Lu’u Lu’u 44

Da iya k’arfinta cikin siririyar muryar da Allah ya hore mata ta kwamtsa k’ara tare da dafe kunnuwanta ta durk’ushe a wurin, hannayenta bibbiyu ta kai kan gawar Musail ta fara jijjigawa da iya k’arfinta, da sauri su Bilkees da mahaifiyar Bukhatir suka rik’eta suna k’ok’arin jayeta daga nan, wani harbin bindigar suka ji hakan ya tilasta ma kowa tsayawa cak a inda yake yana zazzaro ido.
Zafreen ce rik’e da bindiga da alama a kid’ime take kuma ta sha wani abun, dan idonta sunyi jajir sai layi suke, kan Ayam ta nuna da bakin bindigar nan tace “Kar wanda ya motsa a inda yake, idan ba haka ba sai na harbeta.”
Cak kowa ya k’ara tsayawa har da Umad dake durk’ushe kan gawar Musail, cike da kulawa yake kallonta yana son hango ta yanda zai farmaketa ba tare da kowa ya ji rauni ba, sake jinjina bindigar tayi tace” Na ce kowa ya tsaya, kar wanda yayi yunk’urin wani abu, idan ba haka ba zan kasheta.”
Matsowa ta dinga yi sannu sannu tana yi tana kallon gabanta da bayanta, saida ta matsa har daf da Umad sannan tace” Ka ciro min kambun dake kanta.”
Da mamaki ya kalleta hakan yasa a tswace tace” Na ce ka ciro min kambun, ko kuma in tashi kanta da bindigar nan.”
Cikin rud’ewa Juman tace” Kin ga Zafreen, ita f…”
A tsawace tace” Shiru, shiru malama.”
Umad ta sake kallo tace” Maza ka yi abinda na ce.”
A hankali ya fara takawa ya nufi Ayam data tsaya kan k’afafunta amma hawaye na mata ambaliya, hannunshi ya kai ya d’auko kambun dake kanta wanda ya mata kyau sannan ya mik’o ma Zafreen d’in, karb’a tayi da sauri kamar zata had’a da hannunshi sannan ta saka a kanta, kecewa tayi da dariya sannan ta sake cewa “D’auko sark’ar ka saka min.”
Cike da taka tsantsan ya sunkuya ya d’auki sark’ar sannan ya mik’o mata, sake nuna Ayam tayi da bindigar tace “Ka saka min na ce.”
Gyara sark’ar yayi sannan ya saka mata a wuya, zai ja baya ya bata wuri saboda ganin Haman sun dawo daga neman maharbin nan, da ido ya mishi alamar su nutsu sannan suyi koma da baya su yi wata dabarar da zata sa kowa ba zai jikkatu ba, yana cikin masa magana da ido kawai ya ji Zafreen ta shak’o wuyan rigarshi cikin halin maye tace “Na ce ina sonka…ina son ka ama..babu wanda ya kulani, to na ji kuje ku rayu kai da ita, amma ka ga yanzu ni ce mai mulki, ni ce saraunyar Khazira yanzu, hatta…da mahaifinka ma..a k’ark’ashina yake yanzu, dan haka…”
Ba tare da tunanin komai ba ta d’ora labb’anta a na shi labb’an, kafin ya ankara har ta tsotsi bakinshi sannan ta raba bakinsu tana mashi wani mayataccen kallo tace” Ina son…”
Bindigar ta d’ora a cikinshi da niyyar ta harbeshi Ayam da ita duk su rasa, yana jin ta d’ora bindiga a cikinshi yayi sauri cikin dabarar fad’a ya juyar da hannunta zuwa cikinta, kafin ta ankara da ina bakin bindigar yake ta danna kunamar, hakan yasa ta tashi kanta da bindigar, take ta k’walalo ido ta jimk’e rigarshi sosai, sannu sannu ta fara sulalewa sai gata k’asa kwance cikin jini.
Jaye jikinshi yayi hakan ya sake haifar da turmutsutsu, a nan ma dai yau saida aka kira ambulance da suka tafi da gawawwakin, saidai ko ba komai yanda Musail ya cika da kalmar shahada haka gawarshi ta samu mutuntawa har da zubar hawayen talaka, inda aka kaisu mutuwa kafin gari ya waye a kaisu gidansu na gaskiya, mutane kuma suna ta cecekucen waye ya kashe sarki Musail? Wanda ba’a gano hakan ba, saidai ko ma waye an tabbatar ba zai wuce da hannun Zafreen d’in ba.
Juman da Ayam sun gigice musamman Ayam da ke d’auke da jinin mahaifinta a jikinta, Juman kalamai d’aya take ta fad’a a bakinta har yanzu shi ne “Mah ko gafararsa ban rok’a ba, ban nemi yafiyarsa ba akan abubuwan da na masa, ya sadaukar da rayuwarsa a kai na da ‘yata, ya zauna da mak’iyanshi da murmushi a fuskarshi, na nuna masa k’iyayye ya had’e ya shanye Mah, ya zanyi yanzu? Ya zanyi Mah? Ina son mijina, wallahi ina son mijina.”
Ayam kuma wuri d’aya kawai take kallo sai in ta k’yabta da k’yar, hakan yasa Bilkees ta kalli Umad tace” Ka je da ita d’akinta, ka kwantar mata da hankali, ni zan zauna da Juman a nan.”
Jinjina kai yayi sannan ya kama hannun Ayam bata ma san yayi ba har suka je d’akinta, zaunar da ita yayi bakin gado ya shiga ban d’aki, ruwan wankan ya had’a sannan ya fito ya kamata, saida ya tsayar da ita tsakiyar ban d’akin yace” Ki yi wanka ga ruwa nan, idan kin kammala ki d’aura alwala.”
Shiru kamar bata san yanayi ba, dan haka ya juyo ya fito daga ban d’akin ya rage kayan jikinshi sannan ya koma.
Duk da ta fahimci singlet da dogon wandonshi ne a jikinshi, amma sam hankalinta ba nan yake ba, musamman bandejin dake nad’e tun daga kafad’arshi zuwa hannu wanda Haman ya cire mishi harsashin da aka harbe shi ranar nan, duk d tana jin kamar ta tambayeshi, amma ina gaba d’aya komai na ta ne ya tsaya.
Gabanta ya tsaya k’ik’am ya fara zare mata zip d’in riga, da a hayyacinta take ba zata tsaya ba a yanda suke d’in nan, amma sai gashi ya rabata da komai ya rage daga pant d’inta sai bras farara k’ar da su, jawota yayi jikinshi kamar ya rumgumeta sannan ya b’alle mata bras, tana jin haka wasu hawaye masu zafi suka taho mata har suka sauka kan kafad’arshi.
Cire mata yayi sannan ya sunkuya ya zage mata pant d’in, shi kanshi sai yake jin wani nauyi nauyi, watak’ila dan ko waccen ranar bai wani ganta sosai ba ne, yana ajiye kayan ya jata zuwa k’asan shower ya sakar mata ruwa masu d’umi.
Wanka ya mata da sabulu tas sannan ya d’aura mata towel suka fito har yanzu tana nan kamar gunki, kan gadon ya zaunar da ita sannan ya d’auko man da ya gani ya zo ya fara shafa mata, jefi jefi ya kan kalli fuskarta, amma yanda idon nan nata masu abun al’ajabi suka yi ja sai yake jin tsoron kallonsu, gashi shi take kallo bata ko k’yabtawa sai an d’auki lokaci.
*Alhamdulillah.*
The post Lu’u Lu’u 44 first appeared on 2gNovels.com.ng.
[ad_2]