BABY KHAUSAR COMPLETE HAUSA NOVEL
BABY KHAUSAR COMPLETE HAUSA NOVEL

????????????????????????
[10/2, 11:42 PM] Spouse 2: ????????????????????
????????????????????????
????????????????????????
BABY KHAUSAR
NA
LAYUZA KABIR ADAM
DEDICATED. TO
HUBBY NASS❤
2⃣2⃣
*Da wata irin matsananciyar yunwa ta farka kasancewar .jiya ko na magibar da ake sammata. Bata samu Ciba baccin. Wahala ya dauketa .
Jitai yunwar na shirin kaita barzaku .don haka ta fito .zuwa dining. Ai kuwa cikin saa .ta tararda hadadddan dilutions. A flate. Sai tiriri yake harda spoon aciki
Hhhmmmm abinka da yarinta bata tsaya tunanin komaiba tasa. Hannu ta fara. Biga. Loma. Ci take hannu baka hannu kwarya. Ai. Kuwa ta doka saa harta. Gama ci tayi kat ta bude standing fridge dake .dining area din ta dauko bottle na ruwa me sanyi. Ta. Kwankwada
Ahhh tai ajiyar zuciya .rabon data ci abinci me dadi irin wannan ta koshi harta. Manta .
Taku taji. Daf daf ana saukowa daga stairs. Ai kuwa da sauri ta juya
Bilal ne yake saukowa yana dannan wayarsa
Kam ta Kame jikinta ya hau Mazari ganin yana tun karota da mamaki ya tsaya yana kallonta ganin flate din abincinsa dayayi ba komai shi daya tafi yabarshi a rufe amma gashi bude ba komai
Keee.
ya daka mata tsawa . don uwarki ina abincin dake aje anan
Cikin muryan kuka ta fara fadin don Allah. Yaya kayi hakuri don Allah karka dakeni please my broth
Keee rufemin baki ko na karyaki don kan babarki .
Kinsan ina zanje da safannan nasa akamin girki. Shine na ajiye inje. Indauko. Phone dina kikasa agaba kika cinye
Wai ke gaki mayya ko .to yanzu zanyi maganinki
Kai mata shaka yayi ya rike. Mata makogaro waishi dole saita amayo da abincin
Amma dake Allah Allah ne .
Ko kadan abincin bai fitoba
Ganin yayi iya yinsa abincin ya fito yaki haushi ya kamashi ya kifa mata mari ta kife zuwa kasa
Bol yashiga yi da ita yana takata
Ahaka. Dad ya sakko zai fita ya tararda wannan aikin .amma kallo daya yai musu ya kauda kai
Harya. Kai kofar fita a parlour n ya juyo yace. Bilal zan wuce. Baka bukatar wani Abu .
Kasan nacema zankai wata biyu a can ko
Bani da bukatar wani Abu inma akwai wani Abun .zan sanar dakai ta waya
Dad Allah ya kaika lfy
Ameen my son bye
Wayyo Allah Dad dina ina zaka tafi .don Allah ka dawo ka rika min wanka kamar da karika bani abinci abaki ka rika fita dani .yawo a mota . Dad ka dawo ka rinka sona kamar yanda kake sona da
Kuka ta kara saki me karfi. ???????????? ganin yasa kai yafice .
Yanajin kuna matuka azuciyarsa .dik sanda yaga tana cikin wani yanayi ko kuma yaga hjy ko Bilal tana dukanta tana kuka
saiyaji shima kamar yayi kukan
Amma kuma ko kusa ko alama bazai iya yin komaiba
Yanzunma jin zuciyarsa na kuna yasa ya fice da sauri.
Kee rufe wa mutane baki ubanme akai miki da har zaki rikaiwa mutane wannan ihun cewar hjy data sauko kasa yanzu
Momy kinsan kuwa me wannan tunkiyar yarinyar nan tamin
Wai abincina ta cinyemin daga na je dauko phone dina shine ta cinyemin
Kan ubancan .kaikuma shine ka tsaya kana kallon ta bazaka dau mataki ba
To ai momy kinsan sauri nakeyi yanzu inna tsaya hukuntata bata wa kaina lokaci zanyi
To bari inbaka shawara maza jeka sata a zoo ka kulleta inka dawo saika San me zaka mata
Good good momy na kin kawo shawara me kyau kuma kinsan banzar tsoron .monkey take . don haka a dakinsa zan sakata .
Jin abinda suke fadi yasata sakin wata mahaukaciyar kara tana girgiza kai .
A a momy karki bari ya kaini zoo banso
Momy help me momy ki ji tausayina don Allah
Janta yai kamar jaka tana ihu tana birgima
.
Dik wannan Nisan dake tsakanin su da zoo din. Akasa yajata .
Yana zuwa ya umarci me kula da wajan daya bude mai
. tunkan su karasa dakin monkey din ta daina kukan ta kulle idonta matuka numfashinta yazo wuya don tsoro da razani
Cillata yai cikin dakin monkey din .ya rufe .
Sannan ya kalli me kula da gun yace ban yarda afito da itaba harsai na dawo .
Jinjina kai yai yace angama uban gidana
????????????????????????????
[10/2, 11:42 PM] Spouse 2: ????????????????????
????????????????????????
????????????????????????
BABY KHAUSAR
NA
LAYUZA KABIR ADAM
DEDICATED TO ????
All students 2013 /.Sa’adatu rimi college of education kano
2⃣3⃣
Tunda ya wullata dakin birin nan ya juya ta sume
Shidai inuwa bin bayan Bilal yai suka fita
Yana tsaye daga can nesa ya hango direba yaja Bilal a mota sun fice .
Ajiyar zuciya yasaki da gudu ya koma cikin zoo din ya shiga dakin birin
Abinda yake tinani shi yagani
Wato ta suma . da sauri ya daukota ya fito da ita karkashin bishiya ya ajiyeta ya debo ruwa
Yana kwara mata taja numfashi da kuka ta tashi da sauri ya riketa
Yana fadin yi hakuri Baby kinji yanzu ba a dakin biri kikeba bude idonki kiga
A a nidai bazan budeba don Allah ka fitar dani daga gunnan wayyo iya Abuta kizo Karna mutu kinji
Tausayi matuka ta bashi don dik Wanda yake gidannan yasan da sabon sauyin da
Yazo yanda ake azabtar da marainiyar Allah
Rukota yai da muryar rarrashi yace baby bude idonki Kiga wlh na cireki daga dakin birin .ba aciki kikeba kinji
Ahankali take bude idon .ganinta karkashin bishiya yasata sauke numfashi daga bisani ta saki wani kuka me ban tausayi .
Rarrashinta yashigayi yana fadin ba komai baby kiyi hakuri kinji rayuwa ce wata rana sai labari
A iya shekarunki da uwarki tana Raye biki wuce kiyi rigima ta goyaki ba amma sai gashi dalilin maraici karfi da yaji kinzama mamallkiyar kanki
Yi shiru baby Allah yana gani kuma baya bacci hakika akwai abin dubawa a lamarin gidannan shedan yasamu wajan zama dirshan
Dikda ba fahimtar Yawancin abinda yake fada takeba. Amma tabbas tasan tausaya mata yake
Nan yazauna yanata yi mata hira har wajan karfe daya yaje yai sallah .sannan yace wa me gadin babban gate .dayaga motar da direba yafita da Bilal ta shigo gidan yamai flashing
Koda aka kawomai abincin sa na rana rabi yaci yabata rabi ya tsinko mata goba nunannu taci tai kat tasha ruwan fanfo abinda bata taba shaba tunda aka haifeta sai bayan lalacewar gidan
Haka ta kwanta a kasa tai baccinta ta koshi
Sai laasar ta farka
Zuwa lokacin inuwa yagama shirya dik dabararsa .
Wata waya yasamu ya lankwasar ta dakin birin yai hanya sosai inda mutum zai iya shiga ya fito . sannan yacewa baby idan yayanki ya dawo yaganki anan akwance zai tanbayeki wa yafito dake .saikice masa ta wannan kofar kika fito .karfa kice ni na fito dake inba hakaba zai maidake dakin .kinji ko sannan inya tanbayeki kinci abinci kice masa a a .kinji ?
Gyada kai kawai take .itadai
Wajan karfe biyar yashigo gidan ai kuwa motar nashigowa .me gadi yaiwa inuwa flashing. Da gudu ya shige dakinsa dake bakin kofar zoo din ya kwanta bayan ya sa baby itama kwanciya a karkashin bishiya
Baibi takanta ba yashige fart dinsu saida yai wanka yafito yaci abinci .sannan yashiga dakin momynsa
Bilal kun dawo
Eh mundawo momy
To ya hanya ya jikin baban sadiq din
Da sauki .gaskiya momy garinsu sadiq da nisa tun .muna hira harnai shiru
Ah haba kano da jigawa ba wani nisa Bilal kawai dai don baka saba doguwar tafiya by road bane .shiyasa
Kai momy ya yarinyar nan nifa harna manta na kulleta a Zoo.
Kai nima na manta jeka dubata shegiya Allah yasama ta mutu aciki kowa ya huta
????????????????????????
24/9/2017
[10/2, 11:42 PM] Spouse 2: ????????????????????
????????????????????????
????????????????????????
BABY KHAUSAR
NA
LAYUZA KABIR ADAM
Nakune wannan
Mahaifana Allah yasaka muku da mafificin alkairi
❤ my lovely Dad kabir Adam
Allah yaja da rai
❤ my sweet mahmah
Juwairiyya yusuf
( horo saiga Malami ) momyna
2⃣4⃣
Yana zuwa dakin inuwa yafara lekawa .yaganshi kwance kan katifarsa .ya lulluba da zani sai makyarkyata. Yake
Ya inuwa ya akaine naganka kwance