Lu’u Lu’u 15

“Saboda ba shi nake da buk’ata ba.” Kallonta yayi yace “Me kike da buk’ata yanzu?”
D’auke kai tayi daga gareshi tace “Iyaye na, ina so na gansu, ka mayar dani wajensu ni har karatun ma na fasa.”
Girgiza kai yayi yana murmushi ya jawo wayarsa a gaban aljijunshi, tana kallo ya dinga danna wasu lambaobi, ko da ya danna ok ya mik’o mata wayar yace “Kiyi magana da su, hakan zai sa hankalinki ya kwanta.”
Da sauri ta karb’i wayar ta d’ora a kunne jin tana k’ara, ana d’auka cikin muryar kuka da sangarta tace “Hello!”
Cikin zumud’i da karsashi Habbee ta amsa da “Gimbiyata, gimbiya kina lafiya?”
Mik’ewa tayi tsaye tace “Mah ban da lafiya, gaba d’aya bana jin dad’i, so nake na ganku.”
Cikin ladabi Habbeetace “Kiyi hak’uri kinji gimbiya, zamu had’u nan kusa, ki kwantar da hankali ki saki jikinki da mutumin nan, mutumin kirki ne, na tabbata zai kula dake yanda ya kamata.”
Juyowa tayi ta kalli Umad sannan tace “Mah, ni ban yarda da kowa ba, maganar gaskiya ma a tsorace nake, wasu abubuwa ke ta faruwa a nan kuma babu wanda yake min bayanin komai.”
Daga b’angaren Habbee ta numfasa tace “…
*Kuyi hak’uri da wannan yan uwa, akwai gobe Insha’Allah*
*Alhamdulillah*
The post Lu’u Lu’u 15 first appeared on 2gNovels.com.ng.
[ad_2]