TUN KAFIN AURE 1-END

TUN KAFIN AURE Page 11 to 20

*******************

Dai dai yake kallon mutane kowa da budurwarsa ana ta sha’ani. Shegiya Tilly da nasan haka take ai da tun wuri na nemi me rako ni nan. Kai da wa kake magana Juni? Shafa kansa yayi zancen zuci ne ya fito fili birthday boy…Imi dan wani gwamna ne abokin Junaid ne tun suna secondary duk watsewarsu tare sukeyi. Ina babe din da na ganku tare ne jiya? Tilly barauniya? Ai na bata takardar sallama dazu….sata fa tayi min don rainin hankali. Imi da buduwarsa suka fashe da dariya ai abokina ka fiye kwashe kwashe ne. Ya rungumo yarinyarsa ya Simy akwai wata a kasa ne kada yayi kwanan kadaici yau. Kai kyale ni kawai. Maybe na tafi portharcout gobe. Dont worry I will pay bana son ganinka so quite. Wayarta ta dauko ta mika masa ga hotunan wasu nan duk kawayena ne idan ka zaba kayi min magana. Bakin ruwan suka koma ana ta wasa da raye raye shi kuma yana kallon ‘yan mata kala kala a wayar. Tsaki yayi zai kira Simy ta karbi wayarta sai kawai yaci karo da hoton da ya daga masa hankali. Zuciyarsa ce take bugu da sauri da sauri…he wants this girl at all cost abinda kawai yake fada a ransa kenan.

Batul Mamman

TUN KAFIN AURE???? 10

Jikinsa har tsuma yake bai taba ganin macen da ta sace masa zuciya ba kamar wannan. Fatansa daya wannan saurayin daya rungumeta ba mijinta bane. Tura hotunan yariyar yayi daya gani a wayar ya tashi da sauri ya je wurin da Imi da Simy suke ta rawa yana mata liki da dubu daya. Janyo hannunta yayi suka fito daga wurin rawar Imi ya jawo wata suka cigaba. A irin wannan rayuwar ana tafka kazanta da tsabar rashin kishi. Muna mantawa akwai ranar da zamuyi accounting for every second da muka rayu a duniya.

Rawar ta cigaba da yi a gabansa ganin hakan ya sake janta suka kara nisa da mutane. Yarinyar nan nake son duk wani information a kanta. Ta dan nutsu ta kara kallon hoton wai wannan kake nufi? Eh mana are you blind? No…sai tayi dariya sorry. Gaskiya Juni bansan….katse mata magana yayi kada kice baki santa ba. Kudi ya dumbuzo daga aljihunsa ya damka mata a hannu. Ki nemo min duk abinda ya dace …ya sake kallon hoton…my God she is so pretty. Kallonsa tayi Juni wannan fa pre-wedding pictures ne. Maybe ma anyi auren don na kusa wata da ganinsu. A wani group aka saka na ma manta wadda tayi sending. Ai sai ki sake sending ki tambaya. Look Simy bani account number dinki. Washe baki tayi yanzu kayi magana. Zan nemo ta ko tana gidan miji ne sai tazo ta kashe maka kishi…kanne masa ido tayi ta tafi. Simy ‘yar shekaru goma sha tara karamar yarinya ce da iyayenta suka kyaleta take irin rayuwar da take so saboda yanayin aikinsu. Tana abinda taga dama babu me tsawatar mata a cewar su kuruciya ce ke damunta. Wai kuma yar musulmi kenan babu ko tsoron mutuwa.

******************

Kallon ‘yan uwanta take ana ta hayaniya. Kanta har wani sarawa yake don ciwo. Wai nan lefenta aka kawo shine har yanzu mutane basu gama tafiya ba. Dakinsu ta nufa kai tsaye wata kakarta tace ai tunda kika dawo bamu watse ba ki tsaya ki kalli abin arziki. Ai ni kam wannan miji yayi ina ma ina da sauran kuruciya. Dariya duk aka sa Hafsi ko sai hawaye. Auren da zaayi ba dadin rai. Abinda komai Baban Saif ne yayi don yace shi ba karamin mutum bane aure ya zama dole. Shi kuma Saif kamar bai taba cewa yana sonta ba alaqar tasu yanzu ba yabo ba fallasa. Da gaske yayi nadamar abinda ya aikata sai dai kunyar iyalin Baffa yasa har ransa baya son ayi auren. Allah Yaso shaidan baici galaba a kansu ba da da wane ido zai tsaya a gaban mahaliccinsa? Ko matasa nawa ne ke tuna irin wannan a lokacin da suke matse ‘ya’yan mutane suna aikata haramun?

Ita kanta Hafsi tana tsoron rayuwar da zasuyi. Da wane ido zasu rinka kallon juna. Ba don zuwan Baffa ba da kila shikenan. Rayuwa kenan wasu na nadama wasu kuwa zuciya ta gama bushewa a aikin sabo. Tir da wannan rayuwa ta shaye shaye da zinace zinace. Ya Allah Ka kara shiryamu Ka bamu wadatar zuci.

Batul Mamman????

TUN KAFIN AURE???? 11

Da gaske Simy ta shiga neman yarinyar hoto don Juni dubu dari da hamsin ya saka mata a account yace cikon sai bukata ya biya. Hoton ta fara turawa groups uku da take tsammanin daga nan aka turo don ta manta inda ya fito. Sai bayan kwana hudu ya kebbi tayi magana tace ai saurayin yayan kawarta ne a kano suke. Jin haka Simy tayi saurin cewa ai yarinyar da makotansu ne sun dade basu hadu ba tana neman address dinta ne. Nan dai ba wani dogon bincike yar kebbi ta turo da number din Zainab. Mata mu rage tallata sirrinmu a social media don Allah.

Kamar akan kaya yake a lagos din sai dai kuma dole ya tsaya don Imi yana nan Simy ba tafiya zata yi ba. Yana cikin restaurant din hotel din da yayi masauki tayi masa waya ta shigo. Nan yayi mata kwatance suka hadu. Sai da ta cika cikinta da abinci wanda ya kasa ci don dokin jin abinda zata fada masa. ta sanar dashi yadda suka yi da yar kebbi cikin tsananin farinciki ya kankameta sannan ta bashi number din Zainab. Tana ta dariya Juni lallai yarinyar nan ta tafi da imaninka idan akwai saura. Ke me kike nufi? Ya daure fuska…ni duk iskanci na bana hadawa da izgilanci ga addini fa. Ga wayarki ya mika mata..zan ciko miki kudinki anjima. It was nice doing business with you Juni. The pleasure was all mine ya bata amsa.

Dakinsa ya koma ya hada kayansa. Bayan ya gama ya kira number din Zainab. Kamar gaske sallama ya fara yi mata ta amsa duk da taji bakuwar murya.

Dan gyaran murya yayi( Zainab ce ko)

(Eh, wa ke magana)

Shiru yayi yana tunanin karyar da zaiyi ( ina yayanki ango to be?)

( ya Saif ya fita)ta bashi amsa.

( suna ta shirye shiryen biki ko)

Mamaki ta fara yi dai amma tayi shiru (eh amma fa still bangane ka ba)

( ina printing din cards na biki ne a nan kusa da unguwarku shine nake son nuna masa sample don kiran kasuwa).

Sai a lokacin ta dan saki rai tayi masa kwatancen gisansu kamar yadda ya bukata ba tare da ta kawo komai a ranta ba. Yarinyar kamar mara wayo ya fada shi kadai, ba wani bincike ta turo da address.

Scrolling waya yayi ya nemi sunan Oldman ya kira. Senator Rufai yayi mamakin ganin sunan Junaid yaron da number dinsa da suke da ita gaba daya basa samu sama da sati biyu. Hakuri Junaid ya bashi tare da sanar dashi zai tafi kano wurin Hajiyan Dangi itama ya bata hakuri. Senator Rufai murna yayi sosai. Yana matukar son dansa lalacewar yaron kawai ke damunsa.

******************

Kano ta dabo tumbin giwa yau tayi babban bako. Junaid Rufai Bukar ne yake tafiya cikin nutsuwa don yau manyan kaya ya saka tare da aski wanda gashin na zuba zuciyarsa na kuna. Hatta faratansa yaje wani salon a lagos ‘yan mata sun gyare shi. Shadda yasa light blue anyi mata dinki mai kyau kansa harda hula. Idan ka ganshi sai kasa shi cikin mazan kwarai sai dai abin ba a fuska yake ba.

Yana tafiya maaikatan airport na binsa a baya ganin sunansa yan maula sun rude. Motar da babansa ya turo ce ta karaso gabansa aka saka masa kayansa a cikin booth. Kudin ya basu masu yawa tunda bai san zafin nema ba. Kowa sai murna…Tilly dake bayansa wadda baisan ma jirgi daya suka biyo ba tayi murmushi tasan ba a banza yayi wannan shigar yazo kano ba. Sai ta rama wulakancin da yayi mata a lagos. Wayar Rosie ta nema ta sanar da ita ta shigo gari.

Previous page 1 2 3 4 5Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button