DIREBAN GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVEL

DIREBAN GIDANMU COMPLETE HAUSA NOVEL

Duk kansu suka mik’e tsaye..
“Zan iya aurenshi tunda ba haramun bane”

“Kin ga sai a buga a jarida da gidan radio cewar ga wata ta auri direbanta”

‘Daga hannu tayi zata mareta,Raihan tayi saurin rik’e hannunta.

“Ki sakeni in nuna mata kuskaranta meyasa zaki hanani Raihan?”
Tayi maganar tana zubda hawaye.

Nan da nan jama’a suka taru.

Lubna kuwa tayi ta fad’a tana cewa a barta taga me zatayi mata,dan Asara ta rasa wa zatayi soyayya dashi sai drivernta.

Kuka sosai Janan take yi,Raihan tayi saurin janyeta suka shiga cikin lecture hall d’in.

Tunda ta shiga kanta yake a k’asa tana kuka,su Khalid ‘yan dprtmt d’insu suka zo suna tambaya amma Raihan tace su k’yaleta kawai dan kar abin ya sake damunta.

“Gaskiya lubna bata kyauta ba ai babu dad’i dizgi”
Zakiyya tayi maganar lokacin data dafa Janan.

“Ki k’yalesu kawai na San dole zasu shirya sun samu tsab’ani ne kawai”

Janan ta d’ago kai ta kallesu,fuskarta sharkaf da hawaye tace “a cikin taron jama’a tayi min haka,to zan aure shi zanyi soyayya dashi inga abinda wani zaice ko kuma naga abinda zatayi sai ta kaini gidan radio da hujja” hawaye ta goge ta d’auki jakarta ta fita.

Raihan na mata magana ta shareta kawai.

Napep ta tara abinda bata tab’ayi ba,kwatance tayi masa ya kai ta har k’ofar gida.

Tayi knocking maigadi ya bud’e ganin itace yasa shi saurin matsawa.

Tana shiga taga Ali zaune a kan bencin maigadi.

Ta d’an kalleshi fuskarta d’auke da hawaye,shima idonsa a kanta yake,kamar zata masa magana sai kuma kawai ta wuce ciki.

“Uhmm yarinyar nan akwai rigama”

“Da wulak’anci ba”,Ali ya fad’a yana kallon inda ta wuce

” ai bata da wulak’anci akan yayarta”

“Allah ya shirya”
“Amin”
Maigadi ya amsa.

Tana shiga bata Tatar da kowa a falo ba,dan haka tayi saurin wucewa bedrum d’inta.

Wani sabon kukan tayi mai isarta sannan ta shiga toilet ta watsa ruwa..

Tana fitowa taje bakin mirror ta tsaya tana murza mai a jikinta ta kalli madubi taga yadda fuskarta ta d’an kumbura.
Mai ta murza a jikinta ta fesa turare sannan ta zura doguwar riga nylon ta fita.

‘Dakin mameey ta wuce,tarar da ita tayi a kwance hannunta d’auke da waya da alama ta gama amsa kira ne.

Zama tayi kusa da mameey tayi shiru na tsawon lokaci sannan tace “mameey bakiga na dawo ba?”

Tashi tayi zaune ta kalleta tace “mamaki kika bani ai”

Murmushin k’arfin hali tayi sannan tace “mameey ina son in fara sanin yadda talakawa keji,saboda ban San inda rana zata fad’i ba”

“Amma kin San wannan ganganci ne ko?kin san halin babanki sai yayi fad’a”

“No mameey pls karki fad’a masa kinsan zaiyi fad’a”

“Oh kinsan da hakan amma kika dawo ba ki kira an d’aukeki ba?”

“Am srry Baran kuma ba”

“Ki kiyaye”

“Insha Allah mameey”
“Yawwa”
“Mameey ina Aunty Fauzah?”
“Tana skul”
“Okay Yaya yana office ba?”
“Kema ai kin Sani”

Hira suka cigaba dayi cikin raha da annashuwa.

Ranar dai haka ta yini duk abinda take sai ta tuno Ali direba har ta fara zargin kanta akan maganar lubna.

    *********

Tana jingine da fuskar gadon hira suke k’asa-k’asa.

Fauzah dai duk ta rasa mafita gaba d’aya gani take kamar abinda take shirin yi ba mai d’orewa bane.

“Gaskiya ina tsoron abinda nake shirin yi Zuby”

“Ban gane tsoro ba”
“Saboda duk abinda nake yi ina yinsa ne a b’oye wallahi duk ranar da aka gane na shiga uku,musamman Janan da ta samin ido zata Iya b’aro jirgina”

“Hmmm Fauzah kenan,Janan kike tsoro k’aramin alhaki,kefa macece karki bani kunya mana”

“Amma zuby karki manta direban gidanmu ne fa”

“Sai me a ciki,naga shima d’in d’an hannune da kinje masa da buk’atarki zai biya miki”

“Ta ina zan fara”
“Ki fara kamar irin kina son shi sai daga baya kina saka kayan da zasu ja hankalinsa kin gane ai”

Murmushin k’asaita tayi sannan tace “zan k’ok’arta”

  **********

Yau da wuri ta shirya dan bata so tayi latti.

A gurguje ta kammala break fast sannan ta samu mameey a d’aki tayi mata sallama.

“Kin fad’ama driver?”
“Eh tun jiya na ce masa ina da lecture k’arfe 8”
“To Allah ya tsare”
“Ameen mameey”

Da saurinta ta fita dan gani take kamar zai gudu.

Tana isa taga ya bud’e mata back seat duk sai taji ba dad’i duk da dama haka yake mata ko yaushe..

Sun fara tafiya tana son tayi magana amma zuciyarta na bugawa haka tayi shiru ta kafa masa ido yana driving abinshi.

Suna shiga gate a dai-dai central mosque tace ya tsaya

Parking yayi kamar yadda ta umarceshi,ta d’auki jakarta har ta fito sannan ta juyo tace “kayi hak’uri da duk abubuwan da nayi maka insha Allah bazan sake ba,zan kiraka idan mun gama lectures”

“Masoya yau kuma anan aka keb’e”

Da sauri suka juya suka kalli ko wacece dama ita Janan ta san itace.

Alk’alamin Sadeey
[9/6, 10:08 AM] prince_s_square: ????????????
DIREBAN GIDANMU
????????????

by
SaNaz deeyah????

Dedicated 2 Mrs Xerks & Safnah luv

02

Suna shiga falo ta zube ta fara dirzar kuka.

Da sauri mameey ta taso ta rik’eta tana tambayar abinda ya faru.

Fauziyya ce tayi mata bayanin komai.

Janyo Janan tayi tana rarrashi tare da fad’in “ki daina musawa babanki Janan kin san shi baya da wasa kuma kaifi d’aya ne”

Ta d’ago idonta da suka gama rinewa tace “akan direba Abba zai mareni,ya zubar min mutumci a gabanshi”

“Ya isa haka kiyi hak’uri”

Ranar haka ta yini a bedrum d’inta tana kuka,ko abinci sai da aka tilasta mata sannan ta fito taci.

Bayan sallar isha’i Abba ya sa aka kirawota,nasiha yayi mata sosai akan babu kyau wulak’anta d’an Adam sannan kuma ya rarrasheta har zuciyarta tayi sanyi,fahad kuwa gaba d’aya lamarinta haushi yake bashi.

        ******

Haka ta hak’ura Ali ya cigaba da kaita makaranta amma kullum cikin zaginshi take tana nuna masa tsana k’arara.

A satin kuma aka sayowa Fauzah motarta sabuwa k’yal k’irar ‘prado’.

Yau ma kamar kullum tana zaune a bayan mota tana latsa waya shi kuma yana driving a nutse.

‘Dago kai tayi ta kalleshi tare da jan dogon tsaki “dalla malam kayi da jiki sai jan mota kake a k’asaice kamar ta tsohonka,Malam kar kasa na makara fa”

Da sauri yaja burki ya tsaya yana kallonta.
“Kallo na kake? To ko motar babanka ce kaifa direbana ne wall…………”
Wuyanta ya shak’o Wanda ya hana ta k’arasa maganar.

“Karki k’ara ambatar mahaifina ki zaga” sakin wuyan yayi ta zaro idonta a tsorace cike da mamaki tace “ni ka shak’e?to wallahi a bakin aikinka”

“Zan miki abinda yafi shak’ewa idan har kika cigaba da zagin babana”

“Ni kam yau sai ka bar aiki a gidanmu tunda har kasan shak’a to tabbas zaka iya kisa”

“Na yarda zan bar aikin koda kuwa baki saka an koreni ba ni zan bar gidanku da kaina” ya fad’a yana goge hawaye.

Abin ya mutuk’ar bata mamaki ganin yana zubda hawaye gaskiya yana son shi da yawa ta fad’a a zuciyarta.

Har suka je skul ba wanda ya sake yima wani magana tana son ta bashi hak’uri amma tana ganin kamar zai rainata ne.

Tana fitowa daga motar su Raihan suka k’araso,Lubna tayi saurin k’arasa jikin motar tace “sannu Aliyu ina yini”
“Lafiya lau ya karatu?” Ya amsa cikin sakin fuska.

“Karatu Alhamdulillah ya mantawa dani”

Da sauri Janan ta juya suka had’a ido tayi saurin janye k’wayar idonta daga kanshi.

“Ban manta dake ba saboda kina da matuk’ar mahimmanci a gurina”

“Nagode da wannan matsayi da ka bani”
“Nine da godiya”
“A’a ni dai Dana samu kyakykyawa handsome yayi appreciating d’ina”

“Lubna idan kin gama surutun ki samemu a hall”
Janan ta fad’a ranta a b’ace dan tana jin haushin yadda lubna ke kuranta Ali har tana fad’ar yana da kyau a gabanshi salon ya raina masu aji.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14 15 16 17Next page

Leave a Reply

Back to top button