Lu’u Lu’u 7

Khatar daya kasa anfanuwa tunda ta shiga kora masa bayani ko k’yabtawa bai yi sai yanzu, cikin fitar hayyaci da rashin sanin me ya fad’a yace “Ta musamman.”

“Me?” Zafreen ta fad’a a tsiwace, kamar mari ta gaura masa haka ya zabura ya juya ya kalli canal, cikin masifa ya shiga fad’in “Dama haka kake mata kashedin? Wai wannan wace yarinya c da kai kan ka ke tsoron had’a ido da ita? Me ta taka a k’asar? Dan gwamnati ta d’auki nauyin karatun ta ba shi ke nufin zata taka kowa ba, ka fad’a min wacece ita?”

Tsura masa ido canal yayi yace “Wacece ita?”

“E, wacece ita?” Ya fad’a a zafafe, numfashi ya sauke sannan yace ” *Abinda idonka ya nuna maka*, ita d’in ita ce, bayan haka bansan komai ba.”

Tsaki Khatar ya ja tare da juyawa ya kalli Zafreen yace “Zo muje gimbiya.”

Da sauri suka fice a ofishin canal na kallonsu, saida suka fita har da bayinsu shi ma ya ja tsakin yace “Aikin banza, naga ma kai ka fini firgita da lamarinta tunda suman tsaye ka yi, can kuje ku k’arata da matsalarku da ita ni ku daina sakani, tunaninta kad’ai hawan jini yake tayar min.”

*Ayam* kam na fitowa ta kawo daf da motocin da Khatar ya zo ta tsinkayi muryar Umad yace” Ke.”

Yi tayi kamar bata ji ba ta ci gaba da tafiya, sake fad’in yayi” Ke.”

Nan ma ko waiwaye bare hasa ran zata tsaya, saida ya bushi iska ya daddage yayi ta maza yace” Ayam.”

Cak ta tsaya tare da juyowa tana murmushi tace” Na’am yallab’ai.”

Gyara tsayuwarta tayi saida ya k’araso yana d’an cije leb’e da mamakin kenan ta ji banza ne ta masa? Tsareta yayi da ido kamar mai son gano wani abu a fuskarta sannan yace” Me yasa kika wa babban mutum fitsara? Dama rashin kunyarki ta kai haka? Sannan me yasa kika mareta?”

Ajiyar zuciya ta sauke irin ka dameni d’in nan sannan ita ma ta zuba idonta a na shi a yaren Italy tace”…

 

*Saura k’iris a rufe free page, hanzarta ki biya na ki, farashin mai sauk’i ne.*

 

*Alhamdulillah*

The post Lu’u Lu’u 7 first appeared on 2gNovels.com.ng.

[ad_2]

Previous page 1 2 3 4

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button