TUN KAFIN AURE 1-END

TUN KAFIN AURE Page 21 to 30

Nicon Hilton suka shiga. Manyan mutane da dama sun halarci taron. Su mommy ma da sauran matan manya sunzo amma shadaya suka koma gida. Sai wurin shabiyu da kwata mommy tayi wa Junaid waya kan su taho gida haka saboda Hafsi da suka yi zaman mota.

Ummati da Hafsi suna ta hira kafin motar da zasu shiga su karaso gabansu idon Hafsi yakai kanta. Tabbas matar da tazo wurin dinner dinsu ta kano ce. Matsowa tayi gaban Hafsi tana tafiya duk jikinta na girgiza amarya mun sake haduwa ko. Ga naki gift din nasan Juni boy da rowa baiyi sharing nashi dake ba. Wai wacece matar nan ne ta tambayi kanta? Tana mika hannu zata karba Junaid ya doke hannun. Da bomb ne ma haka zaki karba ko ya fada yana zare mata idanu. Mota na tsayawa yaja hannunta ya tura ta ya kalli ummati kema shiga zan biyo abokina. Yana rufe musu motar kafin su fara tafiya Hafsi taji yace cikin daga murya what the hell do you want? Suna tafiya a zuciyarta Hafsi ta kara yarda akwai wata a kasa tsakanin Junaid da yarinyar nan.

Ka zama uba ga abinda ke cikina. Ka rabani da rayuwar da nake ciki. Maana ka aureni. wadannan ne amsoshin da Tilly ta bawa Junaid. Imi dake ta yiwa Junaid horn ya shigo su tafi ya fito daga mota ganin yadda abokin nasa ya rude.

Ya mutumina wannan ce akuyar dake neman daga maka hankali? Ai ka barni da ita na farfasa mata jiki kawai. Yana magana ne yana kokarin dauko wani katon dutse cikin wadanda akayiwa wurin ado dasu. Imi baya daukar raini shiyasa Junaid ya tabbatar yana daukan dutsen nan jikin Tilly zai dire shi.

Batul Mamman????

TUN KAFIN AURE????25

Rigar jikin Junaid ta gama jikewa da gumi saboda tashin hankali. Yana ganin iyayensa sun shige yayo kansu ita da Rosie sam ya manta da Hafsi a falon. Ke don ubanki me kike nema ne a tare dani? Idan ciki ne dake ki sa a ranki har abada Junaid bazai taba zama uba ga abinda ke cikinki ba.

Hafsi tana jin furucinsa ta nemi hanyar barin falon rasa wurin shiga tayi don bazata bi su mommy ba a wannan yanayin da suka tashi. tana turo kofar dakin da take tsammani ma na masu aiki ne taji yo Tilly tana dariya…haba Juni boy ai kowa yaci tuwo dani miya ya sha. Ni ka zane a lagos daga na fadi abinda baiyi ma dadi ba. Rosie ta dan dake ta to banza rage muryarki. Ta maida kallonta ga Junaid ai kai karamin dan iska ne don giyar kudi ce ta kaika tashar iskanci mu kowa, ta nuna kanta da Tilly wahalar rayuwa ce ta kawo mu kaga dole mu fika rashin imani. Tsayawa yayi ya rasa yadda zaiyi dasu. Ya juya ya fita daga falon tare da buga kofa da karfi har sai da gaban Hafsi ya fadi.

Masu aiki ya tarar a barin nashi ya ma manta wai shara akeyi da sauran gyare gyare. Get out ya fada cikin karaji har su Nafisa suka fito daga ciki ita da Hamida. Sauri tayi ta dafa masa kafada Junaid what is wrong? Ban sani ba wannan karon hawaye yake sosai. Ku fita wallahi ko wani yaji ciwo. Ba shiri duk suka yi waje shi kuma ya shiga sabon bed room dinsa. Bai taba tunanin first day dinshi da Hafsi zai zo masa a haka ba. Tsakani da Allah yake sonta don a yadda ya tsara ma kansa ma bashi da niyyar takura mata. A hankali zai bita ya koya mata sonshi don yasan yanzu baya gabanta. Gashi yar tsiwarta da fadan da suke suna burge shi. Drawers ya rinka budewa kamar mahaukaci yana neman kayan maye ko yaya ya gusar masa da hankali ya manta da bacin ransa.

Wata taba dogowa ya dauko wacce Imran ya kawo masa tsaraba daga Italy. Kujera ya hau ya rufe idanunsa. Yana kunnawa yaji an fizge ta daga bakinsa yayi saurin bude ido. Hajiyan dangi ce tsaye kansa fuskarta jike da hawaye. Haba dan albarka. Yanzu ashe akwai wani maganin bakin cikin rayuwa bayan ambaton Allah da karatun Quran ko sallah? Ashe duk abinda ake fada maka bayan kunne yake bi. Bakin gado ta zauna dora kansa a kan cinyarta ya saki kukan da yake ta kokarin boyewa. Kyale shi tayi yayi mai isarsa har yayi shiru don kansa. Bai tashi daga kan cinyarsa ba yace Hajiya sai da nake son na canja halayyata kuma sai wannan masifar ta taso min? Kul ta ce masa tana girgiza masa kai. Allah sarki ne mai dinbin rahma da jinkai ga bayinSa. Shekararka nawa kana saba masa Yana hakuri da kai? Meye baka sha ba da aikin neman mata duk sai yanzu don Ya jarrabe ka kake neman kara fadawa ga halaka. Shin ka sani ma ko silar shiga aljanna ce wannan jarabawar? Dago kansa yayi yana kallonta. Hajiya wallahi yarinyar nan karuwa ce. Na rantse miki da Allah ita ta fara nema na a club. Abinda ta fada duk karya ne ya dan sunkuyar da kansa maganar cikin dai bazan karyata ba kila da gaske ne.

Kayi hakuri ka daure kaci jarabawar nan. To Hajiya zancen Hafsa fa? Ya zanyi da ita idan taki ni. Murmushi Hajiya tayi ,kasa Allah a ranka yarona komai zaizo da sauki. Hafsa tayi min yanayi da mutanen kirki idan ka nuna mata kai mutumin kirki ne sai kaga Allah Yasa ta zauna da kai lafiya.

Batul Mamman????

TUN KAFIN AURE????26

Neman Hafsi aka rinka yi a cikin gidan an rasa ina ta shiga. Mommy sai kuka take ko don taji zancen ciki ne ta gudu. Wata mai aiki mai suna Amaka ce ta tafi bakin gate ta tambayi securities din wurin ko sunga fitarta. Kusan awa biyu ana abu daya har Hajiyan dangi da Junaid suka shigo gidan don ta matsa masa akan yazo ya nemi gafarar iyayensa. Ganin gidan a hargitse Hajiya tace Salma me ya faru ne haka. Mommy cikin kuka tace bamu ga Hafsa ba Hajiya. Kinga har babansu ya fito nemanta.

Tunda akace Hafsi ake nema Junaid ya dena gane me ake fada. Na shiga uku Mommy ta gudu. Tilly da Rosie dake zaune a gefe ko a jikinsu. Ya nufo su cikin tsananin fushi ku sa a ranku indai banga matata ba wallahi kun gama ganin farinciki a duniya. Banzaye Matsiyata, karuwai….kafin ya kara magana Amaka mai girki ta fito daga dakinta da gudu. Madam amariya dey for my room. Bangaje ta Junaid yayi ya shige dakin. A daidai lokacin Senator ya fito yana waya da IG na police kan a baza masu nemanta. Me zai fadawa Mal Aminu? Duk kudinsa mutumin kwarjini yake masa sosai.

A kwance ya sameta kan gado tana ta rawar sanyi. Hafsi me ya faru ya fada yana shirin taba ta. Doke masa hannu tayi da kyar don wani zazzabi ne ya kamata sosai bayan tayi kuka mai isarta. Zuciyarta a cushe take da tsananin bakinciki. Badon abinda tayi ba tun kafin tayi aure tasan Allah bazai hadata aure da mazinaci ba.(don ma bata san yayi shaye shaye ba).

Ganin yadda ta hade fuska ga wasu hawayen sun taro a jajayen idanunta. Kasa ya sunkuyar da kansa kiyi hakuri Hafsi ki bari na taimaka miki ki tashi naga kamar ba kya jindadi. Harararsa tayi tayi tsaki a hankali zata mike. Ke ba kya gajiya da harare harare ne , wata rana sai na tsire miki ido. Duk da suna tare da damuwa da bacin rai amma sai da duk sukayi murmushi. Nafisa ce ta fara shigowa sannan su Mommy suka biyo baya. Hajiya tace mamana duk kin samu cikin damuwa tun dazu ana nemanki. Sai a lokacin suka kula da idanunta. Mommy ta zauna a bakin gadon. Kiyi hakuri yata nasan duk abinda zan fada zakiyi tunanin ko don bani na haifeki ba. Hafsi ta share hawaye ba haka bane mommy. Hamida tace wai ni me ya faru ne shi yazo yana mana fada dazu mun shigo kuma ance ana neman ta.

Babu wanda ya bata amsa. Mommy da kanta ta taimaka wa Hafsi ta tashi. Zazzabi ne a jikinki ko? A’a kaina ne kawai kuma zai dena idan nasha magani. Mommy tace ku zama shaida idan har yarinyar nan tace bazata zauna da Junaid ba sai an raba aurensu. Hajiyan dangi zancen bai mata dadi ba ta kama hannun danta. Muje Allah Ya kyauta.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button