Lu’u Lu’u 12

A wani yatsine ta kalleshi inda Zafreen tace” Ni kuma me yasa kuka kawoni nan? Waye kai ma?”

Gyara tsayuwarshi yayi yace” Sunana Bukhatir, mai jiran gado a Egypt.”

Zafreen ce ta d’ora da” To ni kuma me na ke a nan? Ku maida ni makaranta mana, kasan ka mu su waye?”

A wulak’ance ya kalli Zafreen yace” Na sani, kuma a dalilin yawan fad’a da kike yi ne ya kawoki nan?”

Hanya ya nuna mata hanya yayi ba yanda ta iya dole ta shige gaba suka bi bayanta, kallon Ayam yayi yace” Ma pr茅cieux, zan turo hadiman da zasu kula min da ke yanzu, wannan shigar bata dace ki ba.”

Juyawa yayi zai fita Ayam tayi kukan kura ta shak’o rigarshi dam a hannayenta tana kallon fuskarshi tace” Babu inda zaka je sai ka mayar dani inda ka d’auke ni.”

Cikin matsanancin shauk’inta ya lumshe ido ya fara zura hannunshi akan cinyarta yana neman zurawa a cikin towel d’in, ido lumshe yace” Gashi kin kawo min kan ki, Zaf… Eera.”

Da sauri ta ske shi ta ja baya tana hararenshi, wani shakiyin murmushi yayi ya juya ya fita, da sauri ta kama k’ofar zata bud’e sai ta ji a rufe take gam, tsaki tayi ta shiga zagaya d’akin tana sln sanin a ina take? Me ta zo yi a nan? Su waye kuma take tare da su?

Bud’e k’ofar da aka yi yasa ta saurin juyawa, matasan mata ne su biyu da kayansu iri d’aya a jiki, da girmamawa suka rusuna suna gaisheta, cikin fad’a ta nufesu tana musu yarensu tace “Wai ku su waye? A ina nake nan ne?”

Nuna musu k’ofa tayi tace “Maza ku bud’e min k’ofar nan.”

Rusunawa sukayi a ladabce cike da tsoron kar su mata ba daidai ba ransu ne zai b’ace daga gurin mai gidan na su, d’aya daga ciki ce jikinta na rawa tace “Ranki shi dad’e yallab’ai ne ya umarcemu da mu tayaki shirya kan ki.”

A tsawace Ayam tace “Ranki shi dad’en banza, wane banzan shiri ne zaku tayani? Mu saka ce ni aka fad’a muku? Ko dama can fil azal ku kuke min wanka ne? Mtsssss!”

Rikicewa sukayi suka rasa yanda zasuyi, cikin hushi ta nufi k’ofar ta sake kamawa zata bud’e, amma sai ta ji ta gam ta k’i bud’ewa, a tsawace ta kallesu tace” Zaku bud’e min ne wai ko sai na bajeku a nan?”

Da sauri suka fara riga rigan bud’e mata k’ofar, d’aya a ciki ce ta d’ora hannu a k’ofar tare da danne wani mab’alli dake k’asan hannun k’ofar, bud’ewa tayi ta kauce mata a hanyar, ai kam ficewa tayi da sauri tana k’arewa tabkeken falon kallo, tsaye tayi ta shiga bin ko ina da kallo dan gaskiya d’akin ya birgeta sosai, tab’e baki tayi ta ci gaba da tafiyarta ta nufi inda take ganin nan ne mafitar.

Zata bud’e k’ofar kenan aka bud’e daga waje, cak ta tsaya ta zubawa mai shigowa ido, saidai sab’anin d’azu da fuskarshi ke d’auke da fara’a da annashuwa, yanzu kam fuskar a had’e take tam, yanda ta lura yana ta kallon bayanta ne yasa ta d’an juyawa, matasan matan nan ta gani duk sun zube k’asa kawunansu sadde jikinsu sai b’ari yake.

Juyawa tayi ta kalleshi sai kawai ta ja tsaki ta kula juyawa ta kallesu tace “Ku mik’e tsaye kunji, me ye na wani rusunawa har k’asa gaban mutum d’an uwanku.”

D’aya a ciki ce tayi k’arfin halin d’aga kan ta ta kalketa sai kula ta sunkuyar, muryar Bukhatir ce ta sa ta juyo sanda yake fad’in “Me na fad’a muku a kan ta?”

Jiki na kyarma d’ayar tace “Yallab’ai mun yi iya k’ok’arinmu amma ta k’i…”

Kashe fuskarta yayi da marin daya sakaya girgiza kamar zata fad’i kwance, a mugun hassale ya nunasu da yatsa yace “Ba k’ok’ari ba, abinda yasa na d’auko ku shi ne dan…”

Gauuuu! Ayam ma ta d’auke fuskar Bukhatir da mari, a wani irin razane matan da kuma dattijon ne dake bayansu suka kalleta, dan su kam yanda suke girmama Bukhatir ko sarkin Egypt basa girmamawa haka, idonshi da suka kad’a sukayi jajajir ya d’aga ya kalleta, ido cikin ido suka kalli juna babu mai alamar rusunawa.

Tunanin hanyar da zai fara hukunta ta yake, tunanin kalar muguntar da zai mata yake, hasaso hukuncin da zai mata yake wanda zaiyi sanadiyar ta fara kakkarwa sanda ta ji sautin muryarshi, amma ikon Allah sai ya ji ya kasa aiwatar da komai, sai ya ji wani tausayinta a zuciyarshi ya malayeshi sanda suka had’a ido, sai kawai ya d’auke hannunshi daga kuncin yana murmushin takaici, dan ko iyayenshi ba zai tuna ranar da suka tab’a marinshi ba, ba dan kar ya zama mak’aryaci ba sai yace tun na k’uruciya wanda bai san anyi ba ma.

Sake kallon fuskarta yayi yana lashe leb’enshi kafin yace “Idan har kina son barin nan sai ki fara bin duk wani umarnin da zan gindaya miki.”

A zabure tace “Kai a wa da zan bi umarnin ka?”

Sunkuyar da kai yayi k’asa yana murmushi kafin ya kalleta yace “Mijin da zai aureki.”

Da wani mamaki tace “What!”

Ba tare daya daina murmushin ba yace “Ba zaki gane komai ba a yanzu, ki fara shiga ciki ki shirya dan ki samu ki suturta min jikinki, idan kin fito zamuyi magana dake.”

Rumgume hannaye tayi tace “Kafin nan ka fara amsa min wad’annan tambayoyin nawa.”

Girgiza kai yayi yace “Zafeera mahimmanci gareki a wajena, idan na mayar dake sarauniyata ko fuskarki bana so kowa ya gani, ta ya zan yarda ki tsaya a haka wasu na kalleki? Kin san wacece ke kuwa? Kin san girma da matsayin darajar da kike da shi? Allah ya karramaki dan haka zan tayaki karrama kan ki.”

Cikin jin haushi tace” Tukuna ma wane banzan suna kake kirana da shi ne?”

Murmushi yayi mai kama da dariya ya juya zai fita yana fadin” Ki fara shiryawa sannan, zan amsa duk wata tambayarki.”

Da wata matsiyaciyar harara ta bi bayanshi har ya b’acewa ganinta, juyawa tayi a masifance tace wa matan” Sai ku tashi mu tafi ko? Zaku tsaya k’aton gardi na dukanku kamar ubanku, wahe shi ma tukuna?”

Yanda tayi tambayar tana rik’e k’ugu yasa d’aya a ciki tace” Kamar d’a yake ga sarkin k’asar nan.”

Yamutsa fuska tayi tace” Kama ne ma yake ba d’an sarkin bane, to wace k’asar ce wannan?”

D’ayar ce ta amsa da” Egypt.”

Da mamaki ta kallesu tace” Egypt? Kuna nufin nan a Egypt nake?”

Jinjina kai sukayi hakan yasa ta ita ma ta jinjina kai ta k’arasa bakin kofar d’akin, bud’e mata sukayi ta shige suka bi bayanta.

*Khazira*

A kausashe ya buga teburin yana kallon Adah da kan shi ke k’asa kamar zai fasa d’akin yace “Ta ya ya haka zai faru? Sai da na ce zan je da kai na kuka tabbatar min da zaku iya, yanzu me kuka aikata kenan?”

Cikin girmamawa Adah yace “Ka gafarce ni sarki, mun tarar da hatsaniya ne a makarantar, ga dukkan alama wasu abokan gabar ne suka fara ganota shiyasa suka tayar da zanga zangar, da haka kuma sukayi nasarar d’auke mana gimbiyoyinmu.”

Previous page 1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button