KWARATA 73

???? —— 71
*_Don Allah nidai ina roƙon alfarma wa mutanen da suke ɗaukar tsohon page ina suna saka mishi sabuwar number , abinda nake nufi misali sai a ɗauki page 1 a saka masa page 2 bayan ba labarin bane ba tou na roƙeki maimin haka dan darajar fiyayyen halitta S. A. W ki daina bana san haka idan Annabin ya isa dake ba danni ba._*
*_Attention , labari mara daɗi daya riskeni kusan kwana biyu da suka wuce bana san yawan ƙorafe² a jikin pages ina amma yau dole tasa ni sai nayi magana , cikakken suna na shine JAMILA MUSA , kuma ni haifaffiyar KATSINA ce iyayena da komai nawa yana katsina masoyana ku saurara kuji , yake “yar uwa me amfani da suna na kina maula to kiji tsoron Allah domin ko ba komai ƙarya haramunne inji manzan Allah S. A. W bazan ja miki Allah ya isa ba amma dai kituna zaki mutu kuma nima zan mutu dani dake duk zamu haɗu gaban Allah SW , bani bace nake waya daku cewa ku turomin kuɗi zan siya data zan yi kaza² ni JAMILA MUSA bani bace ba ƙarya ne kuma ƙarya take da suna na tana ansar kuɗaɗe a hannunku dan haka kuyi karatun tanatsu domin da kuɗin nake buƙata a hannunku bazan roƙeku ba sadai na siyar da littafin amma ba komai nasan ƙauna ne yasa yasa kuke bayarwa amma daga yanzu duk wacce tace muku itace JAMILA MUSA ƙarya takeyi 07016–78 shine farkon da kuma ƙarshen number na ngode sosai masoyana ina muku fatan alkairi…._*
Kaine Dikko ? Inna tayi maganar tana kallon idona ! Shima ni ya kalla yace ƙwarai nine Dikkon da kike magana , ai nasan kaima sunan ka Dikko bakai ba Dikkon gidan gwamna shi nake nufi , har yanzu idon Dikko a kaina yake ya ba Inna amsa cewa shine ai , kaine …..? Umm ya bata amsa , yanzu kaine ɗan iskan yaron nan daka raina mutane ? Murmushi Dikko yayi tare da cewa amma dai ai ke ban raina ki ba , wannan duk faɗar mutanen da basa so nane , na raina mutane bana ganin mutuncin kowa idan na taho bana kaucewa kaza² wannan duk labarin “yan uba ne Dikko ba haka yake ba kayane aka linke ta baibaya shi yasa ake ganin mununsu….
Kai da Allah rufe min baki ɗan iska mara mutunci na tsaneka duk duniya idan akwai wanda na tsana tou ka sani ba kowa bane kaine …… , bana sanka yau ji nake kamar in yanke kunne na saboda ɓata lokacina da nayi ina waya dakai , har yanzu murmushi yake kuma bai daina kallona ba yace itama kamar yadda kikayi haka ta ɗauki zafi , nuna kanshi yayi cewa irin bakinmu ɗaya itama Momy wai bata san An mata kema baki san Dikko anyi anko kenan to amma ai dani da An mata kowa yana san kowa ke ko kin daina so nane ? Yayi maganar yana tambaya na da kanshi……
Nima murmushi nayi masa tare da bashi ansa ina sanka kuma saina aureka ko za’ayi ruwan bala’e da ƙanƙarar masifa a cikin familynsu wannan ni bai shafeni ba , duka zagi ko habaici baya gabana ko za’a mutu a dawo idan na kafe a hanya ɗaya tou wannan hanyar duk girman katsina babu wanda ya isa yasa na juya zuwa wata , nuna shi nayi sannan na nuna kaina Dikko ina sanka kuma saina aureka cikin amincin Allah da salama duk wanda baya maraba da auren nan tabbas canja maganar nayi cewa zai so ma…
Cikin ɓacin rai Inna tace fita……. Dikko fitar min daga nan , a , a Mama cikin hayani Inna ta fara turance Dikko shima da yaren da tayi magana yayi mata nidai na zama “yar kallo dan banajin abinda suke cewa kuma bansan yadda sukayi ba Dikko ya fita cikin damuwa , kafin na sauko daga saman gado Dikko ya fita daga ɗakin da gudu na fita lokacin harya shiga motarshi ya tada , cike da fargaba na isa wurinshi nace Dikko ka tsaya dan Allah , tsayawa yayi yana kallon can gefen cikin tsananin ɓacin rai…..
Kusa da motar na tsaya na dafa hannuna a saman glass ɗin daya rage bai ida saukewa duka ba , Dikko me Inna tace maka don Allah , dakel ya kalli gabanshi ya busar da iskar bakinshi a damuwance yace ba komai Sulthanah…….. Dam׳ naji gabana ya faɗi sunan babu daɗi a bakin Dikko sai naji wani iri haka da ya kirani da Sultana tunda na haɗu da Dikko da rashin mutunci muka haɗu amma bai taɓa kamo tashar suna na ba sai yau lallai abun yaci tira karuwa ta tsira malam.
Ci gaba yayi da cewa mu ɗau haƙuri mu sanya haka ɗin jarabtace , kuma kowa akwai nashi a rubuce , babu wanda ya isa ya musulta ita ƙaddara idan ka rasa karka manta da Allah , ubangiji keda iko mu bayi “yan kallo ne ! Idan kinyi imani da Allah kuma kin yadda akwai samu akwai rashi , kuma idan har kinyi imani ubangiji yake bayarwa kuma shine yake karɓewa yadda da ƙaddara ki tuna wannan shi ake kira da imani , zumuncin mu yana nan insha Allah kije kuma ki ba Mama haƙuri idan har kinyi imani da Allah ki karɓi auren Sultan kuma ki zama mai biyayya wurin mijinki , kije Allah ubangiji ya albarkaci rayuwarki na barki lafiya , yana faɗin haka ya sulala da motarshi a hankali ya fita , bin bayanshi nayi yana fita daga gidan ya tafi da tuƙin shi mai burgeni……
Kai tsaye g r a ya nufa dan ya samu ya sauke damuwarshi , yayin da hotunan abinda ya faru tsakaninshi da An mata ya fara wuce masa ta gaban idonshi , a ranshi kuwa kukan Sultana yaji a ranar da yayi mata babbar kajin ƙauri , tana roƙarshi cewa { kaji tsoron Allah karka ɓatamin rayuwa ka rufamin asiri dan girman Allah , } goge hawayen idonshi yayi tare dayin magana a bayyane amma dake banaji shine banyi haƙuri ba saida nayi kaicon ka Dikko me kaji ? Da nayi haƙuri na barta duk haka bai faru ba nima kaina da ina nan zamana lafiya haƙuri yana da matuƙar kyau a rayuwa kuma yana da wahala babu wanda zaiyi haƙuri yayi nadamar yinshi , amma idan kaƙi haƙuri kayi abinda zuciyarka tace tabbas sai kayi nadama da zaran ka gama aikatawa , wani irin wawan burki ya taka tare da juya kan sitiyari ya nufi inda su Bello suke yau saiya kashe Bello daya kawo mishi An mata wurinshi ! Saiya faɗa masa dalilin daya sa saishi aka zaɓa ya ɓatawa An mata rayuwa ƙalu bale gareka Bello…..
Inna kiyi haƙuri don Allah zan auri Sultan , ko kiyi haƙuri ko kar kiyi babu gudu babu ja da baya aurenki da Sultan babu fashi wallahi , to Inna in Allah ya yadda , amma dan Allah Inna me kikace ma Dikko ? Ai na ɗauka da kika bishi ya faɗa miki na tsani Dikko sakarar banza ballagaza dake dama Sultan yacemin ko a asibiti tare kuke kwana idan har kika bari Sultan yace ya fasa aurenki ƙaryarki ta ƙare asirinki ya tonu.
Haka ya kasance dani ɗan uwana ya fito yayi hidima da rayuwata munyi soyayya mai tsabta auren zuminci shine al’adar familynmu amma tunda ake haɗa aure ba’a taɓa samun maso san junansu ba sai mu domin mu ba haɗamu akayi ba mune muka haɗa kanmu , biki ko suna komai da kika sani duk inda zanje muna tare , munayi ma juna soyayyar da ta zama abin sha’awa ga duk wani wanda ke ahalinmu dan wannan soyayyar ta kafa tarihi mai girma , amma lokaci ɗaya Binna ya shigo rayuwata yayi min karatun yaudara zama ɗaya na ɗauka kuma na kifa kaina ƙasa nace na fasa auren Umar , duka zagi anyi amma na kafe sai Aliyu….
Abun ya zama abun tashin hankali da jimami a ahalinmu , yayin da wani ɓangaren ake kallon abun kamar anyi wani babban rashi , duk wani ɗan uwana ko “yar uwata suka juyamin baya wannan bai dameni ba tunda dai Aliyu yana tare dani , Umar yayi kuka kamar ranshi zai fita wasu kuma suna cewa ko na fasa a aura masani dole , amma nace idan har aka ɗauramin aure dashi wallahi saina daɓa mishi wuƙa ya mutu , kaf ahalina suka juyamin baya bayan an ɗaura min aure da Aliyu kinga dai yadda rayuwar gidan Babanki take kuma nayi haƙuri duk nayi ta tsotse dafin wahalar gidanshi amma kinga daga baya saiya sakeni waishi baya zuwa bikon mace , dakel aka anshe ni a gidan nan Umar kuma baiyi zuciya ba ya dawo yayi aure amma ba auren zuminci ba.
Mazan basu da tabbas ko kace kana sansu daga ƙarshe sai sunyi maka tultular ruwan tsohon tulu suyi maka gori abu kaɗan kayi musu sai suce ka gagari iyayenka ka zaɓesu ka bar iyayenka , wanda ya gagari iyayenshi abun mamaki ne ya gagari mijinshi ? Ko a kuskure kayi abu sai sun goranta maka auno girma da rashin mutuncin Dikko Sultana , bani na faɗa ba duk garin nan kowa yasan halin Dikko ya gwane wurin rashin mutunci baya ganin ƙima ko darajar kowa koya aureki bazai riƙeki da amana ba , gashi yanzu ya faɗa cewa mahaifiyarshi bata sanki nima bana sansa , haka zakije ki fuskanci wulaƙanci da hantara a cikin zuri’arsu , kuma nayi imani wata rana saiya goranta miki yace miki karuwa kuma zai miki gori kinbar uwa kin zaɓi namiji , tazara mai nisa tako ina Dikko yayi miki asalinki da nashi ba iri ɗaya ba , tun ba’asan meye suna ba tunin duniya tasansu , mutane masu arziƙi da cikar asali sunyi kuɗi na tashin hankalin da kwalwarki bata ɗauka , sun nemi kuɗi kuma sun samu sun tarasu tun mutane na bacci , Dikko yafi ƙarfinki kuma yayi miki zarrar da baki kamoshi ki shafawa kanki ruwa ayi miki aski ,
Ke kina wasa da lamarin Dikko ko ? Hmmm dan girman Allah wata rana kije inda yake zama ki kalli mata masu siga da nagarta kamar ba mutane ba tsabar kyawunsu , Sultana har Dikko yana kallon dakakkin mata “yan gayun bala’e masu ilimi wanda suka goge masu aji zai saurareki ? Dan Allah kije wata rana kiga yadda mata kebinshi , ko yace zai aureki ƙarya yakeyi yaudararki kawai yakeyi dan nayi imani Dikko baya aurenki yafi ƙarfinki wallahi , kiyi haƙuri kiyi ma kanki karatun ta natsu ke ba ajinsa bace ƙarya yake ba sanki yake ba kaiki zaiyi kawai ya baroki , tunda dai abinda yake nema ya samu kuma tunda ya more kiyi haƙuri ki auri dai² ke shine zaman lafiyarki…..
Inna wallahi Dikko yana so na , ke yarinya ce Sultana baki san Dikko ba baki da labarin halinshi ne ganinshi kikeyi filinshi kika sani baki san ɓoyenshi ba , duk yadda za’a faɗa miki iskanci Dikko ya wuce inda bakya tunani , hausawa na cewa idan ruwanka baya iskarka wanka sai kayi alwallah ka tashi…..
Amma Inna Dikko baya neman mata kuma na zauna gidanshi har na gama zamana banga wata mace tazo ba , murmushi Inna tayi cewa ai kinji yarintar in banda abinki tunda kina nan taya zai bar wata macen tazo ? Ko an faɗa miki gidan da kika zauna nan ne kaɗai gidanshi ? Ai wayau sukeyi saboda siyasa basa neman mata a gida saidai su haura sauran jahohi su ƙwanƙwaɗi iskancinsu su dawo , shiko Dikko karuwanshi duk ba “yan nan bane ba zuwa sukeyi daga wasu ƙasashe kuma yana gama biyan buƙatarshi zai basu kuɗi su juya abunsu ba tare da wani yaji ko ya gani ba , kinga waye ya ganshi da mace anan bare yace shima manemin mata ne ? hmmm ke yarinya na kiyayeki da Dikko domin haɗarinshi yana girma.
Nidai haƙuri nayi ta bawa Inna kuma na haƙura har a zuciyata na yadda da auren Sultan kuma na bawa Inna haƙuri sosai ta kuma gode tare da sanyamin albarka sannan tabar ɗakina , tana fita na rufe ƙofa na kwanta ni bansan me yasa ba idan har zanga Dikko ko naji muryarshi sai in nemi hankalina da tunanina duk na rasa ina ya tafi amma insha Allah koya kirani bana sake ɗauka na haƙura dashi Allah ya bani dangana…..
Wata irin shaƙara Dikko yayi ma Bello cikin sanyinshi yace me nayi maka don Allah ? Me yasa ka haɗani da yarinyar da kukeyi rikicinku bayan ni bai shafeni ba ? Shiru Bello yayi baice komai ba , Dikko yace faɗamin ina saurarenka kadai lura ina cikin fushi ko ? Jinjina kanshi yayi cewa tou faɗamin kafin in ɓare maka biyu in kashe ka kuma na kashe banza sai ka zaɓa ga mutu ga kuma rayuwa……
Da sauri Bello ya dafa hannun Dikko , sakinshi yayi tare da cewa ina saurarenka , cikin kuka Bello ya faɗawa Dikko saboda yayi fyaɗe wa wata yarinya da suke gidan shine shima Binna ya rama akan matarshi , wannan dalili yasa ya kudiri shima saiya gurɓatawa Sultana rayuwa kasancewarta bugun zuciyar Binna , soyayyar da Binna yake mata yasa duk inda zata tafi yana tare da ita saboda baya so ta shiga cikin wata damuwa ko halaka , Binna baida tsoro kuma bashi da mutunci akan duk wanda ya taɓo masa Uwar masu gida saboda yana jinta kamar wata rayuwarshi , ni kuma ina nan haƙe dashi ina neman sa’a yadda zanyi na taɓo wannan rayuwarshi tashi dan huce raɗaɗin ciwon abinda yayi min , ƙwatsam sai Binna yazo min da labari cewa yau Uwar masu gida taso ta jawo masa fitina da kanta ta zagi ɗan gwamna yaro mara mutunci daya raina mutane dakel aka bashi haƙuri ya haƙura saina lura Binna yanayin maganarshi ya nuna yanajin tsoronka bayan shi kuma bayajin tsoro kowa.
Ganin haka sai nayi amfani da wasu mutane daya ci bashinsu nace musu Binna yace bazai basu kuɗin nan ba yace ya cinyesu idan suna da wani isashshe yazo ya karɓar musu a hannunshi , nine na tunzurasu sukayi ƙararshi aka kamashi kuma ni dakaina na bada kuɗi wa “yan sanda sukayi mishi lullusar fitar hayyaci , kuma nine naje na biya kuɗi nayi belin shi , saina bashi shawara za’ayi caca yazo yayi ya shiga tunda yana da sa’ar caca bai taɓa faɗuwa a caca ba idan yaci kuɗin saiya biya bashin , nasan baida kuɗin da zai saka kafin alƙalamin caca shine nace masa kawai ya saka Sultana , da farko bai yadda ba duk da saida nayi masa asiri kuma bokana ya tabbatarmin da zai sakata a cacar ya kuma bani maganin da zan zuba mishi a abun sha wanda zaisa yayi wasi² , haka kuwa akayi bayan dai Binna ya yadda ya saka Sultana a wurin caca na zuba mishi maganin wanda yasa yayi wasi² ya faɗi a wasa.
Ba wani abu kayi min ba na kawo ta wurinka ba saboda na lura Binna yanajin tsoronka kuma na tabbata ko tsafi yake kai kafi ƙarfinshi saboda kai ka zama dodon duniya kuma kai jan gwarzon maza ne dan kowa yasan ka gaji nagarta , duk wani ɗan ƙaramin tsafin shi bazai kamaka ba dan kai nari ne ko an jefe ka haka nan jifar zataje ta dawo kuma idan taƙamarshi yayi shari’a dakai kune gwamnati bai isa yaja dakai ,
Gwamnatin ubanka Dikko ya faɗa tare dakai mishi wani irin kyakkyawan halbi a baki saida yaci uban Bello da kyau ya kuma sake ɓare mishi haƙora sannan ya kashe Dady da mari yayi haukanshi sosai babu wanda ya bashi haƙuri dan babu mai riƙeshi sunci ubansu kuma suma yau sun ƙara saki da lamarin Dikko saida ya tabbatar sun tashi aiki ya nufi gidanshi cikin ɓacin rai !
Cikin farin ciki kowa ya wayi gari duk wanda ka gani a gidanan yau yanayin farin ciki , kowa sai hidimar gabanshi yakeyi yayin da ni kuma nasha wanka na tsuke cikin wani ƙaton leshi kalar launi mai kyau , nima dai duk da banajin daɗi hakan bai hanani nuna farin ciki ba amma na ciki yana ciki , Inna ma tana cikin farin ciki tana ta hidima da mutanen arziƙinta kai Inna gaskiya wayayyace “yar gayu kisan farko ga kyau ga hutu wallahi baka gajiya da kallonta.
Misalin ƙarfe 2:00pm aka ɗaura auren da taron dubun mutane suka halatta , ina ɗaki kwance ina ta kuka na rasa abinda yakemin daɗi Inna ta shigo ɗakin cikin tsananin ɓacin rai tasha kuka har ta gode Allah , kayana ta fara tattarawa tana kuka idan ta zuba a akwati sai ƙawayenta su ɗauka sukai waje cikin mota su dawo , duk abinda ya shafeni saida Inna ta tattarashi kaf ta ware lefen da aka kawo jiya ta ajiyeshi a gefe wayata ta ɗauka tare da jawo hannuna tana fizgata cikin ɓacin rai haka muka keto cikin taron mutane kowa yana kallonmu , Kaka ta biyo Inna tana cewa Fatima wai kedai ban isa in faɗa miki ba ? Bata bata ansa ba har yanzu kuka Inna keyi , haka Kaka ta biyomu har harabar gidan amma sam Inna bata saurara mata ba ta buɗe bayan mota ta jefani ta kulle da kanta taja motar kamar zatabi ta kan Kawu ta wuce ta fita daga gidan , sauran mutanen da suka zo mata biki suka biyo bayanta.
Har muka zo gidan Inna dake barhim estate Inna kuka takeyi , ƙaton gida ne da akayi mishi ginin zamani gidan “yan gayu an ƙawata shi da filawowi wanda suka ƙara martaba darajar gidan , tanayin parking ta fita nima fita nayi daga motar nabi bayanta ina kuka palo ta zauna tana goge hawayen idonta da tissue a haka taron ƙawayenta suka shigo suna ta bata haƙuri dukansu da turanci suke magana ni dai bansan abinda suke cewa ba saidai inaji lokaci² tana kamo sunan Dikko , haƙuri dai suke ta bata har wanda nake tunanin shine mijinta yazo kiranta yayi suka shiga ciki ƙawayenta suka ci gaba da tattaunawa akan abinda Yayar Inna tayi bata kyauta ba ,
Tayi ƙatuwar cin amana sukaci gaba da maganarsu da yaren da nake fahimta su kuma sun kasa gane saboda nine Inna take magana dasu da turanci tunda tasan ban iya ba , wai ashe ita Yayar Inna jiya itace ta faɗawa Sultan wai ni ina da cutar ƙanjamau lokacin da akayi min fyaɗe aka sakamin cutar shi yasa “yan gidanmu sukayi ta ƙyanƙyanmi na ko kofi na taɓa basa amfani dashi wannan dalilin yasa na shiga bariki kuma abinda yasa na amince da aurenshi wai ni nake faɗa zan yadda na aureshi ne dan na saka mishi cuta , kuma ni karuwar Dikko ce kuma kona aureshi wai ni na faɗa mata bazan daina bin maza ba , da Sultan ya faɗawa Kawu , Kawu yace ƙarya ne ka auri yarinyar nan zaka zauna lafiya amma sam mahaifiyar Sultan tace wallahi baya aurena , Kawu yayi faɗa cewa ya taro mutane daga wurare da dama zasu zo ɗaurin auren ɗansa saiya musu waya yace an fasa saboda wulaƙanci ? Shine Mami tace sai a ɗaura auren da ɗiyar ita Yayar Inna , yanzu da ita aka ɗaura auren duk Inna bata san wainar da ake toyawa ba saida aka ɗaura yau akayi ta mata habaici wai ta lulluɓo “yarta kura da fatar akuya taso ni na auri Sultan na goge masa cuta , sukayi ta faɗin maganganu marasa daɗi akaina shine Inna taji haushi kuma in banda munafirci jiya sune suka tunzurata ta nemo Dikko tayi mishi wulaƙanci , ashe su sunsan Dikkon shine Dikko ita kuma Inna bata sani ba tunda dai kawai shi wannan Dikkon ta ɗaukeshi matsayin ɗa yana girmamata ta gayyatoshi ne ya tayata tayi faɗawa wa Sultana sai kuma ya kira Dikkon gidan gwamna yayi masa concrete worning ya fita harkar Sultana , shine tayi rashin mutunci wa Dikko data gane shiɗin dai ne Dikkon da take nema tayi ma Dikko wulaƙanci a daren jiya sosai wanda kare baya ci ,
Ita ba rashin Dikko bazai auri Sultana ba dama tasan babu maganar Dikko ya auri Sultana gaskiya saboda ba irinshi bace ita , tanayin baƙin cikin zumincin data dagula tsakaninta dashi , sai kuma kukan abinda “yar uwarta ciki ɗaya tayi mata yanzu da bata raye haka rayuwar Sultana zatayi ta wurgegeniya babu mai taimakonta , ita kanta ta sani wato ta bada “yarta ita kuma Sultana ko oho ,…….
Sai dare kowa ya tafi daga gidan shima mijin Inna tafiya yayi ba’anan zai kwana ba , Inna tana cikin damuwa sosai ɗakinta ta shige ta kulle , tou banda abin Inna ita kuma Kaka meya shafeta a cikin wannan matsalar ne ? Wata zuciyar tace baki sani ba kila itama tace wani abu , tou amma me yasa inna ta haɗa hada Kawu ? Oho zuciya tace sudai suka sani domin sunfi kusa……
Duk gargaɗin da Inna tayimin akan Dikko saida na kunna wayata na kirashi , kamar jira yake tana shiga ya ɗauka ya gaggaɓe da wata irin dariya yace amaryar Dikko ai nasan wallahi dudduniya babu maike saini , yaci gaba da dariya cikin dariya yake cewa abinda yasa bana aurenka baƙin rai baka dariya ba fara’a doke² gaka mahaukaci sai aljannu kamar iccen tsamiya hahahaha ashe rabon mahaukaci ce lallai zamuga wasan kura An mata matar Dikko , ke kafiya ni kuma aljannu kamar iccen tsamiya , hmmm inzo Barhim ɗin zaki fito wurina…………..?
Dan Allah kuyi haƙuri wallahi ina fama da matsalar rashin caji ne kuyi haƙuri da wannan !
06/10/2019 ????????
*JAMILA MUSA…..* ????????