RAUDHA 1-END

RAUDHA Page 51 to 60 (The End)

Waro lumsassun idanuwan ta tayi a kansa tana me mamakin abinda yayi mata. Cikin haushin sa tace, “meye haka?” Ta ƙare maganar tana son sauka daga jikin saBe hana ta ba, don shima be san sanda ya janyo ta ɗin ba, kawai dai yabi umarnin zuciyar sa ne, so kawai yake yi yaji ta a jikin sa, be iya ce mata komi ba har ta juya ta bar wajen itama batare da ta sake furta masa komi ba

Ɗakin ta tawuce ta faɗa kan gado, a ranta sosai take mamakin abinda Ray yayi mata, tsaki taja tana birkita kwanciyar ta

“Ko meye ruwan sa dani ne wai? Ni fa na tsani takura a rayuwa ta”. Tafaɗa a fili tana sake jan wani dogon tsakin

Ko kaɗan ba ta son yanda zuciyar ta take damun ta da tunanin sa. Hannu ta saka ta janyo rigan ta tana shinshina, gaba ɗaya ƙamshin sa ya addabar mata hanci, miƙe wa tayi ta hau cire kayan a ranta tana mita, sauya wani kayan tayi ta koma tayi kwanciyar ta ta hau charting da Ƙalby ɗin ta.

      Da dare suna zaune gaba ɗaya a Parlour bayan sun gama cin abinci, Uncle yace da Rayyan “gobe kace zaka tafi ko?”

“Eh Uncle”.

“To sai ku wuce da ɗiya ta tunda itama goben zata tafi”.

“To Uncle”. Ray yace hakan cike da murna a zuciyar sa

Ita kuwa RAUDHA tamkar ma bata ji me ake cewa ba, Game suke buga wa ita da Abubakar

Sai da Uncle ya Kira sunan ta yana cewa, “ɗiya ta gobe zaku wuce tare da Captain, zuwa gobe insha Allahu zan baki kuɗi ku fita da Abubakar ki siya duk abinda kike so ko?”

Murmushi tayi tace, “Uncle ni ba sai ma na siya komi ba”.

“A’a kina nufin ki koma haka babu tsaraba?”

Ammee itama tace, “ai hakan ma bazai yiwu ba, nima zan ƙara miki da nawa, tunda naga ba kya son kayan ku na Hausawa, Ni dai su na siyo miki, da fatan dai zaki saka ko ɗiya ta?”

Murmushi RAUDHA tayi tace, “eh mana Ammee zan saka insha Allahu”.

“To shikenan, zuwa gobe za’a amso daga ɗinki, duk na rigada na bayar an ɗin ka miki”.

“Nagode Ammee sosai”. 

“Ɗiya ta babu godiya a tsakanin mu, ai mu mun ji daɗin hutun nan da kika yi mana”.

Zannurain ya amshe zancen da faɗin, “da fatan dai zaki sake ziyartan mu? ba wai da kin tafi kin manta damu ba”.

Dariya tayi tace, “Ni ai ba don ku zan zo ba, don Uncle da Ammee zan sake zuwa, tunda ku ko tsaraban ma babu wanda yace zai bani a cikin ku”.

Gaba ɗaya suka yi dariya har Ray dake sauraron su yana latsa wayan sa

Faruk ne yace, “kar ki damu Lil Sister, mun miki tanadin tsaraba sai zuwa gobe kowa zai baki”.

Murmushi tayi tace, “Thanks Yaya Faruk”.

      A haka dai hiran nasu ta kasance, inda daga baya kowa ya wuce ɗakin sa don kwanciya

RAUDHA na tsaka da saka kayan barcin ta, taji ana mata Nocking a bakin ƙofa, tsayar da abinda take yi tayi tana kallon ƙofan, sai kuma taƙarisa saka doguwar rigan da sauri, don a tunanin ta Ammee ne taje ta buɗe mata, saɓanin tunanin ta sai taga Faruk ne, waro idanu tayi a kansa tace, “Yaya Faruk kai ne?”

“Eh Ni ne Ƙanwa ta”.

“To me kake buƙata?” Ta sake jeho masa tambayar

“Magana zamu yi Sister, amma na rasa hanyar da zan bi don sanar miki, yanzu kuma naga dacewar na faɗa miki tun yau tunda gobe zaki tafi”.

Murmushi tayi tace, “kai Yaya Faruk, to shigo mana”.

Ta matsa mishi a hanyar ya shiga, sannan ta mayar da ƙofan ta rufe.

Kan kujera ya zauna, itama ta zo ta zauna a gefen sa tace, “ina jin ka Yaya, wani magana ne zaka faɗa min har ka kasa sanar min sai a yanzu?” 

Idanun sa a kanta yayi murmushi yace, “ba abu ne me sauƙi ba shiyasa na kasa sanar miki, sabida wlh kullum na tunkare ki da maganar sai inji nauyin faɗa, ina son ki RAUDHA! ina ƙaunar ki matuƙa”.

Waro ido tayi tana bin sa da kallo, sai kuma tayi dariya tace, “Yaya Faruk kenan, Allah ka bani dariya..”

“Sabida ban cancanci na so ki ba ko?” Ya katse ta da faɗan haka yana me tsare ta da ido

Sosai taji wani iri a kallon da yake mata, idanun sa iri ɗaya dana Ray, shiyasa ko kaɗan ba ta son suna kallon ta. kau da kai tayi tana cewa, “yanzu dai mu bar zancen nan Bro, dare yayi ina jin barci”. Ta ƙare maganar tana shirin tashi

Riƙe mata hannu yayi, hakan yasa ta dakata daga tafiyan da tayi ninya

“Please Sister, ki bani amsa ta don Allah, wlh ina ƙaunar ki, tun sanda muka zo gidan ku na kamu da soyayyar ki, na kasa sukuni gaba ɗaya sai yanzu da na samu na faɗa miki”.

Numfashi taja kafin ta juyo tana kallon sa tace, “meyasaka kake son yaudaran kanka ne Faruk? Kar ka manta Na san alaƙar ka da Suhaima”.

Cikin marairaice fuska yace, “Yanzu ke nake so ba ita ba, wlh ina matuƙar ƙaunar ki, ƙaunar da ban taɓa wa Suhaima ba, kin ga kuwa ke Yakamata in aura ba ita ba”.

“Kar ka ja maganar da tsaho, bazan so ka ba Yaya Faruk, ina da wanda nake ƙauna a halin yanzu”.

Zai yi magana ta katse sa da faɗin, “Please ka fita min a ɗaki ina jin barci”. Ta ƙare maganar tana janye hannun ta tabar wajen

Shiru yayi yana bin ta da kallo, sai kuma ya tashi ya nufi ƙofa, har ya buɗe zai fita kuma yaja ya tsaya, kallon ta yayi yace, “Bazan haƙura dake ba RAUDHA, zan bi duk ta hanyar da ya dace don mallakar ki”.

Juya wa yayi ya fice batare da ya jira jin ta bakin ta ba, wanda itama bata yi ninyan maganar ba.

        Da fitan sa suka ci karo da Ray da ya fito daga Parlour ɗauko ruwa a gora, mamaki ne ya kama Ray ganin inda ya fito, take wani irin faɗuwar gaba ya riske shi, cikin sauri yace da shi, “Kai daga ina ka fito?”

Shafa kansa Faruk yayi yana sunkuyar da kai

“Ba da kai nake magana ba? Daga ina ka fito? Yayi maganar cikin kakkausar murya cike da fushi

Sosai Faruk ya tsora ta da ganin yanayin nasa, cikin sauri yace, “Brother daga wajen RAUDHA na fito, lafiya?”

Mari ya wanke shi dashi, ya saka hannu ya finciki wuyan rigan sa, cikin tsananin fushi da har idanun sa sun kaɗa yace, “me kaje yi ciki? Me kuka yi?”

Mamaki sosai ya kama Faruk da abinda Yayan nasa yayi masa, wanda be taɓa tunanin haka a gare sa ba, idanun sa kawai yake kallo yana mamakin tsantsan kishin da ya hango a tattare dashi. Cikin sanyin murya yace, “babu kom..”

Be bari ya ƙarisa ba ya daka masa tsawan “ya bar gaban sa”

Da sauri Faruk ya wuce yayi hanyar ɗakin sa, yana me sake mamakin yayan nasa, “kar dai ace shima son ta yake yi?”

Ray kuwa na tsaye a wurin zuciyar sa na tafarfasa, sosai yake jin ƙuna a ransa, sabida abinda zuciyar sa ke raya masa, riƙe kansa dake sara masa yayi, sai kuma ya juya ya nufi ɗakin RAUDHA

Har ta kwanta taji an hankaɗo mata ƙofa, da sauri ta ɗago kai tana kallon Ray da ya nufo inda take, idanu kawai ta zuba masa tana kallon sa tamkar zaki

Gaban ta ya ja ya tsaya yana bin ta da kallo cike da tsantsan fushin da ya nuna a fuskar sa, cikin kaushin murya yace, “keee uban me ya shigo da Faruk cikin ɗakin nan?”

Mamaki maganar nasa ya bata, sai ta miƙe zaune don ta kalle sa da kyau, cikin taɓe baki tace, “kai kuma asuwa da zaka tambaye Ni abinda ya kawo sa?”

Sosai ransa ya sake ɓaci da maganar ta, cikin tsawa yace, “wato kina nan kina halin ki ko? Ke daƙiƙiyar ina ce da baza ki taɓa sauya wa ba? Wato iskancin naki ya tashi kan wasu ya koma kan ƙani na, ƙani na kike bi?”

Sosai RAUDHA tayi mutuwar zaune da jin zantukan sa, sai kawai tabi sa da ido domin ta kasa ko ƙwaƙƙwaran motsi bare ta furta wani kalma, duk da kuwa laɓɓan ta sai motsi suke yi, sai dai baƙin cikin zantukan sa yasa ta kasa furta komi, kafe sa tayi da idanun ta ko ƙyafta su ba ta yi

1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button