BA JINI NA BA CE 1-END

BA JINI NA BA CE Page 41 to 50

Da alama nacin MD ma kawai zai sa yasamu yadda yake so lol????????????????????

Maman Islam ce

بسم الله الرحمن الر حيم

*__________________________________*

☀ *FIRST CLASS WRITER’S ASSOCIATION* ☀

   FCWA

*{Home of qualities and trusted writer’s of The nation}*

https://www.facebook.com/First-class-writers-Association-111719967001810/?referrer=whatsapp

*________________________

???? BA JININA BACE????

2021

              NA

HASSANA ABDULAZIZ YAKASAI

MAMAN ISLAM

Godiya ta musamman gareku masoyan gaskiya hak’ik’a ina jin dad’in yanda kuke min ina ina sonku domin Allah musamman ma ku d’in nan

MAMAN Jani

Ammeyn Sadik

Antyn muhseen

Ya Rahman

Mare

Jidda

MAMAN Abul

Mom Irchad

Ummey Idris yakub

MAMAN sayyadi

Shamsan

Maman sultan

Umm nawaad

MAMAN Raees

Safiya Sopy

Aisha munir

MAMAN jabir

Xeeyyah

Rashida Muhammad

Afra

Fauzi

Ummukurthum

Aishatu k sani

Zainab autar mm

Jannat Aliyu

Barira Aminu

Hykarianeg 17

Ameenatu

Khadija Muhammad

Hafsat Bala kawu

Maman Arif

Ikilimatu D Baraya

Ummu Abul

Mr maimunatu

Aisha ibarahim ummi

Zainab Muhammad sambo

Juwairiyya Lawal

Maman twins

Mama

Khadija Isa Dari

Duk wanda bai ji sunan sa ba yamin afuwan mutara a text fage ina k’aunar ku nima son so fisabilillahi.

Page 33

Tusio tasa ta goge bakinta kafin ta mik’e ” ina zaki?”

Kallon yadda ya wani lafe jikin kujeran dining d’in tayi kafin ta wani tab’a baki tace “ina kaji Baffa yace yana son ganinmu?”

Kai ya d’an dafa alamun ya manta sai kuma ya tashi yace “muje” batareda tace komai ba ta mik’e ta wuce yabi bayanta suka nufi part d’in Baffa.

Tun kafin su shiga suke jiyo b’ab’atun haj. Sailuba sai faman bala i take zubawa Baffa wani mugun tsaki MD ya saki har ga Allah ya mugun tsanar matar nan haka nan, abinda ya dad’a d’aure musu kai shine yadda suka shiga suka tarar tana zuba ruwan tujara shi kuma Baffa yana lallab’a ta yana bata hak’uri, da dai yaga abin yak’i k’arewa ne ya dubi Ammey yace.

“Aminatu dan Allah na rok’eki ke ki hak’ura taje tunda ita ban isa da ita ba baza tayi min alfarma koda sau d’aya na sauke hak’k’in ki ba”

Cikin wani irin yanayin da bazaka tab’a iya fassara shiba Ammey tace “ai dama Baffa ni ba matar gida bace ‘yar zaman jiran gida bace da kula da gida ko ba haka ba?

Gaskiya Baffa wannan karon bazan yarda ba nima duk abinda zai faru sai dai ya faru amma nataji wallahi haba dan masifa da bala i shekara da shekaru abu yak’i k’arewa nima wannan karon bazan hak’ura ba Baffa sai dai duk abinda zai faru ya faru.

Nan fa Ammey itama ta bud’e wuta ta rik’a zubar da maganganu masu d’aci kunsan ance mai hak’uri bai iya fushi ba to haka ne yafaru ga haj. Amina yau duk irin yadda Baffa yaso rarrashin ta botsare masa tayi.

Dai dai shigowar su MD da suka gama sauraran komai MD ya kafe Baffa da ido kafin yace “Baffa mai yake faruwa ne nakejin abinda ban tab’a jiba game daku?” ya fad’a yana kallon Ammey cikin yanayin da bai tab’a ganinta aciki ba.

“Kamar yadda aka saba ne Muhammad yauma nayi magana ne akan kujeran hajji danake fitarwa duk shekara, Sailuba bata tab’a bari na bawa Amina tabawa wani nata ba sai sau d’aya kuma ni bansan me take da kujeru har guda goma ba tunda ko ta b’angaren mu nike biyama dangi, to itama mai hak’urin yau ta botsare min tace sam bata amince ba itama na rasa yadda zanyi yanzun”

“Kawai kabawa wanda kake ganin yafi cancanta”

“Baza abawa wanda yafi cancanta d’in ba wallahi ko zata mutu wannan kujeru nawa ne dan haka banga wanda ya isa hanani wannan kujeru ba ehe, idan kuma tak’ama ce naga ubanka ma acan k’auye raba kujerun nan yake kamar babu gobe”

“Ni bana harka da jahilai marasa ilimi dan haka bani da lokacin da k’ik’ancin ki*

“Uwar ka ta kabari itace dak’ik’iya baniba dan is………..kafin ta k’arasa taji wani irin fitinannen zafi ya karad’e fuskar ta ta d’ago a firgice dan ganin wanda yayi mata wannan d’anyen aikin sai da ta wuntsula daga kan kujeran ta ganin Baffa ya kafeta da kallo yana huci, yayin da MD ya mai da kansa k’asa cikin tsantsar b’acin rai da wani irin tsanar haj. Sailuba.

Da wani irin tashin hankali ta bar wajen domin wannan ne karon farko da hakan ya tab’a faruwa iya tarihin rayuwar su dan haka abinda yayi matan yai masifar gigitaya ta sani hakan yana nufin aikin ta yana rawa kenan ai kuwa ya zama dole ta sabunta shiri

Tana barin wajen Baffa ya dubi MD yace “Muhammad na fad’a maka ka fita hanyar Sailuba matar nan jahila ce amma bakaji” da mamaki MD yake duban Baffa to shi mai yace dan kawai yace Baffan yayi abinda yake ganin daidai shine ya shiga sangarta? 

Da wani irin fushi MD ya bar wajen yayin da duk suka bishi da kallo sai Maryam ma ta rufa masa baya dan sam bataji dad’in abinda maman nata tayiba.

Ammey ma tashi tayi yayin da Baffa itama ya bita da kallo haka dai duk suka watse kowa zuciya babu dad’i Nassar ne kawai ya zauna ya ci ya koshi abimsa ya kama gabansa ya tafi gidansu boy abokansa.

Sanda Maryam ta isa part d’in MD har ya gark’ame k’ofar da key babu irin bugan da batayi ba yai banza da ita kamar baikita ba.

Haj. Sailuba kuwa tana shiga d’aki a gigice ta nemi wayar ta ta kira haj. Zakiyya kamar wata k’aramar yarinya haka take kuka wurjanjan cikin tsantsar tashin hankali ta kora mata duk abinda yafaru. 

Sosai ta rarrasheta tace tunda abin haka ne kawai ta shirya cikin satin nan su wuce India can ne za ayi musu aiki mai kyau sun jima suna tattanawa kafin suyi sallama, sai lokacin ta d’an samu sassauci

Maryam kuwa d’akin ta ta koma cikin damuwa tasani cewa Mama bata kyautaba ko kad’an amma Kuma ita meye laifin ta da zai wani rufe mata k’ofa.

Ganin zaman bazai mata ba kawai ta mik’e ta saka mayafinta da niyyar taje wajen Halima ko zata d’an rage damuwa, daidai bakin get suka had’u da Baffa ya hanata fita dole ta dawo gida cikin k’unci.

MD kuwa tunda da yake babu Wanda ya tab’a zagar masa uwa ido da ido sai yau hakan ya masifar k’ona shi da k’yar yasamu ya rarrashi kanshi ya baro falon shi yasa ya kulle kanshi domin a halin dayake ciki baya buk’atar kusanci ga kowa atare dashi.

Ammey kuwa cikin fushi ta koma d’akin ta ranta a masifar b’ace tasha alwashin bazata k’ara yarda Sailuba ta rik’a juya ta ba tunda babu adalci a lamarin itama ya zama dole ta zage ta kwatar wa kanta yanci.

Haka da ranan mutanen suka kwana kowa zuciya babu dad’i da safe da zasu wuce islamiyya hankalinta yana kan k’ofar sa bata taba alamun ya bud’e k’ofar ba, sai ta tab’e baki a k’ok’arin ta nasan yakice tunanin shi aranta tunda shima fushi yake da kowa na gidan.

Sai dai duk irin yadda taso kore tunaninasa aranta hakan yak’i samu sosai tayi sanyi dan ko k’awayen ta na islamiyya sai da suka gane tana da matsala, sanda suke dawowa daga islamiyya shi kuma ya fito daga d’akin dake lokacin an yi kiran Azhar ne sai da ta d’an razana ganin har ya d’an fad’a daga jiya zuwa yau kacal bata kulashi ba ta d’auke kanta, Nassar ne kawai ya gaida shi, ya bita da kallo har tashiga ciki kafin ya juya ya wuce masallaci.

Koda ya dawo shima cikin gidan ya dawo lokacin har sunyi zaman cin abinci banda haj. Sailuba datake d’akin ta tun juya shima wajen ya tunkaro duk suka bishi da kallo har Baffa wanda yay mamakin ganin shi hakan Ammey tafi kowa shiga damuwar ganinsa a hakan.

K’arasawa yayi ya gaida su kafin shima su Maryam suka gaida shi Ammey ta zubawa kowa nasa abincin amma MD da kanta ta fara bashi dan ta riga tasan halinshi muddun yana cikin damuwa baya iya cin abincin sai dai yayi ta fama da tunani tana cikin bashi ya tsinci muryanta tana fad’in.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button