TUN KAFIN AURE 1-END

TUN KAFIN AURE Page 31 to 40

Wani irin radadi ne ya ziyarci kafafunta duka biyun ta runtse ido ko motsi ta kasa yi saboda duk wurin pieces din glass ne. Tilly kuwa kwanciya tayi wanwar a kasa tana kwarma wayyo cikina, wayyo ta kashe min da na shiga uku. Rosie tace kiyi hakuri Talatu ki mike tsaye. Hafsi ta kallesu tana cewa sannu amma duk kafafunta sun kone saboda zafin abincin harda cikinta don karamin mayafi ta yafa sanin cewa babu ma aikata maza da ake bari su shigo cikin gidan. Ga plate din da ya tarwatse wasu duk sun soke mata saman kafafunta. Duk da haka bata damu ba ta duka tana son taya Rosie ta daga Tilly tsaye. Hannunta taji Tilly ta make tana kara sautin murya. Muguwa azzaluma don kawai ina da cikin mijinki shine kike son zubar min dashi. Wallahi duk abinda ya sami dana kotu ce zata raba mu. talakar banza.

Wawan mari Talatu taji an dauketa dashi. Mommy ta sake daga hannu Hajiya ta riketa yi hakuri Salma muji abinda ya hadasu. Rosie cikin kukan makirci tace Talatu ce ta fito zata sha iska tace dakin yana tayar mata da zuciya. Tana fitowa wannan yarinyar ta nuna Hafsi, mommy kuwa ta make hannun karki sake nuna min yarinya da yatsa wallahi. Rosie ta share ta cigaba da magana kawai tana ganin Talatu sai tace mata zanga yadda zaki haifi dan shege a gidannan. Tray din da plates din da ke kai duk ta tura mata a ciki. Hajiya ko kadan bata gaskata zancen ba ganin yadda Hafsi ke kuka tace mamana me ya faru. Hafsi ta fadi iya abinda ta sani. Mommy ta kama hannunta su koma falo ayi maganar.

Sai a lokacin suka kula da yadda jini ke bin kafar Hafsi ta dama Mommy tace maza a kira mata Junaid yazo ya kaita asibiti.

Da fara’arsa ya shigo falon. Mommy daga nasa yarki dafa min indomie sai ace in kaita asibiti. Ko ta kitse albarka. Gunjin kukan Tilly yaji daga bayansa ya juya da sauri lafiya? Rosie hade rai ka tambayi matarka da take son zubar wa Talatu da ciki. Yace au ashe sunanta Talatu ai na zata Tilly ne. Muryar Mommy yaji tana kiransa. Ya zan aika a kira ka sai kazo kana wani zancen daban. Ka dauko key mukai yarinyar nan asibiti nace. Ya kalle Hafsi duk fuskarta hawaye yayi saurin karasawa gabanta. Me ya faru Hafsi garin yaya kika ji jiwo? Mommy tace ka tashi mana ka zauna kana mata tambayoyi.

Suna shiga motar Nafisa na isowa Hajiya tace ta debo su Rosie su taho tare. Amma ta taho da security don kada su zama su kadai. A motar Junaid kuwa Mommy tana ta balai ya dauko musu masifa har gida. In Allah Ya yarda sai cikin ya zube. Ga Hafsi nan ki saki jiki kiyi ta zuba masa ‘ya’ya tunda su yake so. Hajiyan dangi ta gama waya da senator ta sanar dashi halin da ake ciki sannan ta dubi mommy tana bata hakuri. Junaid kuwa banda sannu babu abinda yake fadawa Hafsi. Hawaye ne wani ke bin wani a idanunta don ita kadai tasan me take ji musamman a cikinta. Ga babban mayafi ta yafa wani karin zafin a cikin.

Suna isa asibiti Junaid daukarta yayi don ganin yadda kafar taki dena jini. Emergency aka shige da ita da Tilly. Kururuwa kawai Tilly take yi ita tasan danta ya mutu. Ai kuwa basu dade ba nurse ta fito tace Tilly tayi bari. Nafisa ta rike baki cike da mamaki wato don sunji yau zaayi scanning suka bullo da wannan abin. Dariya tayi tana gyada kai sai tayi maganin mutanen nan.

Junaid yana tsaye doctor ya zare glass dinda ya shige kafar Hafsi yana ta mata sannu. Bayan an gama cirewa ansa plaster ya lura ta kasa kwanciya da kyau yace Hafsi akwai inda yake miki ciwo bayan kafar ne? A hankali ta daga kanta tace cikina. Fatar ta daye. WHAT??? Shima ya gama tsorata yayi saurin cire mayafin ya nunawa doctor din. Da almakashi ya yanke barin rigar daya kwanta akan cikin yace yi hakuri fatar bata cire ba. Ya dauko magani zai saka mata Junaid ya karba don tuni ya kule da kallon da yake mata. Dr bai ma san me yake ba ya nuna masa yadda zai shafa ya fita.

Ba karamin tausayi ta bashi ba yana shafawa tana runtse ido duk hawaye. Sai da ya gama ya duka yana hura mata cikin tuni ta hadiye kukan. Ya dago kansa sannu kinji Hafsi rabin raina. Ashe tsautsayi ne yasa nasa ki girki. Amma me ya hadaki da waccan. Fada masa komai tayi yace ba komai. Allah Yayi mana jagora.

Dr Sunusi yana fita Nafisa ta ja shi suka yi magana tace dr ina jin yarinyar nan cikin karya gareta. Yace ya akayi kika sani tace yar uwarmuce ce daga garinmu ina jin karya take ta matsu ne ta haihu sai tayi ta kiran cikin karya gashi kwanaki tayi bari baa wanke cikin ba. So nake don Allah kayi mata wankin ciki zan biya ko nawa ne. Bani da burin da ya wuce Talatu ta sami haihuwa. Ta dan matse hawaye. Dr Sunusi yace ba komai Hajiya ki kwantar da hankalinki. Yana fita Nafisa tace shegiya ai karen bana shike maganin zomon bana.

Batul Mamman????

TUN KAFIN AURE????31

Senator Rufai ranshi duk a bace da aka sanar dashi result din test din. Ya kalli Hajiya ni yanzu ya zanyi da Hafsatu? Duk irin abinda ya faru kafin a bashi aurenta gashi kuma baaje ko ina ba rayuwarsa ta baya tun kafin yayi aure tana dawo musu. Hajiya tace ni dai idan zaka dauki shawarata Rufai kabari yarinyar nan ta tare. Kullum mu kwana mu tashi da ita bata san makomar aurenta ba ai kaga ba dadi. Irin wannan ne idan iyayenta suka sani lamarin sai ya baci fiye da yanzu. Mommy tace anya Hajiya a bar shi da yar mutane kuwa? Bafa kowacce mace bace zata yarda ta zauna da mutumin da yake da da a waje ba. Wata ko dan kishiya bata so bare dan kafin fatiha. Senator yace to ku bani zuwa wata asabar din sai a kaita. Kisa su Hamida su tambayeta irin kalar motar da take so ma. Mtsw Ya danyi tsaki yaron nan bai min adalci ba wallahi. Gara tun da sauran mutumci na naje har gida muyi magana da babanta.

Zaman dakin duk ya isheta tana ta canja tashoshi babu wani abin kallo ta mike ta daga labule tana kallon waje. Tun jiya da su Nafisa suka zo da nurse bata sake fita daga dakin ba, Nafisa dai ta fada mata zasu dawo ta kai Talatu scanning. Tun dazu take jiran zuwansu ko ta sami abokin hira. Su mommy suna iya kokarinsu wurin debe mata kewa sai dai kuma suna cikin damuwar maganar cikin nan. Tana dan tunaninta ne ta kalli kasa suka hada ido da Junaid. Wani abu ne ya ratsa mata zuciya har kafarta. Murmushi yayi mata tayi saurin sakin labulen. Ta koma ta zauna bakin gado. Meyasa take saurin rikicewa ne akan Junaid..abinda take tambayar zuciyarta kenan.

Meyasa zata masa rowar kyakkyawar fuskarta ne. Su Hajiya suna masa gashin kuma gashi yanzu yana cikin jindadin kallonta ta gudu. Girman laifinsa yasa ya danne zuciyarsa bai dami iyayen nasa akan a bashi matarsa ba. Itama yana jin nauyinta sosai a ransa. Ina amfanin badi ba rai? Karamar yarinya tana masa kwarjini saboda ya zubar da girmansa a waje. Ga su Rosie sunyi kane kane a gidansu. Fasa shiga gidan nasa yayi ya koma main house. Mai aikatan gidan suna ta gaishe shi ya haye sama da sauri. Addua yake kada kowa ya ganshi a hanyarsa ta zuwa dakin Hafsi.

Rub da ciki tayi tana karanta wani littafin tarihin Annabawa da Hajiya ta bata taji an bude kofar. Duk a zatonta Nafisa ce tayi saurin juyuwa babbar yaya ina ta jiranki tun dazu yau bani da….kallon da yake mata bayan ta juyu yasa tayi shiru. Ya zaka shigo min ba sallama? Ni da dakin matata har sai nayi sallama? Ya kara kallonta ita duk kayan jikinta suna mata kyau. Dinkin yau ma riga da skirt ne fitted sunyi mata kyau sosai abinka da yar Mama tela. Ya jawo kujerar dressing mirror banda gulma duk wannan kwalliyar kice babbar yaya kike jira? Fada min gaskiya dai ni kika yiwa wannan kwalliyar ko. Bargo ta jawo ta rufe jikinta da sauri ni ba kai nayiwa ba. Kan gadon ya dawo ya zauna a gefenta ya rage murya are you sure? Har fa zuwa kika yi bakin window don na ganki kuma na gani. Daga cikin bargon tace ni Allah ba kai nayiwa ba. Ji tayi kamar ya tashi daga kan gadon sai dai kuma har fuskarta ta rufe yace malaiku na jinki kina cewa yar miji kika yiwa kwalliya ba shi ba. Yau littafinki sai cika da rubutu amma fa daga na hagun. Muryar nan ta shagwaba ta fara yi ni ba haka nake nufi ba…kafin ta karasa magana taji ya daga bargon daga wurin kafafunta ya shigo ciki. Hannuwansa yasa ya danne duka sides din don kada ta bude. Tuni idanunta suka raina fata, they were so close suna shakar numfashin juna. Ya kashe mata ido daya ina jinki wa ma kika yiwa wannan kwalliyar? Ki fadi abinda nake son ji sai na fita salin alin. Kanta a kasa tace kai. Malama ni banji ba fa. Ta sake cewa kai a hankali. Bari na sake matsowa kusa kila zanfi ji. Da karfi tace kai nayiwa. Good girl to ki dan bani chance mana na yaba kwalliyar. Bata ankara ba taji ya janyota ya rungume. Yana shafa mata gashi a hankali. Wata ajiyar zuciya yayi Hafsi Hafsi ki tayani addua yau nayi interview har biyu ta neman aiki. Nasan nayi laifi da yawa shiyasa su Mommy basu da time dina amma don Allah zaki zama friend dina kuma special adviser dina. Dago kanta tayi tayi masa murmushi eh. Thank you so much. Ya mike yau zaki min girki? Ban iya ba ta bashi amsa. Au kin manta da malaikun ne? Itama mikewar tayi na iya, me zaka ci? Kallonta ya sake yi gaskiya kayan nan naki fa suna…kodayake ba komai ki dai rufe jikinki kafin kije kitchen din. Indomie da kwai nake so ina sonta sosai. Idan kin gama ki kirani. Wayarta ya dauka yasa mata number dinsa. Duk ta tsufa anma dena yayin irinta. Itama Gwaggo Zainab ce ta siyo mata irin second hand dinnan. Ki taho dashi daki zanzo na karba. To kawai tace ya fita. Tayi tsaki meyasa idan taga Junaid take zama wata wawiya ne. Ko dan jan ajinma sai ya nemi ya gagareta.

1 2 3 4 5Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button