TUN KAFIN AURE 1-END

TUN KAFIN AURE Page 11 to 20

******************

 Ummati ana ta rawar kai biki ya gama matsowa da kyar aka barsu zuwa salon don ko gyaran jiki Hafsi bata yi ba. Wannan kuma duk yana cikin punishment din da aka tanadar musu a gida saboda laifin da sukayi don a cewar Maman Ummati itama haka zaayi mata tunda bakinsu daya.

Sai da Saif yayi jan ido sosai sannan kanwarsa Zainab ta fada masa gaskiya ita ce garin binciken waya taga wadannan hotunan a wayarsa ta tura wayarta, daga nan kuma ta tura wa kawayenta. Da belt ya zane ta tana ihu tana bashi hakuri. Ko da mamansu taji dalilin dukan Allah Ya kara tace musu duk su biyun. Ke banda gulma me ya kaiki bincika masa waya….bayan zainab ta koma daki da kuka Maman tace gobe ma ka sake daukan yar mutane kuje yin hoton rashin kunya….istigfar ya rinka yi a zuci. Allah Yasa daga wannan bazasu fuskanci azabar Allah ba. Don kam shi da Hafsi sunyi nadama sosai.

Batul Mamm

TUN KAFIN AURE???? 14

Duk abinda yayi niyyar yiwa Pretty kamar yadda ya saka mata suna maganganun da Hajiyan Dangi tayi masa yasa duk jikinsa yayi sanyi. Washegari bai bari ya makara sallar asuba ba domin kafin lokaci ma yayi setting alarm. Suna dawowa ya shiga dakin Hajiyan Dangi. Har ka manta yadda ake sallama ne? Ba shiri ya fita yayi sallamar ya jira tayi masa izini ya shigo. A kasa ya zauna cike da ladabi tace yau dannan nawa akwai magana a bakinka. Fadi inji Allah Yasa alkhairi ne. Shafa kai yayi alkhairi ne Hajiya. To ina jinka. Wai yau shine da jin kunya abin ya bashi mamaki… dama yarinya na gani ina son aura kuma idan da hali da wuri nake son auren. Allah mai girma da daukaka ta daga hannu sama ta yabi Allah SWT sannan ta kalle shi. A ina take kuma ya sunanta? Nan fa daya yace a ransa, sai kuma dabara ta fado masa. Nasan gidansu dai amma banyi mata magana ba domin mafi son ki fara nema min izini. A’a wai kuwa Junaidun da ta sani ne wannan? Yau komai a hankalce yake yi. Allah Yasa bata yi masa zancen Sayyada ba itama yarinyar bata sani ba da yazo ya bata kunya. Kwantar da hankalinka bari na fadawa Baba sai musan abinyi zuwa karshen sati. Sanin cewa nan da kwana uku zaa daura mata aure Junaid ya fittike mata shi lallai yau yake son taje. To naji bari dai na fada masa tunda da kanka ka zo da maganar. Tana fita yayi ajiyar zuciya yarinyar da har yanzu baiga zahirinta ba yake tunanin aura….sai dai kuma irin yadda yake jinta a ransa yasan da gaske yake burin rayuwa da ita, baya jin zai taba iya yarda wani ya shiga tsakaninsu.

Sai bayan laasar Hajiyan Dangi ta shirya tare da wata yar uwarsu Gwaggo Mairo suka nufi unguwar sabontiti inda Junaid yayi musu kwatance a matsayin gidansu Pretty. Karba ta mutumci da karramawa Mama tayi musu bayan sun gama gaisawa ne Hajiyan Dangi ta gabatar da kanta tare da fadin dalilin zuwansu. Mama tace kuma nan gidan yaron ya fada muku? Nan ne domin ya kwatanta min gidan ta waje sosai Hajiya ta bada amsa. To Hajiya ni dai banda yaran nan biyu da suka gaisheku bani da wata ‘yar sai Hafsa wadda asabar dinnan zaa daura mata aure. Babbar kuwa shekararta uku ma da yin aure. Shiru Hajiyan Dangi tayi sai Gwaggo mairo ce take ta basu hakuri tace nasan yaronnan kam ba kananan yake nufi ba zamu sanar dashi yayi hakuri. Hajiyan Dangi ta fiddo kudi a jakarta tace gashi a bawa amarya. Allah Ya sanya alkhairi. Mama taki karba itama hakurin ta basu. Hajiya sai ta ajiye kudin a kan tebur. Suna kofar fita Hafsi ta dawo daga salon duk a gajiye. Har kasa ta durkusa ta gaishesu. Ko baa fada ba Hajiya tasan wannan ce Hafsar da danta ya gano. Lallai ya rude don yarinyar tana da kyau. A sabule suka fito don ba haka aka so ba. A tunaninta indai yayi aure wasu daga cikin ayyukan barnar da yake aikatawa zasu ragu ko ma ya bari gaba daya.

Tun a mota ta kira shi domin taga missed calls dinsa da yawa sai dai bai dauka ba. Suna isa gida Sayyada ta sanar da ita ai ya tafi masallaci ne. Dadi ne ya cika mata zuciya sannan ta shige daki. Cike da doki ya shiga dakin yana ta washe baki. Har zuciyarta take tausayinsa… junaidu yarinyar nan ashe ranar asabar za’a daura mata aure. Kayi hakuri ka nemi wata. Mikewa yayi hakuri fa kika ce Hajiya. To ma baki basu kudi bane? Ai wallahi da sunga kudi magana zata chanja. Murmushi tayi zauna Junaidu. Ina so ka sani ba fada ta bace Annabi SAW yace babu kyau wani ya shiga cikin cinikin wani ma balle harkar neman aure. Ai ba’a hada nema akan nema. Abu daya zaisa ka iya nemanta sai dai indan wancan yace ya fasa. Wani irin bacin rai yaji a ransa idanunsa sun kada sunyi ja. Fita yayi fuuu ya buga mata kofar daki har sai da ya tsorata ta. Allah Ka shirya mana ta fada a fili.

Jan mota yake a guje kamar zai tashi sama. Baya ganin gabansa ma da kyau. Club ya shiga ya tayar da kura kafin ya tsayar da motar. Idanu duk a kansa ya shiga. Waiter na shirin zuba masa giya ya sunkuce kwalbar yana kafa kai. Sai da ya bugu sosai ya jawo hannun wata yarinya suka fita tare yana tangadi. A waje ya dauko wayarsa ya bata yana lumshe idanu kira min oldman. Waye kuma oldman? Ki dduba za zaki gani a wayar. Ringing biyu ya dauka sai yayi mamakin jin muryar mace ta sanar dashi wurin da dan nasa yake ya daga masa hankali. Yana ajiye wayar ya kira Hajiyan Dangi ya fada mata. Nan tayi masa bayanin abinda ya faru sannan ta sanar da maigidanta inda Junaid yake. A can abuja kuwa Mommy Senator Rufai ya tasa yace mata gobe zamu kano.

Batul Mamman

TUN KAFIN AURE???? 15

Hajiya da maigidanta sun rasa yadda zaayi a dauko Junaid saboda Baba baya iya tuka mota idan dare yayi. Suna ta shawarwari ne suka ji karar motar sa. Da sauri suka fito motar duk ya buge ta a hanya har fitila daya ta lotse. Haka suka kama shi yana ta tangadi sosai suka shiga dashi dakinsa. Hajiyan dangi sai kuka take jin yana ta sumbatu yana cewa ko a aura masa pretty ko ya saceta ta karfi. Haka Hajiyan Dangi ya zauna dashi har yayi bacci shi kuma Baba ya kira senator Rufai ya sanar dashi halin da ake ciki.

Jirgin karfe 7 na safe suka biyo shiyasa kafin karfe 9 sun iso kano. Motoci uku ne suka je tarbar maigirma senate president da matarsa Hajiya Salama.

Gyadigyadi suka nufa gidan Hajiyan dangi. Mommy tana ganin Hajiya ta soma kuka. Bana son irin haka Salama baki san hawayen iyaye cuta ne ga ‘ya’yansu ba? Share idon tayi tace kinga irin yadda nake fama da yaronnan ko. Ni fa har cewa nayi baban nasu ya dena saka masa kudi a account amma yaki. Hajiya tace abar maganar nan yanzu bari mu gani ko ya tashi. Su hudu iyayen suka dunguma zuwa dakin da Junaid yake mahaifinsa ya bude kofar ya tarar dashi a kwance yana ta busa taba. Kwarai yayi mamakin ganinsu ya tashi da sauri…mommy na sannu da zuwa. Hannun daya kawo zai tabata ta doke tare da jan tsaki. Yasan fushi take yayi murmushi kawai ya kalli babansa. Oldman ya hanya? Wannan karon Hajiya ce ta doke masa baki. Uban naka kake kira oldman kuma junaidu? Dole kayi ta ganin ba daidai ba a rayuwarka tunda iyayenka ma basu da kima a idanunka. Da ace ka maida hankali kan addini da kasan cewa iyaye sun fi karfin wasa. Duk zama suka yi Senator Rufai ya cire hularsa yasa hannuwansa ya dafe kansa. Ya rasa yadda zaiyi da Junaid fitinarsa kullum karuwa take. Hajiyan Dangi ce ta labarta musu dukkan abinda ya faru game da yarinyar da Junaid yace yana so mai suna Hafsa. Ya maimaita sunanta a ransa yafi a kirga. Baya jin komai game da maganganun da suke yi. Hankalinsa ya tafi can tunanin yadda zai mallaki yarinyar nan mai suna Hafsa.

Previous page 1 2 3 4 5Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button