cewar Ayush tana ɗaukan jakan ta sannan ta buɗe murfin motan

Daga nan sallama su kayi ta fito cikin motan, ita kuma Shakira taja tabar ƙofar gidan su Ayush ɗin

Tana nan tsaye tana ɗaga mata hannu har ta ɓace ma ganin ta, murmushi ta saki tana faɗin, “Uhmm Dama ta biyu kenan, yanzu komi zai soma min daɗi, tabbas Buri na zai yi saurin cika, da wannan shirin naki Ni kuma zan cika tawa Burin”.

Dariya tayi ta shige gidan su

Babban gida ne me sasa biyu, na farkon shi ne na mahaifin ta, inda akwai ɗakuna Huɗu da kichen a bakin ƙofan gidan; sai kuma bayi dake can ƙuryan sasan wanda aka rufe sa da fale-fale

Ƴaƴan Baban su su goma ne maza da mata kuma itace ta Biyar, sannan duk mahaifiyar su ɗaya.

                 Ɗayan sasan kuma Ƙanin Baban su ne ke zaune da matar sa, yaran sa shida shima maza da mata.

            Ba wani kuɗi suke dashi ba amma suna da rufin asiri dai-dai gwargwado, mahaifin su yana ɗauke musu duk wani nauyi da ya rataya akan sa

A cikin ƴaƴan sa mata Ayush ce kaɗai tayi karatu me zurfi har matakin Doctoring, Wanda hakan shi ne burin ta, don tasan shine hanya ta farko da zata iya bi wajen cin ma babban burin ta, wato auren me kuɗi

Tun tana yarinya ta taso tana jin labarin Familyn Dr. Al’ameen Abubakar Khabeer Cindo, kuma sosai take jin labarin Hospital ɗin sa da ya shahara a faɗin Nigeria, wanda idan har za’a yi kwatance, to, da shi ake yi. Wannan dalilin ne ya saka ta ɗaukar ma kanta alƙawarin sai tayi aiki a cikin asibitin sabida ta nuna wa ƙawayen ta da ƴan uwanta tafi su

Zuwan ta asibitin da yanda taga tsaruwan Hospital ɗin tare da Familyn gaba ɗaya sai tayi sha’awar kasancewar ta cikin FAMILYN, burin ta a yanzu shi ne ko ta halin ƙaƙa ta shiga gidan itama ta zama ɗaya daga cikin familyn da su kayi Suna a faɗin Nageria; kuma suke ji da kuɗi da Izza

1 2 3 4 5 6 7Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button