NOVELSUncategorized

GIDAN UNCLE 47

*G.U*

Dagowa yayi da sauri ya kalleta hawayen da yake qoqarin hadiyewa suka zubo masa yace “nima jin abin nake kamar tatsunniyar tsoffi bloody waini Hameed Adam Hameed Shuwa zaa sake  daurawa aure da wata watanma wai Salma Umaimah wannan abin da ciwo Allah Kaine ka halliceni ka halicci Salma Allah indai da nufin cutar dani da matata jinina takeson shigowa gdana Allah kayimin maganinta Allah kafimu sanin abinda ke boye game da wannan masifaffen auren Allah ka kawomin dauki Allah idan na tuna da yau zaa dauramin aure da wannan baiwa taka Allah zuciyata zafi takeyi bloody ciwon zuciyata neman tashi yakeyi” 



Cikin kuka da baqin kishi da tausayin kanta ta daure daqyar bisa taimakon addu’ar da takeyi a zuciyarta tace “kayi hqr” iyakar kalmar data iya furta masa kenan yayi parking a asibitin ya kashe motar ya ruqo hanunta qamqam a cikin nasa jikinsa na wata irin rawa yace “a… akwai matsala Umaimah dauki wayata ki bude ki kiramin Dr Saleem Umaimah yi sauri zuciyata zata tarwats….” 



Yana fadin haka yana qara qanqameta qirjinsa yana bugawa da qarfi, cikin Kaduwa da tashin hankali ta lalubo number Dr Saleem din ta kirashi bugu daya ya daga ta kara a kunnenta yace “hello ango mijin amarya amma Umaimah nake nufi…” Da sauri ta katseshi da cewa “na shiga ukuna Dr bloody mutuwa zaiyi zuciyarsa ke masa ciwo…” a firgice yace “what? Umaimah kuna Ina?” Cikin kuka tace “muna cikin asibitinku ya kawoni a dubani kuma shima yace zuciyarsa tarwatsewa zatayi jikinsa sai rawa yakeyi” da sauri ya kashe wayar ya fito kafin yazo tuni Hameed ya gama fita daga hayyacinsa amma duk da haka tana maqale a jikinsa yaqi sakinta sai kuka takeyi tana jijjigashi tana danna masa masa qirjinsa saboda tasani tun tana qarama idan ciwonsa ya tashi haka takeyi masa.




 Qarasowar Dr ne yasata ta zare jikinta daga nasa daqyar daidai lkcn kuma wayarsa ta shiga ring batabi takan wayar ba sai taimakawa Dr Saleem data shigayi suka fitar dashi aka dorashi a kujerar tura marasa lfy suka nufi heart attack word da gudu takebin masu turashi din saboda suma gudun sukeyi suna shiga suka nufi emergency din word din suka kwantar dashi suka fara bashi taimakon gaggawa daqyar Dr Saleem ya lallabata sukaje itama ya dubata ya tabbatar mata tana da shigar cikin sati biyu da kwana biyu tayi farin ciki amma damuwar da take ciki ta danne farin cikin ta fitowa tayi ta zauna a reception tayi tagumi daidai lkcn Daddy ya shigo asibitin lkcn 11:30am yayi parking ya shiga word din da sauri hango Umaiman ne yasashi nufarta da sauri yace “mamana meye ya kawo tashin ciwon nan wlh ina kwance a gda Alh Jamilu ya kirani yake fadamin an taru gurin daurin aure shida zai karbi abinsa baizo ba so shine naketa kiran wayarsa najita a kashe na fito na nufo gdan naku don nasani yanda yake dumin wannan qaddararren auren lfy bazata hanashi fitowa ba Ina zuwa Zarah take sanar dani kun tafi asibiti so shine na Kira Dr yake fadamin ke ya raqo a dubaki saboda yana zargin kinada shigar ciki kuma sai ciwonsa ya tashi meye yayi dalilin hakan?” 



Miqewa tayi ta shige jikinsa ya rungumeta sosai ta saki wani marayan kuka tace “Daddy na tabbatar da bloody bayason Salma Daddy bayason auran Salma kuyi masa sauqi wlh qaddararmu ce Salma ni dashi Daddy ya sanar dani komai ya fadamin yanajin tsanar Salma a cikin jininsa amma kuma yakasa bijiirewa auran ta baya tunata idan baya tare da ita sai ta kirashi kota nemeshi kuma idan ta kirashi baya iya bijirewa umarninta Daddy ba fushi zakuyi da Bloody ba addu’arku yake buqata wlh Daddy baya cikin hayyacinsa kagafa yanzu kawai mgnrta nayi masa ciwonsa ya tashi wannan wacce irin masifa ce Daddy me Salma take nufi damu? Meyasa ta nace sai ta shigo cikinmu ta rusa mana farin cikinmu?”



Ajiyar Daddy yayi me qarfi ya sanya hanunsa ya dagota ya fara share Mata hawayenta yace “akwai manufar wannan shedaniyar yarinyar akansa koma dai menene yau dai an daura aure Umaimah tun lkcn da Hameed yayi min mgnr auran yarinyar nan na nuna rashin amincewata amma naga ya dage nasan tabbas akwai matsala so nayi qoqarin tursasashi amma yaqi Umaimah an tsaface mini da an sanya masa ya daina jin tsorona dagani har mahaifiyarku yama daina zuwa inda muke saboda zamu fada masa gsky Hajiya tace jiya ta kirashi tace ya sakeki saboda bazaki zauna da muguwar yarinyar nan ba da Sunanta yayi tambari ta fitar da mace a gdanta kota hanyar saki kota haukata kota kashe abune me sauqi a gurinta amma yaqi yace tayi masa uzuri ku hakan bazai faru daku ba saboda kun fahimci juna kuma kin bashi hadin kai shine ta kumayi masa rantsuwa akan saiya sauwaqe miki bazai kasheki da baqin cikinsa a banza ba Umaimah bayan qiyayyar Salma da ciwon auranta dakecin zuciyarsa harda wadannan kalaman na Hajiyanku addu’a kawai ya kamata muyiwa Hameed saboda kansa na cikin tukunya baya cikin hayyacinsa nasa ma da sauqi saboda qarfin kariyar farko da kuka samu daga kakanku musamman ke da kike mace da abin sai yaci uban haka ki qara hqr Umaimah mijinki yana sonki da izinin Allah komai zaizo qarshe bada dadewa ba”




Da wadannan kalaman ya rinqa kwantar Mata da hankali har yasamu yaga ta nutsu sannan ya zaunar da ita ya shiga ciki yaji dadin ganin jikin Hameed din bai tsananta sosai ba har yadan dawo hayyacinsa yana shiga ya zuba masa ido saida ya qarasa gabansa ya kamo hanunsa yace “sannu babana kuma ango Allah ya sanya alkhairi” kallon Daddy yayi da sauri yace “an daura ne?” Murmushin takaici Daddy yayi yace “to me zaa jira tunda kabada komai Allah dai ya tayaka ruqo ya baka ikon kwatanta adalci babu wata nasiha da zanyi maka tunda kai ba baqon riqe mace biyu bane amma wannan takun yana da bambamci da takun zaman Sadiya da Umaimah dole ka sanya ido a gidanka tunda ka nace hadasu zakayi Hameed kada naji kada na gani wlh har idan kakai hqrn Umaimah qarshe wlh babu ruwana zan cire hanuna daga lamarinka da ita gabadaya na zuba muku ido saboda itama yace kuma tanada yanci” 



Numfashi ya sauke me wahala yace “ina take Daddy cikine da ita ko?” Kawar dakai yayi yace “tana waje bansani ba saboda bamu samu ganawa da likitan ba amma dai bata cikin nutsuwarta akwai damuwa sosai a tattare da ita Hameed ina qara jaddada maka girman amanar dake hannunka ba iya mata kawai take a gurinka ba qanwa ce kuma yace sannan amanar Allah ce” yana gama mgnr ya juya ya fita tana ganinsa ta miqe tayi gurinsa tace “ya tashi Daddy?” Murmushi yayi yana jinjina girman qaunar dake tsakanin yayan nasa yama rasa tsakaninsu waye yafi qaunar wani.
Jinjina mata kai yayi ta nufi dakin da sauri tana shiga ta nufi gadon baiji shigowarta ba saboda duniyar tunanin daya lula saida yaji ta rungumeshi ta karkatar da kanta daidai fuskarsa gabanta ya fadi sosai ganin hawaye a idonsa tasa harshenta ta lashe tace “nayiwa mijina kuma dan’uwana alqawarin zan bashi matsala ta kowanne bangare ba” matsata yayi s jikinsa yace “na gde bloody I love you so much” shigowar Dr Saleem da Daddy ne yasata miqewa a kunyace ta koma gefe ta zauna sukayi murmushi dukkansu Dr Saleem ya dubesu yace.




 “Ya kamata ku cirewa kanku damuwa ku karbi duk abinda ya fado rayuwarku a matsayin qaddara Hameed rayuwarka tana cikin barazanar katsewa indai bazaka daina sanya muguwar damuwa a zuciyarka ba kasan matsalarka yakama komai ka rinqa maidashi abin wasa sannan matarka tana buqatar kulawa saboda nagani blood pressure dinta ya hau sosai sannan ga jaririn ciki komai zai iya faruwa saboda haka kuyi taka tsantsan dukkanku kunada matsalar da batason damuwa” hakanan sukayi sallama dashi suka tafi bayan ya dorashi akan magungunan da yakesha   idan irin wannan matsalar ta taso.



Itace take driving din yana zaune a gefe Daddy kuwa gda ya wucce suna tafe kamar kurame babu wanda ya iya cewa da wani komai suna shiga get din gdan gaban yayi wata muguwar faduwa saboda ganin dayan bangaren cike da mutane ana shiga da kaya da qarfi taci wani uban birki ta juyo ta kalleshi shima ita din ya kalla da sauri yace “ Innanillahi wa innah ilaihir raji’un bloody kinga har sun kawo kayanta wayyoh nikam na shiga ukuna wannan wacce irin qaddara ce” wani matsiyacin kallo ta watsa masa ta bude motar da sauri zata fita yayi saurin riqo hanunta yace “kiyi cooling mind dinki bloody kada su gane rauninki suje su fada mata don Allah na fada mata cewa matata halin nana Fadimatu (R.A) ne da ita inasonki kema kinasona kuma kinason farin cikina kina tayani son duk abinda na kawo Umaimah dole ne kishi kuma halal ne nima bazanso ace baki kishina ba amma kiyi qoqarin danneshi ki barshi iyakar ni kada mubada qofar da zaa samu a shigo mana da baraka cikin gdanmu don Allah wlh nafiki kishin kaina Umaimah ji nake kamar na kashe kaina jinake dama na mutu na dawo duniya a wani bani ba mai tarin qaddarori marasa dadi Umaimah dama mu mutu kowa ya huta tunda mun kasa samun farin ciki a duniya qila mu samu a lahira……









 *UMMUH HAIRAN CE…✍????*

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button