NOVELSUncategorized

RAINA KAMA (BOOK 1) 9&10

????????9
     …….K’yaleta nayi najuya sit d’in bayanmu Na fusge ta hannun wani guy, rubutun farko dage jikin jaridar a shafin farko na tsirama idanu.

*_BABBAR MAGANA, GALADIMA SAMEER RUNGUME DA MATASHIYAR BUDURWA A PLAZA ‘DINSA SUNA SUMBATAR JUNA!!_*
    sai kuma hoton dake k’asan rubutun  shima har kala biyu, Na farko abinda yafarune na fad’uwar Munubiya a birnin gayu plaza, har Galadima yay yink’urin taimakonta amma tadafe baskets ko ta6ata ma baikai gayiba, amma abin mamaki da al’ajabi a hoton galadima ya rungume munubiya ne bakinsa akan nata.
    Hoto nabiyu kuma ni da shi ne afilin idi lokacin damukayi karo har wayarsa ta fad’i, ko kad’an bai ta6aniba, ko waya daya kar6a a hannuna hannuna danashi basu had’uba, amma anan an nuna hoton yana rik’e da hannuna duka biyu muna kallon juna.
     “Innalillahi” nafara maimaita jikina har yana rawa, gawata uwar jufa data fara jik’a sassan jikina, lallai dolene duk inda muka gitta abimu da kallo.
    Ju yowa nayi na kallo munubiya dake tsaye a bayana, itakam hawayema takeyi.
    Jikina a sanyaye nakama hannuta muka fita daga cikin hall d’in, kallon da ake Manama ayanzu yafi na d’azun, Dan labarin sai kuma yad’uwa yakeyi yanzun.
     Muna fitowa muka samu taxi sai gida.
    Tunda muka sauka naga wasu gungun samarin dake layinmu a majalissarsu sun zubo mana idanu gaba d’aya, tuni zuciyata tafara tsitstsinkewa, kenan labarin harya iso nan?. Dagani har Munubiya jamukai muka tsaya, saboda ganin dukkan ahalin gidanmu tsaye cirko-cirko a tsakar gida, hardasu yaa hameed anguna, ga bak’i dabasu gama tafiyaba, innarmu kwance akan tabarma maman fauziyya namata fifita, ga Abbanmu kusada ita tsugunne yana shafa mata ruwa.
      Jaridar dake hannun baba k’arami mukabi da kallo, bansan sanda wani kuka yatahominba nima, sa6anin da munubiya kawai keyin kukan.
     Da gudu mukayi kan innarmu, amma sai yaa hameed ya daka mana tsawa, “karku sake Ku ta6ata wlhy, idan bahakaba jikinku kuwa saiya fad’a muku”.
     Babu shiri mukaja burki, amma sai muka durk’ushe ak’asa muka fashe da kuka.
     Innro tace, “kwayi kuka kuwa munafukai, ahiyyasa ai ANNABI yace a auri mace tagari, Dan ‘ya’ya susami uwa tagari, yo wannan aimu ba sabon abu baneba agaremu, tunda dama halin uwarku kenan, itama saida tagama tambad’arta a titi aka k’ak’abama d’ana”.
      Rintse idanu nayi saboda yanda maganganun innaro ke sukar zuciyata. Dady yakatseta da fad’in “dan ALLAH inna kiyi hak’uri kibar maganarnan”.
        “hameesu barni nafad’i gaskiya, wannan abin kunya har ina, wai jikokinane yau aka buga ajikin jarida namiji rungume da d’ayarsu a titi” ta face hanci tana share hawaye da bakin zani, “ALLAH ya wadaran irin wannan rayuwa taku kuda uwarku, kun jawo mana abunkunya, yanzu dawane ido duniya zata cigaba da kallonmu” feeet, takuma fyace majina”.
     Mudai ni da munubiya muna durk’ushe rungume da juna Luna rairai kuka maiban tausayi dacin zuciya, yayinda ‘yan gidanmu da sauran ‘yan biki suketa k’us-k’us a tsakaninsu.
    Isowar likita yasa aka kama innarmu aka maida falon Abba, a sank’ame take tamkar gawa….
.............
*_GAGARA BADAU PLACE_*
      Shirye-shiryen komawa India yakeyi hankalinsa kwance, Dan yau zai koma ga mahaifansa da ‘yan uwansa dake can, jirgin k’arfe 8pm zaibi.
    Yana gama had’a ‘yan abubuwan dazai iya buk’ata yadawo falo ya zauna, sanye yake cikin farare k’al d’in kayan Adidas na training, dogon wando da Riga mai dogon hannu, yasaki hular abaya, kayan sun masa k’yau sosai.
      Kallo d’aya yayma abincin dake kan center table d’in ya d’auke kansa, cikin k’asaitacciyar muryarsa mai cikeda isar masu mulki naji ya furta “Saykin k’ofa”.
     Kai kace anmasa dolene saiyayi maganar.
     Da hanzari sarkin k’ofa yashigo falon, ya zube a k’asa “barka da hutawa ya shugabana”.
       Kansa kawai ya jinjina, sannan yace, “waye yakawo abinci nan ne?”.
         “ya shugabana bansan daga ainahin wane 6angare bane, amma bayin dasuka kawo daga 6angaren sarauniya Zulfah ne”.
      Baice komaiba ya d’aga masa hannu alamun yatafi.
     Sai da yad’an rissinar da kansa alamar girmamawa sannan yamik’e, dokace agareshi shi bayason kirarin da akema ‘yan gidan sarautar. dan haka basa yimasa shi, Saboda gudun 6acin ransa.
      zamewa yayi yay kwanciyarsa akan doguwar kujerar ya lumshe idanunsa batareda yabi takan abincinba.
     Sallamar sarkin k’ofa tasakashi bud’e idanunsa akansa, ya amsa sallamar bisa la66ansa, sarkin k’ofa yazube agabansa, cikeda girmamawa yace, “ya shugabana yalla6ai Muftahu yace amasa iso gareka”.
      Alama yamasa akan yabada izinin ya shigo.
     Fita sarkin k’ofa yayi. babu dad’ewa saiga Muftahu yashigo da sallama, Galadima yabud’e idonsa yana kallonsa tareda amsawa.
     Zama yayi kujerar dake kallon Galadima, yace, “yalla6ai barka da hantsi”.
      Murmushi Galadima yayi, ya tashi zaune sosai yana fad’in “my man daga ina haka naganka ayikice? bakaje aikibane?”.
       Ajiyar zuciya Muftahu ya sauke, yacije le6ensa na k’asa yana mik’ama Galadima jaridar dake hannunasa, “nafita wlhy sainaci karo da wannan jaridar data fito a safiyar yau”.
         Cikin halin ko inkula Galadima yace, “Miye had’ina da jayidan to?”.
       “Kayi hak’uri ka kar6a ka duba”.
    A shafin farko yay karo da abinda yasakashi sake kallon Muftahu, kai Muftahu ya d’aga masa alamar yacigaba.
  *_ANYI WALK’IYA…., GALADIMA DA AIKA-AIKA A FILIN IDI_*
   cikin hanzari yabud’e shafin farko, nankuma an saka.
  *_BABBAR MAGANA, GALADIMA SAMEER RUNGUME DA MATASHIYAR BUDURWA A PLAZA ‘DINSA SUNA SUMBATAR JUNA!!_*
    sai hoton farko dana biyu, wad’anda suka d’aure kansa, danshi gaba d’ayama ya manta daduk abinda yafaru, tundaga na birnin gayu plaza harna filin idi d’in. d’agowa yay yakalli Muftahu sannan ya maida kallonsa ga dogon rubutun da akai akan sharhin hotunan. bazai iya karanta rubutun ahakaba, saiya fara waige-waigen neman medical glasses d’insa.
     Fahimtar haka da Muftahu yayi yace, “ina yake in d’auka maka?”.
      Da hannu ya nuna bedroom d’insa ba tare da yace komai ba.
    Mik’ewa Muftahu yayi yanufi bedroom d’in, babu dad’ewa saigashi yadawo, ya mik’a masa sannan yakoma inda yake da ya zauna yana fad’in “ko ka kawo na karanta maka”.
      Nanma baice uffanba yamik’a masa jaridar, kansa ya maida jikin kujerar ya jingina ya lumshe idanunsa.
    Tiryan-tiryan Muftahu yafara karanto k’aryar da aka jera jikin jaridar, ko sau d’aya bai motsaba, amma yana saurarensa.
     Muftahu yagama cikin sauke ajiyar zuciya, Amma tabbas wannan wata k’ullaliyace, ai ba abinda yafaru kenanba jiya a birnin gayu, ni nama rasa mizan cema wannan gidan jaridar wlhy”.
        Galadima ya bud’e idonsa dake a lumshe, ya kad’a yay jajur saboda 6acin rai, akan Muftahu ya saukesu batareda yace komaiba, tuno abinda yafaru a filin idi yayi kusan sati 4 kenan, tabbas sunyi karo da yarinya, wadda ayanzu haka ko fuskarta bazai iya tunawaba, dan ko’a waccan ranar kallo d’aya yamata, a jiya kuma ko ta6a yarinyar baiyiba ALLAH ya kareta daga fad’uwar dazatayi. jinjina kansa yayi cikeda 6acin rai da mamaki.
      Muryarsa a sark’e yace, “Muftahu imason bayanai akan yayannan najikin jayiday su duka”.
       “ok yalla6ai, amma ai yarinya d’ayace duba kagani”.
      Kar6ar jaridar yayi yakuma kallon hotunan, tabbas duk yarinya d’ayace, wannan ya sake tabbatar masa da an shirya masa hakanne.
    Mik’ewa yayi yazari mukullin mota batareda yace ma Muftahu komaiba, ganin haka shima Muftahu saiya mik’e yabi bayansa.
         Cikin sauri dogaren dake binsa inhar zai fita suka taso gareshi, amma saiya d’aga musu hannu.
     yana k’ok’arin bud’e motarne Jakadiyya ta iso inda yake…
     Cikin rissinawa tace, “barka da hantsi galadima”.
     Bai iya amsa mataba, sai hannu daya d’aga mata kawai.
    Kuma rissinawa tayi tace, “Galadima takawane yabani izinin in kirayeka”.
     Kallonta yayi zaiyi magana saikuma yay shiru ya maida motar yarufe tareda cillama Muftahu dake bayansa kyes d’in.
    Muftahu ya cafe.
  
  Komawa yayi 6angarensa yashiga wanka, kusan mintina 40 sannan yafito sanye da bathrobe fara k’al, bai wani d’au dogon lokaciba yay shiri cikin k’ananun kaya, yayi k’yau sosai, ya feshe jikinsa da turarensa masu matuk’ar k’amshi.
    Wayarsa ce tashiga ringing, baibi takantaba yacigaba da hidimarsa, dama tun yana bathroom yakejin ana kiransa.
        ta baya yabi inda bayi bazasu isheshi da gaisuwa gaisuwa d’innanba, dayake sarki yana gida, yau ana hutun zaman fada saboda tunawa da abinda yafaru da tsohon sarki (mahaifin Galadima  Sameer) duk ranar litinin tana zama ranar daba’a zaman fadane…
.........
       Kowa ya ganmu yasan muna cikin rud’ani, da k’yar aka samu innarmu ta farfad’o, sai dai an hanamu mushiga mu ganta.
     Gidanmu kam abin nema yasamu, hakama cikin anguwa, saboda yad’uwar labarin a social Media.
     Muna zaune a falo duk mun zabga uban tagumi dagani har munubiya, idanunmu duksun kunbura saboda kuka, Ni ba abinda yafaru a jaridar ne yafi damunaba, halin da mahaifiyarmu ke ciki shine babbar matsalata, bamuda kamarta duk duniya, bazanso wani Abu ya sameta asanadinmu ba, bayan bak’incikin datake k’unsa agidanmu kuma.
     Kamar anjeho mama Rabi’a itada ya Marwan suka shigo falon. mun tsorata kwarai da gaske, cikin daka tsawa mama Rabi’a take tambayarmu innarmu.
     Hakanne ya tabbatar mana da suma labarin yaje musu. munubiya ce tabata amsa cikin kuka, sannan tace “wlhy mama sharrine, ba abinda yafaruba kenan n……”.
      Saukar marin datajine yasakata rufe bakinta 6am, kafin na tantance mai Marin nima naji saukar nawa.
    Ko kad’an yaa Marwan baiji tausayinmu ba, saida yamana lik’is da duka, dak’yar Dady ya kar6emu a hannunsa, amma baba k’arami da Abbanmu casukai yama k’ara mana.
    ‘Yan gidanmu duk sunfito cirko-cirko a tsakar gida, kowa na tofa albarkacin bakinsa, gashi akwai sauran ‘yan biki dabasu gama tafiyaba.
    Iyayenmu da yayinmu duksun taru akanmu, ana tambayarmu wacece daga cikinmu.
    Kafin Munubiya tayi magana nayi saurin cewa “kuyi hak’uri iyayena, nice munaya a gaba d’aya hotunan, wlhy kuma tsautsayine, amma ba ainahin abinda yafaruba kenan”.
        Munubiya zatayi magana nayi sarin rik’e hannunta alamar kartace komai, “karki d’aurama kanki abinda ba laifinkiba Munubiya, nice Munaya na aikata….”
     Itama cikin kuka tace “wlhy bake baceba, nice, wlhy nice”.
     Nima nace “wlhy nice”.. ….
    Tsawa Abbanmu yadaka mana, atare mukayi shiru yace “nasan dama Munaya kece, Munubiya bazata aikata wad’annan abubuwan ba, dukda kema d’in nayarda da tarbiyyar dana baki, amma bansan miya kaiki ga aikata hakanba, shiyyasa ranar idi mukaita nemanki, Ashe kinacan kina d’akko mana magana, tunda aure kikeso zan miki, nabaki nanda sati 2 kacal, inbaki kawomin mijiba zan had’aki dadu Wanda nayi niya”.
      Yana gama fad’ar haka yatashi ya fice, baba k’arami ma ficewarsa yayi.
    Wani kuka mai tsuma rai muka kuma fashewa da shi, musamman ma ni danasan nasaka kaina a tarko, amma hakan shine dai-dai, bazan amince naga ‘Yar uwata cikin bak’in cikiba, insha ALLAH koma minene zan jureshi, muniya tanada hak’urin dazai iya cutar da ita akan wannan lamarin, gashi baba yafurta in ban fiddo da mijiba zai auramin Wanda yaso, to idan hakan ta kasance kan Munubiya wane hali kuke tunanin zata shiga? Musamna dabamusan gidan dazamu iya fad’awaba tunda nasan abinda Abba yafad’a tabbataccene, dan shi baya magana biyu.
     Dady ne yashiga lallashinmu, tareda mana nasiha da nuna mana illar abinda muka aikata, musaman ma ni. ya Marwan kam sai antayamin harara yakeyi shida yaa hameed.
    Yinin yau kam kuka muncishi harmun godema ALLAH, mu duka kwance muke rijif da zazza6i, har akayi isha’i bamu kumajin motsin kowaba, mukuma muna d’aki kwance mu duka k’udundune a bargo.
    Su Aryaan sunacan nanuk’e da innarmu dake 6angaren Abbanmu har yanzun, dan haka 6angarenmu saiya kasance tsitt. a ranar dai haka muka kwana babu lafiya nida Munubiya, babu mai iya taimakon wani acikinmu, ga yunwa ga damuwa ga ciwo.
      Zuwa asubahi ko salla kasa gashi muyita mukayi, dan k’arfinmu yagama k’arewa…????
..........
         Ya isa sassan mai martaba, bayan masu tsaron k’ofa sun gama kwasar gaisuwa suka masa iso.
    Izinin shiga mai martaba yabashi.
      Falone k’aton gaske, Wanda nikaina banmasan yanda zan musalta k’yansa da girmansaba, ga kujeru rukuni-rukuni, ko ina yagama d’umamewa da sanyin AC, gawani k’amshi na musamman.
     daga can gefe na hango mai martaba kishingid’e bisa wani lallausan carpet da aka k’awata da tarin tum-tum, gabansa tirene dake d’auke da jug na glass cikeda zo6o, sai wani k’aramin kwano na tangaram Wanda bansan miye acikiba, saikuma k’aramar butar shayi awani tiren daban, da mug guda d’aya.
      Fuskarsa d’aure take tamau alamar yana cikin 6acin rai, ga jarida a hannunsa.
        Cikeda girmamawa Galadima ya zauna a gefen dardumar, ya tankwashe k’afafunsa sannan ya risina yana fad’in “barka da rana ranka ya dad’e”.
         Mai martaba bai amsaba, sai ma cilla masa jaridar hannunsa dayayi.
     Galadima yabi jaridar da kallo batareda ya d’aukaba.
       “ka d’auka ka duba mana, dan inason sanin gaskiyar zancen”.
      Kan galadima a k’asa yace, “takawa nima yanzu Muftahu yakawo min nagani, nama fito zanje ga gidan jayidayne kiyanka ya isomin, amma wlhy Abba ba gaskiya baneba, ka…….”
       Da sauri mai martaba ya d’aga masa hannu cikin 6acin rai “mi kakeson fad’amin? kana nufin zasu buga abinda baka aikata bane? ai sunsan gidan daka fito, haka kawai bazasu maka sharri ba kodan gudun abinda zaije ya dawo. Sameer yanzun nan da mutuncinmu kaje ka aikata wannan son zuciyar domin ka 6atama wannan masarautar suna? Lallai kacika d’an halak, kuma kayi dai-dai, tabbas ka kafa tarihin dawani bai ta6a yin irinsaba a wannan masarautar, Dama Ashe kabud’e waccan plaza d’inne domin son zuciyarka? Yanzu da ace lafiyar Yaya k’alau wane irin hali kake tunanin zai tsinci kansa? Ina ganinka shiru-shiru Ashe kaid’in shaid’anine”.
     Runtse idanu Galadima yayi zuciyarsa na k’una da kalaman mai martaba k’anin mahaifin nasa, amma yagaza furta komai, sai idanunsa daketa k’are rinewa zuwa jajazur.
     Har mai martaba yak’araci fad’ansa yagama Galadima bai iya furta komaiba, kansa ak’asa ko motsi baiyiba.
      “katashi kabani waje, k’arfe 8:30pm akwai meeting, saika jira hukunci daga mama Fulani ”.
       Rissinar da kai Galadima yayi yace, “ALLAH ya huci zuciyayka, na bayka lafiya”.
       Banza mai martaba yay masa, yatashi yafice shikuma cikin k’unar zuciya.
     
    Yana fita wayarsa ta fara ringing, ransa adagule yacirota da nufin kashewa gaba d’aya, saiyaga *_My dear Momma_* rintse idanunsa yayi ransa nakuma suya, yasan tabbas labari ya Isa gareta kenan, wannan wace irin masiface, mahaifiyarsa dake wata k’asa har ankirata an Sanar mata, ko halin datake ciki baza’a kallaba?. Kasa d’aga wayar yayi harta tsinke.
    Tabbas duk Wanda yake gidan jaridarnan saiyayi Dana sanin saninsa arayuwa.
    Kiran Momma ne yakuma shigowa, yanzuma bai d’agaba harya k’arasa sashinsa.
     Sai da ya zauna sannan yafara k’ok’arin nemanta cikin suyar zuciya data ruhi……………????
To masu karatu, ko wanene da wannan aika-aikar? tabbas yau Munaya tabani matuk’ar tausayi daga ita har munubiya, kai harma Galadima.????????
Kumuje zuwa danjin Yaya kuma zata kasance?????????.
Yanzufa aka fara wasan????????????♀⛹????♀⛹????????????
*_YA ALLAH ka gafartama iyayenmu????????????_*
[4/16, 9:53 AM] +234 811 277 0720: *_Typing????_*
  *_HASKE WRITERS ASSO…????_*
       _(Home of expert and perfect writer’s)_
       *_RAINA KAMA……!!_*
               _{Kaga gayya}_
         *_Bilyn Abdull ce????????_*
????????????
     …….Maman Fauziyya ce taga shirun yayi yawa narashin gittawarmu ta aiko Kamal yagani muna nan, dan ita azatonta ko mama Rabi’a tawuce damu gidanta ne.
     Da gudu yakoma ya sanar mata gamucan babu lafiya a d’akinmu.
    ai bata tsaya jin k’arshen zancenba ta garzayo, halin data iskemu aciki itama hankalinta yakai k’ololuwar tashi, takira baba k’arami a waya tana Sanar masa, duk da haushinmu dayakeji hakan bai hanashi shiga tashin hankaliba shima. atare suka shigo da dady, shima abbanmu sai gashi yashigo.
     Duk kuma jikinsu sai yayi sanyi, aganinsu yakamata su sauraremu ajiyan, amma duk da haka babu iyayen dazasuga wannan abun hankalinsu bai tsashiba, garashi d’an manyan mutanene, nashi mai sauk’ine, amma mune awahale.
     Haka aka kira doctor yaduba mu, yace damuwace ta haddasa mana zazza6in, sai kuma yunwa.
     Da k’yar maman fauziyya ta taimaka mana mukayi wanka da ruwa mai d’umi, sannan mukayi sallar asubahi. tea ma dak’yar muka shashi sannan mukasha magani, still kwanciya muka k’arayi, nan barci ya kwashemu.
    Dadyne ya kalli ‘yan uwansa, cikin damuwa yace, “yaya Auwal yanzu bazamuyi wani yunk’urin bincike akan lamarinnan ba? ni dai sainake ganin kamar yarannan bazasu aikata hakaba, tsawon shekaru muna tare dasu, bamu ta6a jin makamancin abinan ba daga garesu, sainake ganin bai kamata mu yanke hunci ba akan abinda bamuda tabbas kuma cikin fushi”.
       “Hameesu karka goyi bayansu akan wannan lamarin, babu yanda za’ayi abuga labarinan alhalin bai faruba, kaduba fa shi yaron d’ane ga Sarki, shinema Galadima, kodan tsoron abinda zaije yadawo ai nasan gidan jaridarnan saji tsoron buga labarin”.
      “hakane yaya, amma baka ganin mak’iyanshi zasu iya amfani da wannan damar domin 6ata sunansa? maybe kuma su yaranmu tsautsayine ya gitta akansu”.
         “maganarka gaskiyane Jafaru, nima wlhy hakan nake tunani, amma yakamata mujira muji daga gidan Sarki, Dan inhar Dan 6ata sunan yaron akayi nasan bazasu k’yaleba, kuma zasu nememu”.
     Ajiyar zuciya Abba ya sauke yace, “nidai koma minene gsky aure yakamata ayima Munaya, Dan nikam banta6a cin karo da abinda ya rud’ar daniba irin wannan, mahaifiyar yarannan wlhy batayi barciba jiya, kwana tayi kuka, kuna ganin dai irin cin zarafin da inna tadinga mata jiya a tsakar gida gaban kowa, shin minene laifin A’isha akan wannan lamarin? zata aiki su Munubiya ne akan suje su aikata hakan?”.
        “kayi hak’uri yaya, lamarin inna sai hak’uri, kasan dai halinta ai”.
      Haka sukaita tattauna yanda zasu 6ulloma lamarin.
...........
      Jiki a sanyaye ya danna kiran Momma, bugu biyu ta d’aga, cikin girmamawa ya gaidata, ta amsa itama cikeda kulawa kamar yanda ta saba. hakanne yad’an sakashi jin sanyi a zuciya, ya sauke ajiyar zuciya yana fad’in “Momma ya jikin Abie?”.
      “Alhmdllh Moh’d. wani mummunan labari yanzu Ummu Erfaan takirani take sanarmin?, sai kuma ga mama Fulani ma takira tanata fad’a. yanzu kuma Sauban ya nunamin wasu pictures wai an turo masane”.
        Rintse idanunsa yayi cikin k’unar zuciya, murya a sark’e yace,  “Momma nima haka kawai nagani”.
        “ban gane kaima haka kaganiba Moh’d, kagayamin gaskiya please, wannan ba k’aramin Abu bane bafa”.
        Da k’arfi ya cije lips d’insa tamkar zai hudashi da hak’ori, cikin wata murya dake nuna k’ololuwar 6acin ransa yace, “Momma wlhy bansan komaiba, yanay idi tabbas munyi kayo da wata yayinya hay wayata tafad’i ta fashe, jiya kuma yayinya takusan fad’uwa a plaza nayi yink’uyin taimakon ta saima ALLAH yasa bata fad’iba, kuma ko ta6a banyiba, shine kawai yau gidan jayiday nan suka maida pictures d’in haka fa”.
       Ajiyar zuciya Momma ta sauke, (dan tarigada tasan halin d’an NATA, duk da ba’a shaidar d’an yau musamman idan yabar gaban idonka) “Muh’d tabbas wannan k’ulline, amma kuma yarinya d’ayace ai”.
      “haka nagani nima Momma”.
     “yanzu mi sarki yace?”.
      “Momma wlhy maganay babu dad’inji, hayma sun shiyya meeting a kaina”.
         “Humm Muh’d wannan maganace mai girma, kuma tabbas domin 6ata sunanka ne da namu akayi, akwai kuma dalilinsu nayin hakan, ita wannan yarinyar kodai da saninta kokuma an shigo da itane saboda cikar manufarsu”.
       “Momma su waye to?”.
        “Masusan ganin bayanmu mana, sun biyo wannan hanyarne domin dak’ileka da ragema kaifi”.
      Wani naushi ya kaima k’aramin teble d’in gabansa na glass, nan take ya tarwatse. bai damu da ciwon dayajiba, cikin k’araji yace, “tabbas kafin suga bayana nizanga nasu!!! rayuwar mahaifina bazata salwanta abanzaba!! Saina wulak’anta dukkan masu hannu aciki kosu waye su wlhy billahi Momma! numfashina fansa akan mahaifina!!”.
       Dole Momma tacire wayar daga kunnenta saboda yanda Galadima ke magana cikin matsananciyar tsawa.
     Saman kujera ya wurga wayar, batareda ya katse kiranba, afusace yafito daga 6angaren nasa, tsawa ya dakama dogaransa.
        Gaba d’ayansu cikin rawar jiki suka nufi motocin da ke fake a wajen, ko jira abud’e masa baiyiba yabud’e yashiga.
    Hankalinsu a tashe yake daganin yanayin shugaban nasu, sunsan tabbas ran ‘yan maza ya 6aci yau, Dan kowa yasan rashin son hayaniya irinta Galadima a masarautar nan.
           Saida suka fito daga masarautar a d’arare sarkin mota yace, “ranka ya dad’e ina muka dosa?”.
      Tamkar bazai tankaba, sai kuma can afusace yace, “plaza!”.
       “angama Ranka ya dad’e, ALLAH ya huci zuciyarka ya shugabana”.
     Banza yamasa bai tanka masaba, sai huci yakeyi yanna karkad’a k’afafu da taunar lips, idonsa yayi zajur saboda masifar 6acin rai.
      A plaza ma tunda yashigo kowa ya fahimci yanda cikin 6acin rai, Dan ko kallon masu gaisheshi bayayi, mutane masu siyayya sai kallonshi sukeyi, dama wasu gulmace takawosu dansu k’ara ganema idonsu akan labarin da ayau yazaga ko’ina da ina. kai tsaye wani Office yashiga.
       Cikin hanzari Wanda yake a office d’in yamik’e domin kwasar gaisuwa, sai dai yanayin ogan NASA yayi masifar rikitashi.
    Bai saurari gaisuwarba yace, “inason ganin abinda yafayu a CCTV tundaga safiyay jiya hay daye”.
      Jiki Na rawa guy d’in yace “angama ranka ya dad’e”.
    Kujera ya jawoma  Galadima ya zauna, sannan yagyra zaman computers d’in wajen sosai, tariyo wa yafarayi cikin nutsuwa, saida yadawo Sunday morning 6pm sannan ya saki, tundaga bud’e plaza har zuwa masu share-share da goge-goge dasukayi aikinsu, har lokacin da masu sayayya suka fara Shiga da fita a plaza d’in, har an wuce yace “dawo baya kad’an”.
       A slowly yadawo bayan kad’an, har zuwa kan wasu samari biyu d’aya sanye da jallabiya d’ayan wandon Jeans da farar t-shirt.
      “kayo zooming d’in yayannan dake tsaye sunan waige-waige”.
     Zooming d’insu yayi, sannan yasanya play yanna tafiya a slow.
     Samarin sunata ‘yan kalle-kallene, saikuma zuwa can d’aya yasaka waya a kunne yana magana da kallon cctv camera d’in dake hasko tsakkiyar plaza d’in Inda motoci ke Parking, saikuma ya janye idonsa ya maida kan motocin dakeJere a wajen. da ganin Kasan yana maganane, Dan d’ayan dasuke tare yanata gyad’a Kansa alamar gamsuwa da abinda d’an uwansa yake fad’a.
     Galadima Na zaune shiru, idonsa nakan computers d’in yana nazarin gayun har aka wuce Kansu, baice uffanba yacigaba da kallon shigi da ficin jama har zuwa 8:11pm, daga nan Computer tayi d’iff.
         Da Sauri Galadima ya kalli sarayin “mi yake fayuwane?”.
       “Ranka ya dad’e wlhy nima ban saniba, amma bara Na duba”.
      Danne danne saurayin yafara da ‘yan dube-dube, babu wata matsala daga nan.
    Kallon Galadima yayi yace “ranka ya dad’e babu wata Matsala daga nan, sai dai Idan daga cameras d’inne”.
       A tsawace yace “bangane mikake nufi daga cameyas d’inne ba!? Kenan hay shigowata jiya babu kenan!? kuma kana zaune a office amma bakayi complain ba tun ajiyan? mika aikata!!? mi suka baka ne domin tozarta ni!!? nace nawa suka baka Saleem!!!!?”.
      Kusan duk Wanda ke cikin plaza d’inan a yau yaji wannan hargagin Na Galadima.
        Jikin matashin saurayin ne yafara rawa, ya zube a k’asa gaban Galadima saboda tsabar tsoratar dayayi da yanayinsa, tunda yake aiki a k’ark’ashinsa baita6a ganinsa cikin wannan yanayin irin Na yau d’inna ba, duk da labarin abinda yafaru yazo kunanensu, sunkuma ganin a jarida da social media baiyi zaton lamarin zaiyi zafi hakaba.
     “wlhy yalla6ai babu Wanda yakeda abinda zai sayeni na cutar dakai, Kaine ka ceci rayuwata daga garari, ka tallafi maraicina a lokacin da nake Neman lalacewa saboda rashin matallafi, kazama gatana nida mahaifiyata da k’annena, mizaisa nabiyema rud’in wasu akan 6ata maka suna….”
     “ya Isa haka!!”. ‘galadima yafad’a cikin tsawa’.
       Gaba d’aya Galadima ya birkice musu a plaza, yasa securitys d’in wajen da dogaransa sun kori dukkan masu sayya dake ciki, ya tartare ma’aikatan wajen a d’aya, ya tabbatar musu da in har munafukan cikinsu da aka had’a baki dasu basu fidda kansuba gaba d’aya sai sunyi dana sanin saninsa.
      Kaf d’insu sun rud’e, sai rantse-rantse da k’ok’arin kare Kansu sukeyi, amma yak’i saurarensu, ganin zasu kuma dagula masa lissafi saiya basu suspension kawai aka rufe plaza d’in baki d’aya.
     Motocinsa Na k’ok’arin barin wajen motar Muftahu tashigo.
     Muftahu ya faka motarsa waje d’aya suka fito shida Harun, (shima Harun abokin Galadima ne makusanci, Dan zan iya cewama yafi sanin sirrin Galadima fiye da kowa a abokansa gaba d’aya, shi d’an waziri ne).
    Tunkan su k’araso Galadima ya sauke glass d’in motar da kansa. kallo d’aya sukai masa duk suka tsorata, Dan basu ta6a ganinsa a irin wannan 6acin ranba, baice uffanba, sai nuni daya musu akan su shigo motar.
    Basu musaba suka bud’e suka shiga, Muftahu a gaba, Harun yashiga baya kusada Galadima.
      Bayan gaisuwa dasukayi garesa babu Wanda Yakuma cewa komai, Dan ko gaisuwar bai amsa musuba, hannu kawai ya d’aga musu.
      Sun hau titi sarkin mota yace “Ranka ya dad’e ina muka dosa?”. ‘cikin girmamawa da taka tsantsan yay maganar”.
    Murya a shak’e yace “gidan Jayiday”.
    Sarkin mota bai fahimtaba, amma yana tsoron tanbaya, murya k’asa-k’asa ya tambayi Muftahu ”.
     Murmushi kawai Muftahu yayi yana girgiza kai, shiya shiga yima sarkin mota kwatance har suka Isa…..
.........
      Muna tsaka da barci saboda allurar da doctor yamana Innaro tafad’o d’akin, babu ko tausayi tashiga tashinmu cikin d’ad’d’aka mana duka a baya da cinyoyinmu.
    Dagani har Munubiya a firgice muka tashi zaune.
       “kutashi munafukai, Ashe abin ba a iya runguma da kama hannu ya tsayaba harda ciki kuka kwaso mana?, tsinannun gayyar tsiya, wlhy dagaku har uwarku yau saikin bar gidanan, a yau d’inan idan ubanku bai saki uwarkuba kun tattara kun tafi saina tsine masa albarka, yazo yaza6a ko Ku ko ni yau agidanan. sai kuma tafashe dakuka, takama bakin zaninta datayo lullu6i tana sharar hawaye, “kai ni dai Malam ya cutar dani akan had’a wannan aure da d’iyar marasa asali, ai gashinan ta Haifa mana bala’i da masifa, shikuma yatafi yabarni da kunyata, Malam kacuceni katafi kabar mana baya da k’ura. Wlhy yau sai A’isha tabar gidanan itada gayyar tsiyar ‘ya’yanta, natsaneku daduk wandama zai soki A’isha, natsaneku wlhy, takuma fashewa da kuka.
       Tuni matan gidanmu kowa yafito, wasu harsun shigo falonmu, wasu kuma Na daga k’ofar d’aki,  harda tsirarin ‘yan biki da sukak’i tafiya domin tsayawa kallon kwaf.
     Cikin matan gidanmu ne wata taje tasanarma innaro wai bamuda lafiya munata amai duk abinda mukaci, anakiran likita ya dubamu yace duk munada ciki wata uku-uku.
   
   Ni da Munubiya mun had’e kai muna kuka mai tsuma rai saboda tozarcin da innaro kemana muda mahaifiyarmu agaban bainar jama’a.
    Dady da Abba k’aramine suka shigo sunama innaro magana akan bafa haka zancen yakeba, babu Wanda yace munada ciki.
    Hayayyak’o musu tayi tana zaginsu, wai k’aryane suna kare Innarmu ne, aida likitan bai fad’aba baza’aje a sanar mata ba.
     Cikin 6acin rai baba k’arami yace, “inna waye yaje yafad’a miki wannan maganar to?”.
        “cikin matan gidanan mana, kuma daga bakin wadda nasan bazataimin k’aryaba”.
     Ran Dady ma a wannan karon ya 6aci, afusace yace, “inna wacece acikinsu? Wace ‘Yar isakar matace”.
        Nanafa matan gidanan mu suka shiga raba idanu akan juna.
     Innaro tace “karka kuma zaginta, idaba ayiba bazatace anyinba, kuma koma wacece bazan fad’aba, idan kuma ni kake zagi sainaji?”.
     “ALLAH ya huci zuciyarki inna, ni yaza’ayi Na zageki”.
     “kai dai kasani sakarai”.
    Duk abinda ke faruwa Abbanmu da Innarmu Na saurare daga d’akinsa amma acikinsu babu Wanda yayi yunk’urin fitowa.
    Kayanmu innaro tafara kwasa tana watsowa waje, wai saimun bar gidan.
   “Innalillahi wa inna’ilaihirraji’un, wannan wane irin tashin hankaline?”. ‘innarmu tafad’a cikin matsanancin kuka’.
    Rungumeta Abbanmu yayi shima yana k’ok’arin maida kwallar data cika masa idanu.
    Ganin abin yana Neman wuce gona da iri baba k’arami yafita da hanzari, wani tsoho dake can k’asan layinmu yaje ya d’akko, tsohon abokin Malam faruku ne na k’ut da k’ut, shika d’aine zai iya takama Innaro burki kuma.
    Aiko hakance ta kasance, tunda yashigo yay magana Innaro ta dakata da abinda takeyi tana huci da fidda numfashi.
    Tsoho Malam Labaran yace, “haba innar jafaru, da hankalinki da girmanki kike aikata wannan abin Na yara a gaban sirikanki da ‘ya’yanki da jikokinki? Shin babu mai fad’a miki kijine wai kekam?”.
        Cikin sassauta murya tace, “malam mai kanwa nasan bakasan ainahin abinda yafaru bane kaima, amma wlhy da dakanka zakace Auwalu yasaki marar asalinnan sukama gabansu itada ‘ya’yanta am…..”
        Hannu ya d’aga mata, yagyara tsayuwarsa jikin sandarsa dake taimaka masa tafiya, naji komai innar jafaru, amma wannan hanyar da kuka biyo ba wai itace mai 6illewa ba, bincike yakamata ayi domin asan gaskiyar lamarin. dan haka zoki wuce gida, zuwa gobe zamu tattauna akan lamarin sannan kowa ya nutsu, mukuma jira abinda zai fito daga can gidan Sarkin”.
     Badan innaro tasoba tafice, hakama matan gidanan mu basuso wasan yak’are iya nanba, sunso a yau Innarmu tabar gidan da saki, sannan mukuma mahaifinmu ya koremu. Kowa taja k’afa takoma d’akinta cikeda takaici da addu’ar ALLAH yasa daga gidan sarkin suma su d’auki mummunan mataki akanmu…..
Maman fauziyya Ce kawai ta nuna damuwarta akan lamarin
..........
  
      Su Galadima ma sun isa gidan jaridar  *Manuniya* tun sanarwar isowarsa ta kad’a hantar cikin ma’aikatan wajen, musamman wad’anda basuda laifi akan lamarin, tirsasu akayi.
     Shi kansa manaja d’in wajen a kid’ime yake, dukya rikice yarasa matsugunni har Galadima da gayyarsa suka iso office d’in bisa jagorancin sakatare d’insa.
     K’asa yazube kawai yana kwasar gaisuwa wajen Galadima, ko kallo bai ishi Galadima ba, cikin daka tsawa yafara magana………..????
Tofa masu karatu, ko manajan jaridar MANUNIYA zai amsa laifinsa? Kokuwa zai fad’i wad’anda suka sanyashine inba laifinsa bane shima? to koma dai shima da had’in bakinsa?. Wane mataki masarautar su Galadima kuke ganin zata d’auka akansa? Shin ina ma maganganun Momma suka dosa ne? Miya faru da mahaifin Galadima har suka koma k’asar India da zama?.????
Kumuje zuwa my guys danjin yanda zata kaya. da amsoshin d’unbin tambayoyinkun nan.????♀⛹????????????
_Naga mutane basa fahimtar yaren yarima????, yarima later R ne baidashi, bawai tsamin bakine dashiba fa, kun gane, naga wasu kamar suna zaton tsamin bakine dashi????._
  _Ngd da comments d’inku, kuna sakani farin ciki sosai, kuyi hak’uri da rashin amsawa ta, kunada d’unbin yawane wallahi????????????????????. I love you wujiga-wijiga all????✋????._

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button