Lu’u Lu’u 10

Wani malalacin murmushi yayi yace” Kenan dole sai nayi magana da baki?”

D’aga kafad’a tayi tace” Haka kawai na ji bai min ba da ka min magana da ido.”

Girgiza kai yayi saboda fara hawa masa kai da tayi ya nuna mata k’ofa yace” To ta fi.”

Zura dogayen k’afafunta ta fara yi ta masa bye bye tace” Saida safe.”

Saida ta kai daf da k’ofa zata fita yana k’are mata kallo yace” Barka da zagayowar ranar haihuwarki.”

Juyowa tayi da fara’arta tace” Merci beaucoup.”

Juyawa tayi ta fita a d’akin saidai kafin ta rufe kofar ta sake kallon shi, murmushi ta sakar masa tace” Halinka ya had’u yallab’ai, kai mutumin kirki ne.”

Rufe k’ofar tayi ta fice shi kuma bai san sanda ya saki k’ayataccen murmushi ba har saida ya ji an sake kiran wayar, yana d’agawa cikin jin haushi Haman yace” Haba Umad, me ye haka dan Allah? Ya zanyi ta kiranka akan abu muhimmin amma baka d’aga min waya? Tun yamma fa nake kira.”

Cikin rashin jin dad’in rashin kyautawa yace” Kayi hak’uri Haman, wallahi na samu wani d’an had’ari ne sakamakon shigarmu jeji, amma da sauk’i yanzu.”

Cikin kulawa har ya manta da b’acin ranshi yace” Subhanallah, me ya sameka Umad? Kana ina yanzu?”

Girgiza kai yayi ya aje kofin hannunshi yace” Ba komai karka damu, na ji sauk’i yanzu ai, fad’a min ya ake ciki daga wajenka?”

Nannauyar ajiyar zuciya ya sauke yace” Umad munyi nasara da yardar Allah, adreshin unguwa da lambar gidan da gimbiya Zafeera take duk yana k’wak’walwata.”

Da k’arfi ya sauka daga kan gadon yace” Da gaske Haman? Ka samu? Ina take?”

Cikin farin ciki yace” E na samu, kuma abun farin cikin tana cikin garin da kai ma yanzu kake kamar dai yanda kayi hasashe tun farko.”

Cike da k’aguwa da zumudi da farin ciki yace” Da gaske Haman? A ina take? Ban adreshin?”

Murmushi yayi yace” Na yi tunanin haka dama, na so zuwa garin yau amma na ga zanyi dare.”

A k’age yace” Haman ba wannan na tambayeka ba, ina ne adreshin da zan sameta? Zan yi sammako na je na had’u da su.”

Dariya Haman yayi yace “Bayan kassuwar Buffar, gida mai lamba 115, amma Umad…”

Bai barshi ya k’arasa ba yace “Nagode Haman, zan kiraka zuwa safe.”

K’it! Ya yanke kiran ya shiga tattara komai na shi dake wurin ya fita a d’akin, likitar na masa magana amma ko kulata bai yi ba saida ya bar asibitin kwana kwanan.

*01/01/2021*

Tun gari bai gama wayewa ba d’aliban suka duk’ufa wajen gudu a filin makarantar, sun yi har sun fara gajiya amma yallab’ai Umad babu shi babu dalilinshi, cikin hakane Zafreen da tawagarta suka biyo ta filin zasu wuce.

Da gangan Zafreen ta bi ta inda Ayam ke gudu, Ayam kam na ganinta a cikin gudunta ta nemi kauce mata, amma dake neman fitina take da d’aukar fansa sai kawai ta tareta gadan gadan ta bankad’eta.

Fad’uwa ta nemi yi hakan yasa tayi baya tana tangal tangal, amma ikon Allah sai Ayam ta jawo hannun Zafreen hakan yasa suka fad’i tare k’asa.

A tare suka saki k’ara inda Zafreen ke kan Ayam d’aro-d’aro, da sauri su Laika suka kamo Zafreen ta mik’e tsaye, Ayam ma mik’ewa tayi tana kallon Zafreen d’in, hannunta na dama ta d’ora kan sark’arta tana k’ok’arin mayar da ita cikin rigarta dake riga biyu ce jikinta, d’aya ta sanyi mai zip a gaba sai k’aramar daga ciki.

A mugun razane kuma a kid’ime cikin tashin hankalin da Zafreen bata tab’a tsammanin fuskanta na ta ga wannan sark’a a wuyan Ayam wacce sark’a ce da ba ko ina ake samunta ba sai a wajen maccen data kasance mata a gurin sarkin Khazira, tabbas ana na bogi amma ta gasken kana ganinta zaka fahimceta, dan dutsen da aka k’era sark’ar da shi daga k’asan ruwa ake samunshi, had’akar lu’u lu’u da murjani ke samar da da dutsen sark’ar, hakan yasa Zafreen jin mugun jiri na neman kayar da ita ya tima a k’asa.

Kamar wacce aka tsoratar ko aka firgita ta juya tana fad’in “Ina! Hakan ba zai faru ba, ina!!!!”

Da gudu ta juya ta nufi hanyar da ake zuwa dan amsa kiran waya, su Laika ma da gudu suka bita suna kiranta, Ayam kam tab’e baki tayi ta gyara sark’arta ta juya a tsanake dan komawa b’angarensu dan ta gaji kam, tunda bai zo ba kuma shi ya sani.

Zafreen na zuwa a gigice ta shiga danna kiran lambar mahaifinta, tan fara kururuwa kam aka d’aga, a matuk’ar rud’e ta shiga fad’in “Pah, pah na ganta, na rantse da abun bauta Ghira na ganta, na ganta sanye da sark’ar Mah, na ganta da ido na.”

Cikin fitar hayyacin daya ninka na Zafreen sarki Musail ya amsa da “A ina? Ina kika ganta?”

Saida ta shiga yarfa hannaye tace “A makaranta ne, yanzu haka tana wajen motsa jiki, gudu take, Pah ita ce na rantse.”

Kamar zai fasa mata dodon kunne yace “Gamu nan zuwa, yanzu zamu zo Larhjadin d’in, waziri da Adah tun jiya suna nan dama, sun samu wasu bayanai akan ta.”

Da sauri tace “Pah indai suna nan su ma ai sun isa, ba sai ka zo ba Pah zamu kawo maka ita.”

Jim ya d’anyi sannan yace “Shikenan ‘yata, na yarda dake.”

Aje wayar ta yi ta juya ta kalli su Laika tace “Ina so na had’u da ita yanzu.”

Jinjina kai sukayi suka nufi inda suka barta, amma da basu sameta nan ba sai kawai Laika ta ce su tafi dan su ma lokacin na su darasin yayi, idan sun fito sun had’u da ita.

*A k’ofar* gidansu Ayam gari ya k’arasa wayewa Umad, safiya na yi ya danna k’ararrawar sanarwar dake jikin k’ofar, daga ciki ya ji an ce “Ana zuwa.”

Gyara tsayuwa yayi ya k’urawa k’ofar ido yana tunanin fuskar mahaifiyar ce ko ta ‘yar zai fara arba da ita dan mace ce tayi magana.

Gaba d’aya k’ofar Habbee ta wangale ta sauke idonta cikin na Umad da shi ma ya saka na shi a cikin na ta, ganin bak’uwar fuska ce sai ta saki murmushi tace “Yaro da me zan taimaka maka?”

Fuskarshi ba yabo ba fallasa yace “…

*Yar uwa kin biya na ki ne? To ki hanzarta dan jin me zai faru, ga Umad k’ofar gidansu Ayam yana neman Zafeera dan d’aukar fansa, ga sarki da mutanenshi ma daf da ita, shin wanene ma Umad d’in nan wai? Sai kin biya na ki zaki san haka.*

 

*Alhamdulillah*

[ad_2]

Previous page 1 2

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button