Al-Ajab

Tirkashi: Matashi ya sheƙa lahira yana tsaka da gwada ƙwazonsa da mace a Otal

Rundunar ‘yan sandan Jihar Ondo ta ce ta fara bincike akan mutumin da ake zargin ya na tsaka da lalata da wata mata a Otal ya rasa ransa a jihar, The Punch ta ruwaito.

 

An tattaro bayanai akan yada Lanre, mamacin ya zage damtse yana ta lalata da matar a wani otal da ke garin Ondo ranar Laraba da yamma.

 

Har yanzu ba a bayyana suna ko kuma wani bayani dangane da matar ba. Wata majiya ta bayyana cewa:

 

“Matar ta sanar da jama’a ne bayan gane cewa mutumin ya rasu bayan ya kammala wanka daga gama lalatarsu da misalin karfe 9 na daren Laraba.

 

“Ihunta ne ya ja hankalin manajan otal din wanda daga bisani ya gayyaci ‘yan sanda daga ofishinsu da ke Enu-Owa don bincike.”

 

Kakakin rundunar ‘yan sandan, Mrs Funmilayo Odunlami ta ce mutuwar tasa ba ta lafiya lau bace, yayin da aka tuntubeta don jin bayani.

 

Amma a cewarta, yanzu haka ‘yan sanda sun shiga lamarin dumu-dumu don gano asalin silar mutuwarsa. An tattaro bayanai akan yadda aka dauki gawar mamacin, inda aka kai ta ma’adanar gawa da ke jami’ar Kimiyya da ke Ondo.

 

 

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button