TUN KAFIN AURE Page 31 to 40

Kasa ta sauka babu kowa sai masu aiki ta dafa masa indomie biyu da daffafen kwai biyu. Tana shiga kitchen Rosie ta hangota ta koma daki da sauri ke Tilly tashi mu jirata a hanya. Akan tray ta dora zata fito wata mai aiki tace madam bari na kai miki Hafsi tayi dariya ai ba nauyi Chinwe nagode. Tana tafiya kamar daga sama Tilly tazo ta bangaje abincin ya zube a kasa plate din ya fashe kawai sai ji tayi Tilly na ihu wayyo Allah cikina.
Batul Mamman????
TUN KAFIN AURE???? 33
Tana kwance suna hira cikin nishadi nurse din ta dawo. To angama komai ina kudina? Rosie ta dauko dubu ashirin a jakar Tilly ta mika mata. Ki dai tabbatar babu wani cikin wadanda suka kawo mu babu wanda ya shigo. Nurse Talle ta washe baki tana murna ta ce angama ranki ya dade. Bata dade da fita ba Dr Sunusi ya shigo dakin tare da wata nurse din. File ya bude yana dubawa, ya dan dago kai kece Talatu Jibo ko? Eh ta amsa da kyar tana ta rike ciki ita a dole mara lafiya. Yanzu likita na rasa baby na kenan? Kiyi hakuri mana ki dena kukan Rosie ta fada tana rarrashinta. Dr yace ya naga kina rike ciki ne ko bai gama fita bane? Saurin sakin cikin tayi ya fita duka ni dai ku sallameni kawai na tafi. Ya kalli nurse din kinga ki gyara min dakin can zanyi mata wankin ciki, ya maida kallonsa ga su Tilly. Ai kada ki damu idan nayi miki wankin cikin before you know it zaki sami wani. Yadda kike rike cikin nasan akwai saura. Wannan karon kukan gaske ta saka masa kayiwa Allah likita kada kayi min wallahi cikin baya ciwo ko kadan. Yace ai dalilin wankin kenan idan akayi bari ba ciwo nan ma akwai serious problem. Tana kuka yace a kawo wheelchair a kaita dakin da zai mata a can.
Kankame Rosie tayi bazata tafi ba. Rosie tace kiyi hakuri Tilly kada asirinmu ya tuno. Saboda tsabar kwadayin daya kawo su Tilly tana ji tana gani akayi mata D and C. Likita dai yasha zagi ta uwa ta uba.
Sai dare aka sallamosu duka a gidan suka hadu da Hamida suna jiransu da Senator. Ko daki basu shiga ba Rosie tace yallabai munyi waya da kawu na baban Talatu yace gobe zaizo gari don na fada masa abinda ya faru. Anyi mata fyade kuma anyi sanadin zubar da cikin. Wallahi maganar nan har yan jarida sai na fadawa. Kowa kallonta kawai yake tana rashin kunya Senator ya hanasu magana a cewarsa dansa ne ya ja masa. Tana gamawa yace idan sunzo goben zaa daura musu aure da Junaid. Yana gama magana ya juya zai haye sama zuciyarsa na kona saboda bacin rai. Ta sake cewa ita kuma wadda ta zubar da cikin idan zaayi adalci sai a saketa ko a dau mataki. Hamida tace uban kuturu kuma yayi kadan in fada miki. Hafsi mutu ka raba da Junaid. Hajiya tace ku wuce ku tafi gidajenku Allah Ya bamu alkhairi.
Junaid da Hafsi basu san abinda ke faruwa ba saboda ya wuce pharmacy da ita neman wani magani. Ac ya ware mata ya ja mayafinta can baya yadda cikin zaisha iska. Motar ko radio bai kunna ba yana ta kallon yadda Hafsi take ta zumbure zumbure. Yasan itama laifinsa take gani ya jawo musu masifa har gida an rasa yadda zaayi dasu saboda gudun abinda zaije ya dawo tunda babansa dan siyasa ne. Tarkace da yawa ya siyo mata na kwadayi bayan ya siyo maganin. Ganin bata da niyar kula shi yace Hafsi Hafsi kiyi hakuri akan abinda ya faru. Bansan dalilinta nayi miki sharri ba amma zanyi maganin abin. Tsautsayi ne ya kaini ga saninta amma kisa a ranki wallahi bazan aureta ba don nasan ko wacece Tilly. Cikin takaici yake maganar Hafsi tayi biris dashi. Ba komai ke damunta ba face yadda aka kasa gano karyarsu kuma ita bata da wani shaida akan abinda taji. Tasan Nafisa ta yarda da ita amma idan basuyi wani abun ba suna kallo Senator zai sa Junaid ya auri wannan matar. Wai ma ya akayi suka yarda bari tayi ne? Ko dai da cikin gasken? Ita ta gama zama confused. Har ta fara kokonto akan abinda kunnenta ya jiye mata
Batul Mamman????
TUN KAFIN AURE????35
Washegari wayar Junaid ce ta tasheta daga bacci da asuba. Ko da ta dau wayar sai taga an rubuta J dear. Lallaima wato har wani saving sunansa yayi a haka. Ta daga cikin muryar bacci tace waye ne waya da asussuba kamar me karbar bashi. Murmushi yayi yana shafa kansa ai zaki biya bashi ne Hafsi Hafsi amma not now. Yanzu dai ya kika kwana? Ya jikin? Da sauki ta ams itama murmushin take. Wani son Junaid takeji yana ratsa ta. Amma babu yadda zatayi yanzu sai sun kawar da su Talatu daga gidan.
Karfe 9 na safe aka sanar da su Mommy zuwan baban Talatu Mal Jibo da kannensa biyu. Senator ta tayar daga baccin da sai bayan asuba ya sami runtsawa saboda tunani. Doguwar riga ya saka ya mike. Ki aika a kira min Junaid tun jiya ban sanar dashi maganar auren ba saboda kada ya daga min hankali. Shi ya jawo matsalar nan so he has to deal with it. Mommy tace amma yallabai baka ganin kara dulmiya shi zamuyi kaga baya sonta kuma basu da kamanin mutumci. Hannu ya daga ya dakatar da ita…haba Salma duk shi baiyi tunanin haka ba sanda yake bin duk macen da ya gani. Ai duk rayuwar da mutum yayi kafin aure indai ba Allah Ya kare ba sai kiga tana bibiyarsa. Ko kadan ita dai abin baiyi mata dadi ba amma dole tayiwa mijinta biyayya. Haka suka sauka kasa ya fita wani falo ya tarar dasu a zaune sun kusa cinye duk abinda aka kawo musu na tarar baki. Bayan doguwar muhawara Senator Rufai wanda rashin son tonon asiri yasa babu wanda ya iya sanarwa halin da ake ciki cikin abokansa da yan uwa ya tsayar da magana akan zaa daura auren Junaid da Talatu nan da sati biyu. Mal Jibon karya yace ranka ya dade ni dai gara a daura auren nan asabar mai zuwa saboda kada ya lallaba ya sake banka mata wani cikin. Wata irin tsawa Senator Rufai ya daka masa ya mike tsaye…kada ka dauki saukin kaina a matsayin shashanci mana. Ina binku ne a hankali kawai don in tayaku sayawa yarku mutumci. Idan kuka shige gonar da ba taku ba wallahi ina da karfin da zansa duk a neme ku a rasa. Duk abinda nake yi saboda girman Allah nake yi so be careful , be very careful. Yana gama magana ya fita Tanimu yace kai baaba kaji yadda hantar cikina ke kadawa kuwa. Baaba yace ai sai da nayi dana sanin magana ma. Wallahi idan Rosie bata biyamu da kyau ba jikinta ne zai fada mata. Kaga yadda yake muzurai kuwa. GG dake gefe yace ai ni na fiku tsurewa yadda yace zai batar damu gani nake kamar ya gama gane mu ma.
Baffa ya dauki wayarsa dake faman ringing tun yana sallar walha ya duba sai yaya sirikinsa ne. Bayan sun gama gaisawa Senator ya labarta masa dukkan abinda ke faruwa a gidan nasa. Mal Aminu dai yau ya rasa bakin magana saboda takaici yanzu irin gidan da Hafsan sa ta tare kenan. Senator ya cigaba da bashi hakuri da neman shawara. Mal Aminu duk yadda ransa ke kuna yace dole ayi abinda ya dace don a rufa asiri kuma shi yanzu kullum Junaid yana kiransa kuma ya yarda da irin shiryuwar da yake ji tare dashi. Haka suka yi ta shawara Senator yace idan ba damuwa ko zaku iya zuwa zuwa Jumaa kai da Alh Bashir saboda bani da wanda zan iya tonawa sirrina. Lallai rayuwa babu yadda bata zuwa ga bawa. Allah Ya kara rufa mana asiri. Daga nan Senator ya nemi dansa ya sanar dashi shawarar daya yanke. Junaid mikewa yayi cikin rudani yana daga murya…wallahi wallahi Alhaji bazan auri Tilly ba, karuwa ce fa.