MAKAUNIYAR KADDARA COMPLETE HAUSA NOVEL

MAKAUNIYAR KADDARA 67

Zinneerah ɗin.

    Kowa yasha mamaki, amma sanin wacece ita a wannan fanin yasa duk suka amince. Itace da kanta ta fara harhaɗama Zinneerah magungunan gargajiya ta fara 

amfani dasu, tace insha ALLAH komai zai daidaita.

      Kwananta takwas a asibitin aka sallameta, Alhmdllhi zuwa yau kuma yara sunsha nono kuma babu wani matsala data biyo baya. Hakan ya saka kowa farin 

ciki dajin daɗi. AK yaga amfanin wannan sani na Mahma da yaketa ƙorafi akansa tunda gashi ta bama matarsa magani an kuma dace.

      A randa aka sallamesun ranar Mammah ta iso Nigeria, zokaga murna wajenta datai tozali da ƴan jikokinta. Su Adilah ma an iso daga Lagos suda tawagar 

Mommy. hakama Gwaggo Maryama. Inna ma da aka sallamota nan AK yace a kawo ta huta sosai kafin a maidata Danya.

     Kai tsaye gidan hajiya iya aka wuce da Zinneerah, za’ai suna acan sannan su koma gidansu su cigaba da jego kuma.

     Yara sunci sunayen Hajiya Iya da Baffah. *_Ameenatu & Kabeer_* za’ake kiransu (Amaan & Anam). AK ya zata Mammah zatai fushi, sai yaji batace komaiba. 

Yaji daɗin hakan, dan koba komai ya yarda ta dawo hankalinta yanzu kam. 

      (An zinni sai muce ALLAH ya raya keda yayanmu angon jego).

        AK dai bason bidi’a yakeba. Dan haka aka shirya ƙwarya-ƙwaryar liyafa anan harabar gidan akaci akasha kowa ya godema ALLAH. Ƴan Danya, ƴan ɗanmusa 

ƴan bauchi sun cika gida dam domin taya murna. Hakama mai jego da jarirai sunsha ƙyau harsun gaji masha ALLAH.

    Kowa ka gani sai son barka. Amare ma da yawansu suna maƙale da cikkuna kanana sai fatan suma ALLAH ya saukesu lafiya.

        Kwana biyu da suna AK ya takura dole su Zinneerah suka tattaro suka dawo gidansu, aranar kuma ƴan danya da ƴan ɗanmusa suka koma. Suma ƴan bauchi 

washe gari suka kama gabansu sai kuna wata ta taso.

      Zinneerah tayi farin cikin kasancewar gidan cike da jama’a. Dan kuwa Ga mahma ga Mammah da suka koma sashen Farah suka zauna. Ga kuma Mama Ai, ga Yaya 

Gajeje da Inna. karima ma maƙalewa tai taƙi bin ƴan suna. Sai Tinene da Atine ne suka koma da amaryar baba.

      Ganin al’amura komai ya daidaita jikinta yayi sauƙi kamar ba yankata akaiba Alhmdllh yasata ƙudirin tunkarar AK da batun dawowar Farah gida. Dan itako 

tama fi son ta dawo hakanan tunda dai tasan zuwa yanzu ta horu. Dan su Meenal suna bata labari da sukaje da Granny kwanaki duba Farah ɗin abin gwanin ban 

tausayi. Duk sun fita hayyacinsu ita da Zakiyyan dan horo mai tsanani maimartaba yasa aketa musu batare da sanin kowa ba. Idan ka gansu bazaka taɓa ɗauka su 

din bane ƴan gayu ƴan ƙwalisa masuji da naira a bankuna.

          Suna zaune a falonta na farko ita da Yaya Gajeje da Karima, Yaya Gajeje tana shirya ƴan biyu da akaima wankan safe. Zinneerah ma tayi nata dan 

tana cikin kwalliyarta tamkar ba jego takeba. Har Karima na tsokanarta da tacigaba da kashe ɗauri baban ƴan biyu ya lallaɓo a samo gambo kafin arba’i.

        “Ya ilahi, dan ALLAH Yaya Karima barmin baki, ina ni ina wani gambo ana zaune ƙalau”.

     Dariya suka sanya mata, suna cikin dariyarne Mama A’i ta shigo riƙe da hannun Little dake kuka wai ya faɗi. Dubansu duk suka maida garesu, Karima na 

kamo hannun little ɗin da faɗin, “Yaya akaine Abdul?”.

       “Faɗuwa yayi, ya shigo da gudu yaci karo da kujera”. Mama A’i ta bama Karima amsa.

       Baki Zinneerah ta taɓe tana miƙama Yaya Gajeje pampas da za’a sakama Anam. Tace, “Maganinsa kenan, shidai a rayuwarsa yayi gudu, bansan daɗin mi 

yakeji ba sai kace wani ɗan ƙwallo”.

      Yaya gajeje ta katseta da faɗin, “Ai tsautsayi dai baya wuce ranarsa, sannu kaji Abdul ka daina gudu wannan gidan naku dake cike da kayan santsinnan, 

ni kaina babba idan ina tafiya wlhy a hankali nakeyi dan ji nake kamar zan faɗi”.

     Dariya Karima da A’i sukayi, Zinneerah taɗan murmusa da zancen Yaya Gajejen tana maida hankalinta ga little. “To gudun mi kakeyi?”.

      Baki ya tura gaba yana makalewa bayan Karima. “Daddyna yace nakiraki zaije anguwa”.

       “Naji to, kace ina zuwa”.

  Sai da little ɗin ya fita ta duba Mama A’i. “Mama an gama haɗa abinda ya rage ɗinne?”.

       “Eh an gama maman Abdul, harma na miki karanbani na shirya a tray ”.

      “Kai aiko ngd aiba karanbani bane”. Zinneerah ta faɗa tana mikewa. Fita tayi domin kai masa kayan breakfast ɗinsa.

         A falo ta samesa zaune yaci gayu cikin ɗanyar shadda ash, yana zaune a dogon kujera little a kusa dashi yana duba masa ƙafarsa da yaji ciwo. Koda 

tai sallama bai ɗagoba har ta karaso inda suke ɗauke da tray ɗin. “Barka da hutawa”.

     “Barka” ya amsa mata yana ɗan dagowa ya dubeta. Duk yanda yaso maida idonsa ga ƙafar little ɗin kuma sai ya kasa. tai ɗan murmushi da ɗauke kanta ganin 

kallon da yake mata. “A ajiye nan ko dining?”.

      Lumshe idanun yayi ya ɗan buɗe a kanta, cikin kasalar data samesa yanzu yace, “Ajiye anan kawai”.

    Saman centre table ta ɗaura tray ɗin da duban ƙafar little dake cikin hannunsa. “Shi kuma wannan miya samu ƙafar tasa?”.

    Iska AK ya ɗan furzar. “Yace faɗuwa yayi ga waje harya fashe, taimakemu da man zafi ma a ɗaki”.

       Bedroom ɗin nasa ta nufa tana faɗin, “Maganin mai gudu kenan idan yana tafiya”. 

      Murmushi kawai AK dake binta da kallo yayi, dan a kwankin nan data haihu duk ramar nan ta ciki da tayi nan ɓacewa take, sai wani irin buɗewama takeyi 

alamar lafiya ta samu. Miƙewa yay yabi bayanta yanama Little gargaɗin ya jirasa ya dawo.

      Zinneerah na ƙoƙarin fitowa sukaci karo, baya ta koma tana faɗin, “Ouch Yayanmu zaka fasamin kai”.

         “Kokuma ni zaki fasamin ba”. Ya faɗa yana matsota. Kallonsa take da mamaki, ganin dai da gaske kanta yayo tai saurin faɗin, “Yayanmu wani abu ya 

farune?”.

       “Faffaruwa ma madam” Yay maganar yana kamo hannunta da jawota jikinsa. Hancinsa ya cusa cikin wuyanta yana magana raɗa-raɗa. “Ko tausayinama baƙyaji 

kin barni da kwana da little ke kinacan kina morewarki ko?”.

     Dariya zancen nasa ya bata, amma sai batayiba tai murmushi da ƙoƙarin ƙwace kanta. “Yayanmu ai amfanin mata biyu kenan, ni ina fama da wannan fiɗan 

inani ina ɗaukarka. Kawai aunty Farah ta dawo kaga ni sai nayi arba’in”.

        Gani tai ya saketa baki ɗaya yana tsuke fusaka. Ya watsa mata harara yana jan guntun tsaki, batare da ƙara cewa komaiba ya juya ya fita a ɗakin. 

Bayansa tabi da kallo tana murmushi, a fili tace, ‘Uhm ka gama mazuranka ne dan nasan kana son kayarka’. 

       

Previous page 1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button