Lu’u Lu’u 6

Adah ya kalla yace” Kai Adah, ka mata jagora zuwa kurkukun k’asa na *Sabah*.”
Maida kallonshi yayi gareta har yanzu da numfashinta take fafutuka yace” Zaki d’and’ani uk’ubata Juman.”
Gefenta sarkin yak’i Adah ya tsaya hakan yasa ta kallonshi sannan ta kalli sarki Musail tayi dariyar mugunta tace” Uk’ubarka wacce ce ban sha ba ? Kai dabba ne ba d’an adam ba, kuma ‘yata tafi k’arfinka banza kawai.”
Kan ta ya sake yi da azama waziri dake ta rarraba ido tsakaninsu yana son fahimtar inda suka dosa ya shiga tsakaninsu, cikin d’aga murya sarki Musail yace” Ka fitar min da ita a nan, kuma na tsawon kwana uku ban yarda a d’iga mata ko da tafi d’aya na ruwa ba bare abinci, wannan umarni na ne.”
Fashewa tayi da dariya tace” K’arshenka ya zo Musail, na ga hakan nan ba da jimawa ba, ka tabbatar min da mafarkina zai zama gaskiya dalilin uk’ubar nan da kake neman sakani a ciki, tabbas ‘yata zata zo a dalilin haka, wannan shi ne ma’anar hannun da take mik’a min a cikin kowane mafarkina.”
Cikin ladabi Adah ya mata nuni da k’ofa, juyawa tayi da sauri ta shiga takawa tana fad’in” Ku zuba ido ku gani, da sannu sabon tsari zai zo a k’asar Khazira, ‘yata zata canza komai ko da hakan na nufin ta cire kawunanku ne, mak’ask’anta kawai.”
A dakonce waziri ya kalli sarki Musail da mamaki yace” Sarki na ka tabbata hukuncin nan ne ya kamaceta?”
A hassale yace” To da me ya kamata nayi?”
Dogon tsaki yayi ya nufi hanyar fita yana fad’in” Ka nemo min babban malami a duk inda yake.”
Sunkuyawa yayi yace” Angama shugaba na.”
Saida ya shige sannan ya d’aga kan shi, jiki a mace yana ta tunanin abinda ya faru yanzun ya fita isar da sak’on sarkin.
*Wannan littafi na kud’i ne, ku garzayo ku biya na ku dan jin yanda zata kaya, dan an kusa rufe free page, dan neman k’arin bayani tuntub’i lambar dake sama, zan ga masoyan k’warai da masoyan baka馃槀.*
*Alhamdulillah*
[ad_2]