BABY KHAUSAR COMPLETE HAUSA NOVEL

BABY KHAUSAR COMPLETE HAUSA NOVEL

BABY KHAUSAR COMPLETE HAUSA NOVEL

Baby da Islam meye tsarabanku hada baki sukai Dad ina zakaje ?

Zanje inkai yayanku Bilal .mkrnta a India.

Dajin abinda Dad yace baby ko kuma magana bataiba don ta tsaneshi.matuka
Itakuwa Islam da murnarta tace Dad kasiyomana irin Kayan da yan India suke rawa dashi.
Dariya sukasa shida mamy .yace to shikenan Islam zaa siyo muku.

????????????
[11/13, 10:52 AM] Spouse 2: ????????????????????
????????????????????????
????????????????????????????

BABY KHAUSAR

      NA 

LAYUZA KABIR ADAM

ZAMANI WRITERS ASSOCIATED????

INA SONKU INA KAUNARKU .
MASOYAN BABY KHAUSAR
ALLAH YABAR KAUNA❤

        4⃣4⃣

Tunda Garin Allah ya waye Bilal da momynsa suke kukan Rabuwa har sanda dad yagama shiryawa yafito ko kallon hjy baiyiba sabida Tunda Ta dawo kala bata shiga tsakaninshi da itaba rungumo Bilal yayi jikinsa Yace be A man mana my son Neman ilmi zakaje dole ka jajirce kazama namijin duniya karkasa tunanin komai aranka banda na karatunka maza wuce muje karmu makara

Tunda  Suka shiga jirgi  Dad  yakemai nasiha akan yarike karatunsa   yarike addininsa  to  Dad kawai yake fadi 

Samiola shine me mkrntr su Bilal din shi yai musu masauki cikin girmamawa

Komai daya kama anyimai anbashi daki acikin hostel An bashi uniform Da dikkan material na karatu .

Saida Dad ya ga komai ya daidaita har Bilal yafara daukan darasi sannan yai shiri yayo gida .

bangaran su baby kuwa komai yana tafiyar mata dai dai don kuwa Yanzu sun koma school itada Islam suke tafiya dikda tafi Islam da aji daya

 Mamy ta dauko musu me kula dasu kama daga yimusu wanka da shiryasu hadamusu abincin da zasu tafi dashi school Shiryasu zuwa islamiyya  yi musu tsifan gashi  kai dik dai wani Abu da ya kama aiwa Yaro  shine aikin bintu  bazawara ce me tsafta da addini  
dakin da akasa sauketa yana jikin nasu baby don haka basu da damuwa 

 Mamy ta koma bakin aikinta  don dama hutun aure ta dauka  yanzu kuwa ta koma 

 Sun sami nutsuwa sosai  baby batada wata damuwa  yanda mamy bata taba nuna  mata wani banbanci tsakaninta da Islam shi yafi komai yimata dadi .

Ranar da Dad ya dawo  sunsha murna sabida   yacikosu da tarin tsaraba .

 Kayan wasan da yai musu tsarabanshi ba magana  haka aka kara cika musu filin wasansu da manyan jiragai  ga dokuna  da giwaye  dik wani abin wasa daxai birgeka  an shirya musu shi a filin wasansu .

Dik ranar Alhamis da jummaa a  kusan nan suke yini Daga sinbaro  school  karfe daya  nan zasuje siyita  Abu daya  sai dai in lokacin sallar laasar yai  su shigo suyi sallah  su koma 

Ranar asabar da lahadi kuwa ba dama don tun karfe  bakwai ake kaisu tahfeez .sai sha biyu zasu dawo

wanka da cin abinci sannan su Dan huta karfe biyu amaidasu islamiyyan sai kuma karfe shida

 Rayuwa me dadi da inganci akeyi agunsu Baby  kai kana ganin Baby bai zama lalle Kayi saurin ganetaba  sabida ta kara wani kyau  Yarinya  abin shaawa da birgewa ga tsafta da aka kafa mata jikinta dashi wata  nutsuwa ta ratsa ta .

Kawance su da Aysha  sai karuw yake kamar ba na yara  ba 

Don yanzu har kaisu gidan su Aysha akeyi itama ana kawota gidansu

Acan kasar India kuwa Bilal ya dage da karatunsa don dama shi Indai a fagen karatu ne ba dama akwai kwakwalwa don haka yakejin dadin komai koda yaushe suna waya da Dad da momynsa don haka hanlalinsa a kwance yake lakadan

Hjy kuwa yanzu ba laifi sun daidaita da Alh. Amma fa. Bawani kamar daba don haryanzu yanajin bakin ciki inya tuna da irin illar data musu shida Baby

????????????????????????

6/10/2017
[11/13, 11:02 AM] Spouse 2: ????????????????????
????????????????????????
????????????????????????
BABY KHAUSAR
????????????????????????

~Na~
LAYUZA KABIR ADAM

ZAMANI WRITERS ASSOCIATION

FATIMA BINTU FATIMA SAI WATA RANA, SO MAFARKI NE DABA TABBAS BA ????????????

Wannan page? naki ne
sweet Ummy y Fatima y Abdullahi

            4⃣5⃣

Haka rayuwa. take garawa yau da gobe bata bar komaiba.

Yau ga Baby Yan matan mamy  ana j s s.one .yayinda Islam take shekaran karshe a Primary 

Ba abinda za'a cewa mami sai  Allah ya saka  da alkairi  domin kuwa  ta  zama uwa ta gari ga ya'yanta  

Mami ja’jirtacciyar uwa ce ga yaranta duk da kasancewar samun waje da boko tayi a gidan hakan bai hana magartacciyar tarbiyya shimfid’uwa a gunsu ba, Abin sha’awa ma sai kaga yanda yaran suke zuba karatun alkur’ani, hadisi da sauran littattafan addini .

Uwa uba sallah Mami bata sassauta musu akan maganar Ibada don haka daga sunji an kira sallah zasu yi maza suje suyi ta
Ga nutsuwa Agunsu komai da akeson d’an musulmi dashi yaran nan sun samu sun mallake shi

Rayuwa tana ta tafiya rayuwa tana kara dad’i ga wasu yayin da take matsewa ga wasu

To hakama hjy Amina rayuwa taimata kunci bata jin dad’in komai don Alh ya hana kowace kawarta shigowa gidan sa kuma itama yai mata katanga da gidan kowa tunda dai batada kowa agarin.
Wannan ne yasa duk ta kara tsangwamewa in kaga fara’ar ta to suna waya da Bilal ne

Wanda shi zuwa yanzu karatun sa yai nisa don har ya kammala secondary d’in suna Hutu kuma Dad yaje ana mai duk wani shirye-shiryen Shiga university d’in
dan gida kacokam dad ya siyami shi shida wani abokin sa d’an nan kano ne shima kuma tun daga J s s .one ya fara tunda suka had’u a can suka had’e Kansu tamkar yan’uwan jini to don haka
da Dad ya siya mai gidan plart ne mai parlour da d’akuna biyu yace su zauna shida sageer d’in

 A haka akaci gaba da garawa  su baby ana s s .2, Islam ana 1 kuma a lokacin sunyi saukar alkur'ani mai girma .

Sun zama yan mata na gani akara kalla gakyau ga iya wanka ga nutsuwa kansu a had’e yake
kullum ka gansu a shiga iri d’aya zaka gansu don yanzu ko d’an kunne d’aya baisawa sai irin wanda d’aya ya saka .
don haka suke birge mutane da dama kowa sha’awa suke bashi sabida yanda kansu yake a had’e

 A yanayin da ake na damuna. ne . yau tun karfe d'aya ake tsuga ruwan sama 

Su Baby suna d’akin su suna ta hirar su har bacci ya daukesu .
Ba’a dauke ruwanba sai karfe hud’u saura kwata

 Islam ce tai juyi taga hud'u tayi mikewa  tayi ta shiga toilet tai wanka tare da dauro alwala, tana fitowa ta tashi  baby .

dukkan su bayan sun gama shiryawa suka fito parlour islam ta shiga shirya musu abinci .
Suna zaune a dining suna cin abincin suna d’an taba hira Mami ta sauko daga up stairs. Tazo .ta zauna tana murmishi tace “um sannu yan Hutu sai yanzu kuka tashi daga baccin?”.

 Dariya suka yi baby tace  "Mami ruwa fa aka yi, kinga baccin yafi dad'i".
  "Hhhhhmmmm hakane kam"

Hira  sukeyi a nutse irin ta wayanda suka waye da ilmi 

Islam ce ta dubi Baby tace  "sis zo mu d'an motsa jiki mana" .
    "Ok muje Mu saka kayan sport"  cewar baby 

 Baby tasa red color yayinda islam tasa blue riga da dogon wando ne sai hula me kama dana sanyi 

Sai fararan combus.

Kai whl sunyi kyau kallo daya ba zai isheka ba matukar kai musu shi

Layuza ????
????????????????????????
[11/13, 11:04 AM] Spouse 2: ????????????????????
????????????????????????
????????????????????????????
BABY KHAUSAR
????????????????????????????

ZAMANI WRITERS ASSOCIATION

Na
LAYUZA KABIR ADAM

DEDICATED TO U ALL SISTERS
1-ZAINAB KABIR
2-MARYAM KABIR
3-AISHA KABIR
4-ZAKIYYA KABIR
AND LITTLE AISHA SAHLA ❤

        4⃣6⃣

Fitowa suka yi da d’an gudu gudu hannun su rike da juna haka sukaita zagaye filin sannan Suka zube kan kujeran dake kasan wata bishiyan fruit .
Sosai yake kara leko kansa daga jikin window d’in dayake a tsaye kasancewar a saman bene yake shi ya bashi damar kallon su sosai

“to wayannan su waye suka zo gidanna su haka yan’mata kyawawa dasu kilama yan biyu ne, don gasu kusan Kansu daya”.

Wannan itace maganar da Bilal yake ta mai-mai tawa a ransa

Saida  suka huta sannan suka tashi Suka shiga   yin snooker  sosai suke  kyalkyala dariya   Wa  junansu  sabida yanda  Kowanne  yake  yi da iya karfinsa  nason  cinye  d'an uwansa  

  Islam ce  ta fara doke  baby  aikuwa nan da  nan  itama ta kara  kaimi  akaro na  biyu   tana shirin kara  zirawa  baby ta saki sandanta akan na islam d'in  yar bol din tayi gefe   aikuwa  baby tace me zatai ba dariya ba  ganin rainin hankali ne abin yasa  islam  ta kaimata cafka aikuwa ta zura  da  gudun gaske itama  ta bita wai saita rukota ya bigi kafadarta  


  Gajiya baby tayi da gudun don Harsin shige  can cikin gidan Kusan sashin su  Hjy Amina  jikin  wani window baby ta jingina  tana  fadin   

  " I'm sorry  sweet sis na tuba ki barni  haka da gudun nan"????

Dariya islam d’in tayi “ok sannu sarkin tsoro na hakura mu wuce ciki”.

 Bakin fanfon dake gefan  gun Baby taje 

Hulan kanta ta cire ta fara watsa ruwa a fuskar ta tare da girgiza kanta gashin ta duka ya baje a a gadon bayan ta da gefen fuskar ta

   Sannan Islam ma ta  wanke fuskar ta  suka   juya zuwa cikin gidan

  Duk abinda suke yi akan idon Bilal  wani irin yanayi yake ji a jikinsa da ransa don yanzu hakama daya koma kan gado ya kwanta komai dawo mishi yake  tindaga fitowar su da d'an gudu gudun nan harzuwa sanda suke koma wa fart d'insu 
   Ammafa yaga d'ayar data danfi tsayi da siranta kamar baby khausar 
  "Kai A'A ba ita bace yaushe baby zatai wannan girman  da  kyau haka"

Yana wannan tunanin yaji anfara kiran sallan magriba 

Jiki a mace ya mike ya shige toilet don dauro Alwala
     Yana zaune a masallaci har akayi sallan isha'i  sannan ya shigo gida  shigowanshi yai dai dai da shigowar motan Dad don haka yaja yatsaya   har  motan tai  farking   da sassarfarsa ya karasa jikin motan  shikuma  shima Dad da sauri  yafito suka rungume juna  cikin tsananin farin ciki 

   "Ur welcm son   ka  zo tunjiya katarar bana  gida ko, ina can duk hankali na yana kan ka  kawai dan dai  meeting dinnan yanada matukar mahimmanci ne. Dana zauna Na tareka my son"

Rike hannunsa yayi suka shiga cikin gida dukkan su fuskokin su d’auke da fara’a

   Suna shiga  part d'in sa yace "my son bari inyi wanka infito  mu zauna  yau ai a bangarena zaka kwana".

  duka 15 minuts ya fito  yasa prayer mat ya tada sallan magriba da isha'i  dake kansa 

zuwa lokacin mami harta cika mai dining t , da kayan abinci don itace da girki sanda ya shigo sunji shigowar motansa to duk suna sallah bayan Ta idar kuma ta shigo ya shiga wanka sai Bilal ta gani zaune a parlour suka gaisa dukda batasan yazo garinba anan ta tsinceshi

  Ta juya zuwa part d'inta tunda yashiga wanka sukaci  karo dasu Islam sun taho mai sannu da zuwa  tace "ya shiga wanka Ku koma zuwa anjima "

"Mami amma dad yasan muna son ganin sa amma shine  kafin mu idar da salla muzo harya  shiga wanka".

     Cewar Baby sanda take zama kan kujeran parlourn su .

  Murmushi Mami tayi tace "to baby meye abin bata rai Dad dinku gajiya ya d'auko yanzu  zai fito Ku gaisa".

Layuz ce
????????????????
[11/13, 1:01 PM] Spouse 2: ????????????????????
????????????????????????
????????????????????????
BABY KHAUSAR
????????????????????????

ZAMANI WRITERS ASSOCIATION

Na
LAYUZA KABIR ADAM

GODIYA NAKE MASOYA NA,
MAKIYA KUWA INA ROKAR MUKU SHIRIYAR ALLAH????

       4⃣7⃣

Mami d’akin ta ta shiga ta kara fesa turare ta fito ta koma part d’in Dad d’in
Kai tsaye d’akin tashiga ta same shi tsaye yana balle Link’s d’in hannun jallabiyar dake jikinshi Yar asalin baharain

Ja tayi ta tsaya jikin kofar d'akin ta hard'e hannayan ta a kirji ta kafeshi da wani kallo na kayimin  lefi 
Mirmishi yayi yana had'e hannayan sa waje d'aya alamar ban hakuri ????

  "Ayi hakuri madam nasan ban kyautaba, na dawo nashiga wanka banjira kinzo kin taimakamin ba 

Uziri namiki nasan kila sallah kike tunda naga daga ke har yan matan naki ba Wanda yazo tarana a bakin mota, amin afuwa ranki ya dade ???? “

“sarautar mata Halima hali dubu cikinsu babu na yarwa, amarya gidan A A mama ga emmata baby da Islam”

Batasan sanda dariya tazo mata ba najin dad’in kirarin nasa Wanda yasaba yimata duk sanda yaga tana fishi

Rungumeshi tayi. Tace  "sannu da zuwa yallabai Andawo  lfy ya gajiyan hanya"

“Ga gajiya kam sadiya tari guda, sai kinmin tausa” ya fad’a yana leka Idonta
Bata tanka mishi ba ganin sun fito parlour ga Bilal

Mikawa Bilal hannu yai alamar yazo suci Abinci da sauri Bilal yabi bayansu suka zauna a kujerun dining din mami ta shiryawa kowa nashi ta mikawa bilal a gabanshi yaja yafara ci

Hakama Dad yanaci suna zuba Hira da santi harsuka gama

Parlour suka dawo suka zauna kasancewar mami wayayyiyar mace yasa tasaki jiki sukai ta hira da Nilal yana bata lbrn zaman India yanda suke karatu dadai yanda yake rayuwa a can

Hhhhmmmm tsakanin d’a da mahaifi sai Allah duk hiran da ake tafkawa Dad hankalinsa naga baby Me yahana ta zuwa gaishe shi har yanzu yau kwana biyu Kenan be gantaba nan da nan yadau wayansa yakira ta ,Islam CE ta daga “hello Dad”
“Islam ya akai naga bukuzo wajena ba tun d’azu?”

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17 18 19 20 21 22 23 24 25 26 27 28 29 30 31 32 33 34 35 36 37 38 39 40 41 42 43 44 45 46 47 48 49 50 51 52 53 54 55 56 57 58 59 60 61Next page

Leave a Reply

Back to top button