Lu’u Lu’u 14

Da sauri ta mik’e tsaye tace “Yallab’ai ya dai? Kana buk’atar wani abu ne?”

Dakewa yayi ba alamar rashin gaskiya tare da shi yace “E, ban d’aki.”

A ladabce tace “Yallab’ai ban d’akik bak’i ta can wajen ne.” Ta fad’a tana nuna masa k’ofa alamar sai ya fita, fuska a gimtse yace “Ban da lokacin da zan koma baya, ke baki san ujila bane.”

“To to shikenan, ga hanyar can yallab’ai.” Ta nuna masa d’akin tsakiya, hanya ya kama zai shiga sai kuma cikin ladabi tace “Yallab’ai.”

A gadarance ya juyo gareta, sake tausasa murya tayi tace “Ka bi sannu, domin madame na ciki, tana da masifa sosai, ka taimake ni kar kayi abinda zata hassala ta ja min uk’uba.”

Da ido ya mata alaar ba komai sannan ya sa kai d’akin, kan shi tsaye ya tura k’ofar, amma d’akin duhu kuma babu motsi, gefenshi ya kalla sai kuma yayi sa’a da makunnin, kunnawa yayi amma bai ga kowa ba a iya dubawarshi, k’arasawa yayi gaban ban d’akin ya d’an k’wank’wasa saboda jin k’arar ruwa, babu wanda ya amsa shi sai ya gyara tsayuwa ya d’an jira, ganin fa bai da lokacin jira yasa shi sake k’wank’wasa murya a tausashe yace “Jiranki fa na ke.”

Shiru ya ji babu wanda ya amsa mi shi, haushi ne yasa shi jan tsaki ya tura k’ofar yana zuba idonshi ta ko ina, sam babu alamar mutum a ciki, dafe goshi yayi ya furta “Ina kuma take?”

Rufe ban d’akin yayi ya juyo ya fito matar nan na mi shi barka da fitowa, bai kulata ba dan hankalinshi ba kan ta yake ba ya fice, wajen motocinsu ha nufa yana zuwa kuma sarki Wudar sun fito shi da Bukhatir daidai kuma da dawowar Zafreen ta saka kayanta wanda ta zo da su.

Fuska a had’e Umad ya bud’a motar ya shiga tare da mik’awa dreban daya kasa fita saboda singlet ce ta rage mi shi makulli, turus Zafreen ta tsaya tana kallonsu dan gaba d’aya kuzari ta rasa ta tunkararshi bare tasan a wacce a ke ciki.

Tana tsaye tana kallo suka gama sallamarsu duk suka shiga motocin suka d’auki hanyar barin gidan, Umad da ranshi ya gama b’aci tuni ya yanke shawarar zai raka mahaifinshi zuwa filin jirgi, daga nan zai san yanda zaiyi ya sulale musu ya dawo, dan yayi alk’awarin sai ya koma tare da ita, ba zai barta nan ba ko da zai shekara d’ari ne ko kuma hakan na nufin rasa rayuwarsa.

Sarki Wudar ma ya tafi amma fa yayi niyyar sai ya had’awa Bukhatir wata mak’ark’ashiyar da zata dawo da Ayam hannunshi, dan ba zai yarda ya rasata ba bayan shekarun daya kwashe na jiranta.

Suna isa filin jirgin dama an basu izinin tashi saboda an san da zuwansu, har farfajiyar jiragen aka bawa motocin izinin k’arasawa saboda sarki Wudar, duk firfita sukayi suka rufe motocin, sun fara takawa kenan sun bada baya suka ji an d’an bubbuga boot, Umad da dreba da sarki ne suka juyo, ganin ba komai sai suka juya suka ci gaba da tafiya, bubbugawa suka sake ji da k’arfi har da tagomashin ihu ana kiran “Kaiiiii! Taimako?”

Umad na d’aukar muryar ya dawo da gudu yayi azamar d’aga boot d’in, da wani irin k’arfi Ayam ta tashi zaune ta sauke kakk’arfan numfashi, kallonshi tayi idonta duk sun rikid’a tace “Da na mutu fa, kai akwai takura a cikin nan.”

Tattare rigar tayi ta zuro k’afafunta ta diro daga motar, Umad kam a bad’ini farin ciki ne ya kama shi, to amma mamakin yanda akayi ta shigo nan sai ya hana shi shak’at, da sauri sarki da sauran mutane suka k’araso, sarki Wudar da farin ciki a fuskarshi yace “Zafeera, ke ce dama? Ya akayi kika zo nan?”

Murmushi ta sakar masa ta tafa hannayenta tace “…

 

*Alhamdulillah*

The post Lu’u Lu’u 14 first appeared on 2gNovels.com.ng.

[ad_2]

Previous page 1 2 3

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button