TUN KAFIN AURE Page 31 to 40

Batul Mamman????
TUN KAFIN AURE????34
Yadda tayi zurfi a tunani yasa Junaid kare mata kallo. Wayarta ce ta hau tsitsi shi ya dawo da ita daga dogon tunaninta. Da sauri ta dauka ganin baffanta ne. Tana masa sallama yace Hafsa ya jikin? Dazu babanku yayi min waya kinji ciwo. Ince ko babu wani mugun rauni..dariya tayi ashe kana sona dai Baffa. Yayi dan gyaran murya kaniyarki wasa nake dake ne. Ta sake wata dariyar baffa babu ciwo sosai glass ne ya shige min kafa amma an cire. To sannu Allah Ya kara sauki, amma ki rinka kula kinji ko. Ga Mamanki duk ta damu itama. Sun dade suna hira da mama da kannenta kowa yana mata sannu. Bayan ta gama wayar yace yanzu tun dazu ina magana kina share ni sai da kika ji muryar su baffa kika yi dariya ko. Yadan bata fuska kamar zaiyi kuka Allah Sarki Junaid babu mai sonka. Har tissue yasa yana goge ido , bata san lokacin da dariya ta kubuce mata ba. Wayarta ya dauka yana juyawa. Ni na gaji da ganin wannan toy din. Idan munje gida kizo ki karbi sabuwar dana siya miki. I hope you will like it.
Bayan yayi parking din motar Hafsi ta bude zata fito yace tsaya ina zuwa. Zagayowa yayi ga mamakinta sai kawai taji ya dauketa. Yau karo na uku kenan yana daukarta. Tana ta mutsu mutsu ya ajiyeta kada wani ya gansu ya share. Da kafa ya tura kofar motar bai tsaya ko ina ba sai a side dinsu dake bayan gidan. Ajiyeta yayi ya bude kofar ya sake daukanta, kan doguwar kujerar falo yasauke ta ya duka hannunwansa duka biyu a gwiwoyinsa yana ta nishi. Wai Hafsi haka kike da nauyi…anya baki kai buhun shinkafa biyu ba kuwa. Filon kan kujerar ta jefa masa wallahi bani da nauyi. Kuma ma ai bance ka daukeni ba. Ya sami wuri kusa da ita ya zauna tare da janyota jikinsa. Gaskiya yarinyar nan idan kika hau kaina buzu na zaa dauka. Mintsini yaji a gefen cikinsa tace ya fa isheka ko don kaji ina shiru. Ya kama gefen cikin ke dama haka kike? Don kin kone a ciki nima nakasa ni zakiyi. Ya danyi murmushi me kama da na mugunta kinsan fatar cikinki zata fi dadin mintsini ko. Tana jin haka tayi saurin tashi sai ta fada jikinsa saboda zafin da kafarta tayi. Rungumeta yayi sosai hmmm su Hafsi wayon ki dan ji dumin jikina shine kika wani fado min a jiki. Maganar da tayi niyar yi ce ta makale mata saboda kunya data kama ta. Zata bashi hakuri taji ya hade bakinsu wuri daya. Cikin kankanin lokaci suka tafi wata duniyar sai dai basu dade ba suka ji bugu a bakin kofa tare da sallamar Hamida cikin daga murya.
Tsaki yayi ya amsa mata tare da mikewa. Tace Yaya munji shigowar motarka amma har yanzu Hafsi bata shigo gida ba. Wani tsakin yayi gata nan zuwa kill joy sim dinta zan saka a sabuwar waya. Hafsi dai gintse dariya tayi don yadda taga yana bin Hamida da harara bayan ta rikota zata taimaka mata su koma cikin gida.
Batul Mamman????
TUN KAFIN AURE???? 36
Senator Rufai yace Allah Yasa magajiya ce sai ka aureta. Yau kaine kake kiran wata karuwa? Ka manta irin kukan da mahaifiyarka ta rinka yi lokacin da kake bibiyar matan banza. Yau gashi a sanadiyar hakan Junaid wasu yan iska suna neman bata min suna. Duk rayuwar da nayi a politics ina taka tsantsan saboda abokan gaba. Hajiyan dangi dake zaune a gefe ta dago kai cikin fushi lallai ma Rufai ashe duk abinda kake ba saboda lahirar mu kake yi ba. Dama saboda mutumcin siyasa kake yi. To wallahi ka sa a ranka duk abinda ya sameka kai ka jawo tunda babu abinda kake don Allah. Mommy dai kuka take don abin yayi mata yawa. Hajiya tace Junaidu? Ya amsa mata cikin kuka. Ina so kayi wa babanka biyayya hakan shine shaidar ka shiryu. Kuma da yardar Allah zaka ci jarabawar da Yake yi maka. Tashi ka tafi Allah Yayi maka albarka. Yana fita mommy ta hau rokon a janye maganar aure. Yace kun kasa fahimta ta ne Hajiya. Nasan ina son kare mutumci na amma ki duba ki gani indai yayi mata cikin da gaske kada su sami abin tozarta shi nan gaba. Bani da burin da ya wuce naga iyalina suna zaune cikin kwanciyar hankali amma hakan bazai taba yiwuwa ba sai mun toshe duk wata kofar da wani zai iya samun damar daga mana hankali. Senator yayi iya kokarinsa wurin ganin iyalinsa sun amince da auren don a iya tunaninsa da haka ne kawai zaa iya toshe bakin su Talatu.
Kamar wanda aka jefo daga sama kawai ganinsa tayi a cikin dakinta. Yar tsiwar data yi niyar yi masa saboda ya shigo mata daki ba sallama ma kasawa tayi saboda wata irin runguma da yayi mata. Cikinta ne ya soma zafin wurin da ta kone ta fara neman ya sake ta. A kunnenta taji yana magana cikin muryar kuka har hawayensa na sauka a kafadarta. Hafsi please dont ever leave me. Dole ta hakura ta tsaya har ya gaji don kansa sannan ya ja hannunta suka zauna a bakin gado. Kansa ya dora kan cinyarta sannan ya fara magana. Alhajinmu yace lallai sai na auri Tilly. Dama tasan haka zata iya faruwa sai dai tayi shiru ganin kamar bai gama magana ba. Na fada masa karya tayi min amma yaki yarda. Hafsi ke kadai kin isheni rayuwa ina tsoron hadaki da kwararriyar yar bariki. You are too innocent bazaki iya kishi da ita ba. Gashin kansa ta shafa indai Alhaji ne ya baka umarni to don Allah kayi masa biyayya. Kada ka manta aljannarka tana tare da farin cikin iyayenka a kanka. Tana gama magana yaga ta share kwalla yayi tashi zaune kingani ko tun yanzu kin fara kuka. Sai kuma ya kashe mata ido ko dai kishi ne ya motsa. Kyakkyawan rankwashi ta sakar masa ya dafe kai yarinya baki sanni ba ko. Sai a lokacin ya kula ashe daga ita sai wani towel iya gwiwa. Yayi wata dariya yau zaki gane nima mugu ne. Towel din ya kama daga daidai kirjinta yana ja tana ja. Muryarta na rawa tace zan maka ihu fa? Ai idan kika ji mace tana zanyi ihu ba yin zata yi ba. Besides ba zaki so a shigo a ganki a haka ba. To naji ta ce masa, don Allah kayi hakuri bazan kara ba. Kallonta ya rinka yi cike da so yace come here. Sake rungume ta yayi yana shakar kamshin jikinta. Shima kansa yana mamakin yadda yake iya kasancewa da ita kuma ya iya hakura ba tare da ya nemi biyan bukatarsa ba. Ya amince wannan shine true love.
Haka suka kasance suna nunawa junansu kulawa har ranar asabar ta zagayo wadda ranar Baffan Hafsi da Alh Bashir zasu iso abuja kuma ranar ne auren Junaid da Talatu Jibo Aka Tilly.
Batul Mamman????
TUN KAFIN AURE????38
Rosie tace dadina dake ba kya cin ribar abu. Kin fiye rashin hakuri kamar gudawa. Ki zuba ido yau a jikinki zai angwance. Ki dai sha kaya da kyau don ki kara kama shi a hannu.
Hamida ana ta rawar kafa kamar ita ce zata tare. Nasihohi da adduoi Hajiya da mummy suka yi wa Hafsi. Hamida taja hannunta masu aiki suka bi bayansu da akwatunanta. A ciki suka tarar da Nafisa da yaranta ‘yan mata biyu Ummu mai sunan mummy da Husna. Suna ganin Hafsi suka kankameta suna murna. Nafisa tayi musu tsawa ku sake ta mana haka kada ku kayar da ita. Husna yar shekara biyar tace Mama Hafsa ni a nan zan zauna tare da ke ko. Hamida tace asheUncle Junaid zai kore ki kuwa. Ai ku da gidan nan sai nan da wata tara. Hafsi ta sunkuyar da kai kasa cike da kunya. Haka suka zauna suna ta hira. Ko kadan basa barinta tayi kewar yan uwanta saboda yadda suke janta a jiki.
Tun daga bakin kofa yake jin kamshi mai dadi sai dai zuciyarshi wani irin kunci take masa. Yana shigowa falon yan uwansa suka fara tsokanarshi. Nafisa tace to ya isa haka ku tashi mu tafi. Duk suka yi mata sai da safe suka fita. Dama tun shigowarsa Hafsi bata yi masa magana ba saboda yadda su Hamida ke tsokanarta. jin bashi da niyyar kawar da shirun dake tsakaninsu tace masa ina yini. Lafiya ya amsa a takaice. Can ya sake cewa tashi mu shiga ciki muyi sallah ko. Dadi hakan yayi mata ta kara tabbatar da cewa Junaid ya fara maida hankali a lamuran addini. Fuskar nan tata a rufe ta bi bayansa. Suna shiga yaji hakurinsa ya soma karewa yace mata kiyi alwala ina zuwa nayi mantuwa a mota.