Lu’u Lu’u 14

*14*

 

Akan babban teburin cin abincin mai d’aukar mutane goma sha biyu, Bukhatir ne zaune akan kujerar tsakiya dake iya fuskantar kowa, a tunaninshi sarki Wudar zai zauna a nan, amma sai gani yayi ya ja kujerar kusa da shi ya zauna, Umad kuma ya zauna kan kujerar da ke fuskantar Bukhatir d’in.

Haka kawai had’uwarsu ta farko ya ji ya tsani matashin, wani cin magani da yake da wani jiji da kai shi dole ga d’an sarki, hakan sam bai masa ba.

Mutane shida ne a wurin gaba har da mataimakin sarki da kuma na hannun daman shi, inda fadawanshi masu tsaronsa suke bayanshi d’an nesa kad’an tsaye, shi ma Bukhatir dattijon nan ne a bayanshi tsaye.

Mata biyu ne ke zuba musu had’add’e kuma lafiyayyen abincin da aka girka dan su, sarki Wudar ne ya kalli Bukhatir cikin rad’a dan dama a kusa suke yace “Me zai hana ka gabatar mana da ita?”

Wani shak’iyin murmushi Bukhatir yayi yace “Yallab’ai ina fata dai ba ka zo da tunanin zaka tafi da ita bane ko?”

Da sauri Wudar ya kalleshi sai kuma ya sunkuyar da kanshi, numfashi ya sauke yana tunanin me Bukhatir ke nufi kuma? Ko ya manta da yarjejeniyarsu ne? D’aga kan shi yayi ya kalleshi cikin sassauta murya yace” Ka fad’a min adadin farashinka? Zan biya ko nawa ne.”

Wata dariya Bukhatir ya tintsere da ita ba tare da sanin yayi ba, ganin kowa ya maida hankali a kan shi har da Umad daya kalleshi cikin jin haushi yasa ya tsagaita, kallon sarkin yayi a cikin rad’a shi ma yace” Yallab’ai, me yasa kayi tunanin tana da farashi a gurina? Ai ni ma na karb’i gayyatarka ne dan na tambayeka farashinka, dan bana so ka d’auka ni ma ci amana ne, ka taimaka min wajen samota kuma na juya maka baya.”

Irin kallon nan mai saka fad’uwar gaba sarki Wudar ya masa, fuskarsa a tamke yace” Bukhatir kasane zaka dinga fad’a min, idan ba haka ba yayan mahaifinka zai san duk abinda kake shiryawa a kan shi, haka zalika zai samu labarin bayyanar jikarshi a k’asarsa.”

Wata harara harara Bukhatir ya wurga masa sai kuma ya shiga rarraba ido yana tunanin lallai fa komai nasa zai lalace idan har Emir ya san da batutuwan nan.

Iska ya huro tare da jan plate d’in abincin gabanshi ya kalli sarki Wudar yace” Na yarda zaku gana, amma ba zaka tafi da ita ba, daga baya zamuyi magana akan wanda ya dace ta zauna tare da shi.”

Kafin sarki Wudar yace wani abu Bukhatir ya kalli dattijon dake bayanshi, da ido kawai ya masa alama, amsawa yayi da girmamawa ya nufi wani sashe na daban.

Umad dai na zaune yana kallon komai a tsanake yana kuma d’ora komai a kan ma’auni, yasan mahaifinshi na neman Zafeera, amma yasan dan ya d’auki fansa ne a kanta kamar dai shi, amma bai san dalilin da yasa yake zafafawa ba sosai haka, duk da dai yanzun ba wai ya fahimci akan me suke magana ba, amma yana ji a jikinshi batun ba zai wuce na son had’uwarshi da Zafeera ba, tunda har a bincikenshi sunan Bukhatir ma ya fito a cikin masu son samunta kuma su mallaketa, to baya raba d’ayan biyun cewa zasu had’a k’arfi da k’arfe ne dan ganin sun samota sannan su muzgunawa mahaifinta, dalilin da yasa Bukhatir kuma yake son kassara sarki Musail d’in wannan ne kam bai sani ba sai nan gaba.

K’wasss! Sautin takalmin k’afarta ya isar musu da sak’on zuwanta farfajiyar, wanda dama yake a k’age da son ganin zab’abb’iya, da ma wanda sam bai da niyyar kallon b’angaren kamar Umad saida suka samu kan su da juya kusan a tare.

Take yanayin fuskarshi ya canza daga had’ewar nan zuwa wani sassauk’an murmushin da baisan sanda ya kubto ya taho masa ba, inda zuciyarsa ta shiga masa wani irin sanyayyan duka tana sanar da shi ta iso, jikinsa kuma gaba d’aya wani karsashi had’e da kasala ya ji suna saukar masa, a tausashe ya juyo da kanshi yanda babu wanda ya fahimta, murmushi ya sake yi bayananne tare da shafa sumar kan shi, a hankali a kan labb’anshi ya furta ” *Zakanya*.”

Tun daga k’asa har sama sarki Wudar yake k’are mata kallo, bakinshi bud’e kamar zaka fad’a a guje, kallo d’aya zaka masa kasan tabbas yana cike da farin cikin daya shekara da shekaru bai samu kan sa a ciki ba, wani b’oyayyan murmushi ne ke fita a fuskarshi mai kama da lallausan dariya.

Ta b’angaren Bukhatir ma haka yake, duk da shi d’in ya ganta ba kamar sarki da sauran jama’ar ba, amma dai haka ya kafeta da ido har saida ta k’araso dattijon nan ya ja mata kujera ta zauna.

Tsarguwa ta fara yi dan kallon da mutanen wurin ke mata tana ji kam a shari’ance ma ya wuce k’a’ida duk da bata da madogara mai kyau, saidai bata nuna hakan ba sakamakon ganin yallab’ai Umad, tsura masa ido tayi tana kallo amma shi kan shi a k’asa, kamar ta k’wala masa kira tace “Yallab’ai.”

Sai kuma muryar Bukhatir ta katseta sanda yake nunawa sarki Wudar ita yace “Yallab’ai ga Zafeera.”

Wani mahaukaciya kuma siririyar dariya sarki Wudar ya dinga yi yana kallonta kamar marar gaskiya yana fad’in “Ehehehehe… Hahahahaha… Ehemmm, na gan ta, na gan ta Bukhatir, fiye ma da yanda ake fad’a.”

Kallon Zafeera Bukhatir yayi ya nuna mata sarki yace “Ma pr茅cieux, ga yallab’ai sarki Wudar, ga kuma d’an sa, wad’annan mak’arrabansa ne sun zo ganinki.”

Wanda ya nuna yace mata d’an sarkin ta bi da kallo galala, amma har yanzu idon shi na kallon farantin gabanshi, cikin larabcin parsi tace “Dama d’an sarki ne?”

Baki wangale sarki yace “E, d’ana ne.”

D’agowa yayi ya kalli mahaifin na shi, d’an tsakin jin haushi yayi a ranshi yana ayyana kar mahaifinshi la ya zama sakarai a gabanta fa, dan ya ga yanda suke k’arewa da canal Jacob.

Juyawa tayi ta kalleshi cikin hatsari suka had’a ido, k’yabta ido tayi sau d’aya sau biyu sau uku, shi kam dan ya fahimci me take fad’a sai ya shiga yin zooming fuskarta yana kallon idon na ta da gashinsu yayi mata wani zar-zar-zar, ganin bai fahimci komai ba sai kawai ya d’auke idonshi ya d’auki cokalin gabanshi.

Cikin jin haushi Ayam ma ta d’auki cokalin gabanta duk da babu komai a cikin farantin ta, turo baki tayi a dole ita ta ji haushin ya k’i kulata ta shiga caccakar farantin na ta, kamar sub’utar baki a harshen italien tace “Wai me ya kawoku nan?”

Dukansu zuba mata ido sukayi, saidai babu wanda ya fahimci me ta fad’a sai Umad, shi ma yana kallonta da ya ga kowa ita yake kallo sai kawai ya d’auke kan shi, kamar wanda baya son yin maganar a harshen data masa magana shi ma yace “Kar ki nuna musu kin sanni, kiyi harkan gabanki kawai.”

Wani irin kallo ta masa irin mamakin nan a zuciyarta tace “Kutttt!”

A zahiri kuma farantin ta ta dinga kallo da ake zuba mata abinci amma cokalin a hannunta tana t daddaga shi a teburin wanda hakan yasa duk mutanen suke kallonta, ita ma mayar mi shi tayi da fad’in “Ashe kai d’an sarki ne, shi ne ka je makarantarmu a matsayin malami.”

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button