BARRISTER IBRAHIM KHALIL 1-END

BARRISTER IBRAHIM KHALIL Page 1 to 10

“Babu inda zan fita wlh, idan har kaga na fita to lokacin tashin ka ne yayi”.

Harara yabanka mishi yaja ɗan siririn tsaki still yaci gaba da aikin sa

“Wai ya maganar Alhaji Mubarak ne? Me ake ciki yanzu? Yakamata fa musan abin yi tun kafin lokaci yaƙure mana”. Cewar Brr. Tahir kenan yana ɗan gyara zaman sa

Kamar bazai ce komi ba, sai can kuma yabuɗi baki ahankali yace

“Muna da enough time ai insha Allahu komi zai zo da sauƙi, zuwa nan da nest week ma zan je Eygpt ɗin”.

Jinjina kai Brr. Tahir yayi yace

“Gaskiya Shari’a da irin su Alhaji Mubarak hatsari ne dashi, yakamata kakula Ib kasaka idanu da kyau, kafin lokacin zasu iya yin komi don kawai su hanaka samun nasara, but naga alaman kana ɗaukan abun kamar da wasa ne”.

“Hmm babu abunda zasu iya yi, kai dai kazuba idanu kagani duk wani take-taken su ina sane dashi, kuma bazasu taɓa samun nasara ba, da yardan Allah sai nayi nasara sai na ƙwato mata haƙƙin ta, insha Allahu ta sanadiyar Nazeefa sai na kawo ƙarshen Alhaji Mubarak da duk kan mabiya bayan sa”.

Brr. Khalil yafaɗi hakan yana kallon Brr. Tahir ɗin

“Gaskiya ne, Allah dai yabaka sa’a, yanzu ya take? Ina fatan tana samun lafiya?”

Ɗan jingina kan sa yayi saman kujeran da yake yana lumshe idanun sa kafin yagyaɗa masa kai sai kuma yace

“Ina son namaida ita asibiti ne domin ina son aƙara duba ta da kyau, zamanta gida babu amfani”.

“Hakan yafi dacewa ai, amma baka ganin kakaita asibitin da Sameer yake? Inaga shima zai fi kula da ita”.

“Nima nayi tunanin haka, sai dai kasan Dr. Hashim yace “abarta agidan hakan zai fi sirri, sannan kasan Big bro ba aikin sa bane, tun farko shi yace dani in nemi Dr. Hashim zai fi bata kulawa, kuma sosai take samun lafiya ba kamar da ba”.

Gyaɗa kan sa Brr. Tahir yayi cike da gamsuwa, daga nan hira suka ɗan taɓa zuwa lokacin tashi aikin nasu kafin suka fito ko wanne yahau motan sa yatafi.

     Kamar ko yaushe ahankali yake jan motan sa, yanzun ma hakan yake yi kamar baya son tafiya, ta cikin mirror ɗinsa yahango wata baƙar mota tana binshi, da farko be wani damu ba don a tunanin sa ko bashi take bi ba, sai yatsaya yana kallonta ta cikin mirror itama motan packing tayi can nesa dashi, tsawon minti 5 be tada motan ba itama haka motan tana nan yanda take, ahankali yataka yaci gaba da tafiya batare da yaƙara speed ɗin motan ba, yana yi yana kallon motan da taci gaba da bin sa, sai da yayi nisa sai kuma yasake tsayawa itama motan taja tasaya.

[8/31/2020, 8:20 AM] نفيسة أم طاهرة: ????️????️????️????️????️????️????️????️????️????️

   *BARRISTER IBRAHIM KHALIL*

                        ♠️

*Written:✍️ By Nafisat Isma’il*

_(Feenah Jikar Lawal Goma)_

*بسم الله الرحمن الرحيم*

 

*FEENAH WRITER’S ASSO????*

“`{{Ɗaya tamkar da Dubu????}}“`

*JIKAR LAWALI CE*✍️

*Wattpad: UmmuƊahirah*????

         *⚜{{F.W.A????}}*

“`ALHAMDULILLAH

ALHAMDULILLAH

ALHAMDULILLAH“`

_ALLAH nagode maka da kabani damar rubuta wannan littafin Brr. Ibrahim Khalil, Allah kabani ikon rubuta abin da zai amfani al’umman mu, kuskuren da zanyi aciki kuma Allah kayafe min AMIIN ???? ya Allah._

*SADAUKARWA*

_na sadaukar ga ƴan uwana musulmai baki ɗaya._

*MARUBUCIYAR*

“`NAFEESAT

LABARIN DEEBIZAH

JARUMAI

RAYUWATA

NUSNIM

BUTULCI

SO MAI ZAFI.“`

.

     *CHAPTER 4*

Gani yayi kuma Motan tayi revers tajuya da gudu ta tafi, ahankali yasauke ajiyan zuciya yatada nashi motan yaci gaba da tafiya, agaban wani ɗan madaidaicin gida yatsaya, har ya buɗe ƙofan zai fita wayan sa tafara Ringing, dakatawa yayi yakalli wayan dake ajiye a gefe, ganin sunan BILKISU ya fito asaman screan ɗin yasanya shi jan gajeren tsaki yafice tare da rufo ƙofan, direct gidan yanufa yashiga da sallama a bakin sa, matar dake zaune bakin ƙofanta ta’amsa mishi cike da fara’a tana faɗin

“Maraba lale Ibrahima sannu da zuwa”.

Tana maganan ne tana janyo tabarma dake kusa da ita

“Zauna mana anan”.

Cire black Combat ɗin dake ƙafan sa yayi yasamu waje yazauna yana faɗin

“Ina yini Baaba?”

“Lafiya lau Ibarahima, yagida ya aiki? Da fatan kowa dai yana lafiya ko?”

“Alhamdulillah Baaba”.

“Ai jiya naji ka shiru bakazo ba, ince dai lafiya?”

Ɗan gajeren murmushi yasaki yace

“Lafiya lau Baaba, ban samu daman zuwa bane shiyasa, da fatan babu wata matsala baku nemi wani abu ba?”

“A’a wlh Alhamdulillah, Nazeefa ce dai ma tafarka ajiyan take neman ka, kuma daga baya sai barci yaɗauke ta, koda tafarka kuma yau bata tambaye ka ba ko magana ma batayi ba”.

Ajiyan zuciya yaɗan saki kana yace

“Ina ga yau zan tafi da ita, Nagode sosai da taimakon ki Allah yasaka, ga wanna babu yawa”.

“Ikon Allah bawan Allah baka gajiya? To Nagode Allah yasaka, ai babu komi yiwa kai ne, ita kuma Allah yabata lafiya”.

“Ameen”. Ya’amsa ataƙaice yana miƙewa

Itama tashi tayi tana faɗin

“Shiga tana ciki ai”.

Be ce komi ba yashiga, yarinya ce da bazata gaza 16yrs ba a kwance akan katifa, fara ce sol sai dai shatin kwarmin idanunta yaɗan yi baƙi-baƙi kaɗan, barci take yi hankalinta kwance, ahankali yamatsa kusa da ita yasanya hannayen sa yaɗauke ta cak ajikinsa yafito, har waje Baaba Talatu tarako shi tana ta saka mishi albarka tare da godiya ga ɗawainiyan da yayi mata

A back sit yakwantar da ita kana yashiga yaja motan ahankali kamar yanda yasaba, shiru yayi yana nazarin abinda yakamata yayi, ta cikin mirror yake kallon ta duk da baya hango ta sosai, but jefi-jefi yakan kai idanun sa kanta.

A bakin Gate yadakata yayi hon, ba daɗewa aka wangale mishi gate ɗin yatura hancin motan ciki, a packing space yatsai da motan, sai da yaɗan yi minti 3 kafin yabuɗe motan yafito da ƙafan sa, wayoyin sa yaɗauka yashigar dashi cikin aljihu kana yafito yabuɗe bayan mota yana ƙoƙarin fito da ita, ahankali tabuɗe idanuwanta tasauke kan kyakkyawan face ɗin sa, hakan yasaka taɗan saki murmushi ahankali tace

“Yayana”.

Shima murmushin yasakar mata yaɗan ja jikin sa daga ɗaukan ta da yayi ninya yace

“Nazeefa.. kin tashi?”.

Gyaɗa masa kai tayi still tana murmushi

“Ok fito ahankali muje ciki, yau na dawo dake gida na, anan zamu ci gaba da zama kinji?”

Nan ma gyaɗa masa kai tayi kafin tayunƙuro tatashi tafito daga cikin motan, ahankali take kallon cikin gidan kafin tamai da idanuwanta kan sa, murmushi yasakar mata kana yariƙo hannun ta suka taka ahankali suka nufi cikin gidan, a main palow suka tsaya yanuna mata kujera yace

“Zauna anan”.

Ba musu tasami waje tazauna tana ci gaba da kallon Palon don ba ƙaramin burge ta yayi ba, sosai yatafi da imanin ta, tsarin Palon da kayan cikin kan shi abun burgewa ne da sha’awa, fridge yanufa yaɗauko faro water yadawo yazauna gefen ta, miƙa mata yayi ta’amsa tana sakar masa murmushi, shi kuma wayan sa yazaro cikin aljihu yaɗan latsa yakara a kunne

“Ina kike?”

“Ok kizo palow Ina jiran ki”.

3minute tafito cikin ɗakin ta, har gaban sa taƙarisa taduƙa tace

“gani Sir”.

“Kikai ta ɗakin ki daga yau zakici gaba da kula da ita, zuwa anjima kiyi ma drever magana yakai ki super makert duk wani abun da take buƙata kisiyo mata”.

Ita sai lokacin ne ma takalli wajen da Nazeefa take zaune, a ranta tana tunanin “to wacece ita awajen shi?”

Batakai ga ƙarisa zancen zucin nata ba taji muryan sa yana ma Nazeefa magana

“Tashi kibi ta ciki”.

Babu musu tatashi, itama Lubna miƙewa tayi takama hanyan ɗakin ta Nazeefa na biye da ita abaya, da ido yabi su da kallo har suka shige kafin yasauke ajiyan zuciya, tashi yayi yanufi cikin ɗakin sa, wanka yayi yasauya kaya cikin ƙaraman t.shirt fara da yellow ɗin Three qweater, yafito palow yanufi saman dainnig yasami waje yazauna, tea cup yahaɗa yafara sipping yana latsa wayan sa, tsawon mintuna ashirin yaɗauka awajen kafin yamiƙe yanufi cikin ɗakinsa, be fito ba sai da aka kira sallan magriba kafin yaɗauro alwala yasanya jallabiya fara sol yafito yanufi masjid, sai da aka yi isha’i kafin yadawo, yana shigowa yatarda Nazeefa zaune saman kujera ta ƙudundune jikinta tana kallo, shigowan sa yasaka taɗago kai tana kallon shi, kujeran dake gefen ta yasamu yazauna yana kallon ta

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button