TUN KAFIN AURE Page 21 to 30

TUN KAFIN AURE???? 24
Dakata Imi zanyi maganinta da kaina. Cheque ya bata na dubu dari biyu. Idan na sake ganinki duk abinda ya faru dake ki kuka da kanki. Suna jan mota ta fita ta tari taxi don yau Rosie bata biyo ta ba saboda laulayi daya fara damunta. Murna take sosai don wannan cheque din sabon makami ne a gareta.
Daki aka bawa Hafsi da kawarta sauran yan biki suna wani masaukin. Nafisa ta tafi da yayarta Hadiza gidanta ita kuwa Hamida ta nace tare zasu kwana da amarya kafin washegari a kaita side dinta.
******************
Wani sabon kukan Hafsi da Ummati suka dasa lokacin da aka fito rakasu bakin motocin da zasu mayar dasu kano. Yanzu haka zata zauna da mutanen da bata gama sanin halinsu ba. Ga uban gayyar wato Junaid ko doriyarsa bata sake ji ba tun a wurin dinner. Kamar yasan tunaninsa take sai gashi ya fito da kananan kaya a jikinsa. Yau ma yayi kyau tunda kayan ba oversize bane. Har kasa ya durkusa ya gaishe da gwaggwaninta dasu Maman Ummati. Hadiza ta rungumota tana ta bata baki akan ta dena kuka haka. Kyaleta Hadiza na gulma ne fa kuna tafiya zata sake. Harararsa tayi yace ai gara ki nuna musu halin da kike min. Hajiyan dangi ta kama hannun Hafsi rabu dasu zan miki maganinsu. Anisa ta Amira ma sunyi nasu kukan da alkawarin zuwa idan anyi hutu. Haka dai suka rabu abin tausayi ana janye Hafsi daga jikin Ummati.
Bayan duk sun tafi aka dawo falo. Hajiya da mommy suka yi musu nasihohi da fatan alkhairi. Nafisa da Hamida suna gefen amarya suna kula da masu dada share wurin kafin su kaita. Sai da aka gama fadan Junaid yace to Allah Ya saka da alkhairi amma yaushe zaku bani matata? Mommy ta cire takalminta ta jefa masa to tsohon mara kunya ai gara ka nuna hali. Ya dafe kai Hajiyan dangi tana duba masa…yauwa Hajiya duba ki gani ko kan ya fashe. Hafsi kuwa dariya tayi har sauti ya fito yace kinci bashi Hafsi Hafsi. Nan suka zauna ana ta raha sai kawai suka ji sallama.
Mata ne biyu sunsha hijab daya sai kuka take dayar tana bata hakuri. Dif Junaid yayi ya dena dariyar da yake saboda ya gane mai muryar. Zuciyarsa ke bugun uku uku yaji yawon bakinsa ya kafe. Itama Hafsi ta gane yarinyar ko baa fada ba tasan akwai matsala don ta kula da yadda ya kidime da ganinsu. A fusace ya kallesu ubanwa yace ku shigo har nan? Wai ma waye ya baku izinin shigowa.
Mommy da Hajiya cikin rashin fahimta suke kallonsa. Junaid kana hauka ne zaka ga baki kayi musu irin wannan tarbar? Rosie ta kiyi hakuri Talatu an gama cutarki shine zaa ci mutumcinki saboda baki da galihu. Mommy tace ku zauna muji abinda ya kawo ku. Tilly harda fyace majina ai yafi kowa sanin dalilin zuwanmu. Idanun Junaid kamar an bada masa yaji yayi kanta yana sirfa mata zagi.
Kana tabata zansa a kulleka mara mutumci kawai. Daga kai yayi suka hada ido da Senator Rufai. Alhaji wai me ke faruwa ne? Yace ku zauna muyi magana. Su Rosie aka wani rakube a kasan carfet ita da Tilly. A bakin gate na gansu suna fada da security yarinyar can ya nuna Tilly tana ta kuka. Ganin haka na tsaya aka kirasu tayi min bayani. Cheque ya dauko daga aljihunsa ta mikawa Mommy. Kingani kudin daya bata jiya wai taje a zubar mata da ciki. Kinga goshinta inda ya fashe lokacin da yake dukanta ta fadi. Kamar anyi masa wanka da ruwan zafi haka yake ji. Me tilly ke nema ne a tare dashi? Kokari yake su hada ido da Hafsi ita kuwa idonta na kasa tana kuka a hankali. Salati su Hajiya suka hau yi tace lalacewar taka har ta kai ka bada kudin yin kisa. Kuka ne ya kwace musu ita da Mommy. Junaid yana ta basu hakuri. Hafsi ta mike zata shige daki don taga zancen kamar ba nata bane. Dawo dawo ai gara kada a munafunce ki Hafsa. Senator ne ya kirata ta dawo ba musu. Ya maida kallonsa ga Junaid. Ka san yarinyar nan? Eh na santa amma wallahi ban dake ta ba. Rufa min baki shashasha. Kullum yadda zaka zubar min da mutumci yake nema. Ko tsoron mutuwa baka yi.
Ke ya daka ma Tilly tsawa ta dago a firgice garin yaya kika amince masa. Ta kara jan majina ta fara bada labari. Ni ina sayar da kati ne kusa da wani club da suke zuwa a gidan wannan yayartawa nake da zama shine ya biyoni wai yana sona. Rannan rannan sai kuka….Rosie tace kudin kati yace taje ta karba shine yayi mata fyade. To ganin cewa danka ne bamu daga zancen ba.
Wallahi Álhaji karya suke duk karuwai ne….bakinsa yaji Hajiya ta make. Rufa mana baki. Rosie ta cigaba to da mun hakura sai kuma ga ciki shine muka neme shi kawai jiya sai yazo har gida ya bata cheque ita kuma ta karba don taga bana nan.
Hafsi tayi saurin daga kai tace ba kece kika zo wurin dinner ba kuwa daren jiya? Junaid yace yauwa Alhaji wallahi kaga itama zata min sheda wurin dinner ta biyoni ba raping dinta nayi ba. Mommu tace Hafsa kada ma ki fara kare masa don bakisan waye Junaid ba. Duk abinda akace yayi zan yarda. Allah wadaran iskanci yau mahaifiyarsa ma taki yarda dashi.
Senato Rufai ya kalli dansa cikin bacin rai yace ka taba ganinta? Eh ya amsa masa. Muamala ta shiga tsakaninku? Shiru ya kasa magana. Ya daka masa tsawa kai kurma ne. Hawayen da yake boyewa ya sauko yace eh. Innalillihi wa inna ilaihi rajiun. Koda ba auren so suka yi ba amma ace mijinka yana neman mata akwai ciwo. Hafsi duk auren ya kara fice mata a kai. Senator yace to ke zaa kaiki asibiti a sake miki gwaji idan ya tabbata da gaske yayi wa Junaid wani mugun kallo zamu jira ta haihu a aura maka ita. Mikewa yayi a fusace su Hajiya suka bi bayansa.
Batul Mamman
TUN KAFIN AURE????23
Tunda suka hau hanya basu tsaya ba sai a garin Abuja. Motar da Baffa ya hado da kayan da yayi wa ‘yarsa ita ce ta karshe cikin jerin motocin.
Duk girman gidan ba duka motocin bane suka sami shiga ba saboda yawansu. Shima gidan cike yake da mutane gashi basu iso da wuri ba. Dakin mommy su Hamida suka kai Hafsi. Ita dai kanta a kasa taki dagowa ta kallesu. Mommy cike da murna tace nasan kun gaji ga magriba ta kawo kai a kai su masauki suyi wanka aci abinci sai su shirya akwai wata dinner din karfe takwas. Hafsi ta kankame hannun ummati sai Nafisa tace mommy wanan fa aminiyarta ce tare zasu zauna kafin anjima ta dan kanne ido ai sai kamarsu ta Junaid ta kara fitowa Hafsi tayi saurin dauke ido.
Suna idar da sallar magriba akace Hafsi ta shiga wanka. Komai na toilet din daban yake…oh su Hafsi a toilet din matar sanata. Tana fitowa Hajiyan dangi ta tarar suna hira da mommy sai ta kasa fitowa. Hadiza da Nafisa wadanda tuni jininsu ya hadu kamar sun dade tare suka fara mata dariya. To yan nema da girmanku kuna tsokanarta ko. Fito kinji Mamana ni da nake so nan da yan watanni nazo yi miki wankan jego. Ai Hafsi ji tayi kamar ta nutse a kasa Mommy tace Hajiya banda kwacen ‘ya fa. Fita suka yi aka hau shirin amarya. Kwalliyar yau tafi ta sauran events din. Suna gamawa kowacce ta dau ado jiki da fuska aka fito. Motar da tafi kowacce kyau daga tsakiya wani abokin Junaid ya bude mata kofa ta shiga ya rufe. Taso kwarai Ummati ta shigo sai kawai taga angon nata ya bude kofa ya shigo. Ko tari bata yi ba don ganin yadda yake mata wani irin kallo. Ganin abin yayi yawa tace ya dai? Kamar ya, ya bata amsa. Ta dan turo baki kallo dai idan yayi yawa kuma zai shiga babin haramun. Yayi yar dariya Hafsi Hafsi kenan malaman karya. Wa ya fada miki kallon miji ga matarsa yana ciki. Yadda tayi da bakinta yasan sarai murguda masa shi zata yi. Yarinyar nan akwai tsiwa. Yace to basai kin murguda min baki ba idan kina son kiss, you just need to ask. Sakin baki tayi tana kallonsa lallai ma mutumin nan..dole ta fasa ta kara hararsa. Yayi dariya sannan yace karamar mara kunya kawai.Hular kansa yasa ya rufe fuskarsa. Idan mun isa ki tasheni jiya banyi baccin kirki ba. Ko kula shi bata yi ba ta juyu tana kallon garin da bata taba tunanin zuwansa ba nan kusa.