TUN KAFIN AURE 1-END

TUN KAFIN AURE Page 31 to 40

Cike da damuwa yake tuki ya rasa abinda ke masa dadi. Ace ya rasa abinda zaiyi ta tunani a yau sai Tilly, Why ??? Gidan ya nufa yayi saa suna zaune a falo. Mamaki karara a fuskar Tilly yace hado kayanki ki sameni a mota. Yana fita suka sa shewa da dariya. Tilly ta yi saurin dauko jaka ta watsa kaya kadan a jakar ko sallama babu ta fice. Rosie ta koma daki tana cin farar kasa wadda ta zame mata abinci yanzu. Mayen cikin yaki zubewa ita kuma tana tsoron wankin ciki.

Kusan awanni biyu kenan da fitarsa amma taji shiru. Tun tana sharewa har ta kasa hakuri. Lekowa tayi wajen gidan babu daya daga cikin motocin da yake shiga. Komawa tayi ta zauna tana ta sake sake. Gajiya tayi ta tashi tayi sallar isha da nafila ta zauna kan darduma tana karatu.

Hotel ya kama musu don yasan babu mai bashi mukullan gidan da Alhaji ya kama masa kafin ayi masa wani ginin inda zai iya hada matan biyu. Tilly ansha gyara ciki da waje. Ta nuna masa salo salo na kwarewarta a fanin shegantaka. Wayarsa ce tayi kara wurin shadayan dare. Har ya fara bacci Tilly ta dauka taga ansa H dear. Kashe wayar tayi gaba daya tayi tsaki sannan da dariyar mugunta. Yarinya yau zaki bushe ta fada a fili..

Saroro ta tsaya kallon wayar. Yanzu ita Junaid ya kashewa waya? Ko tayi masa laifi ne? A falo ta kwana ranar tana kuka ita wannan wace irin rayuwa ce daga wannan sai wannan kullum. Ta yanke shawarar idan bai dawo ba da safe zata sanar da iyayensa.

Batul Mamman????

TUN KAFIN AURE????37

Hafsi da Ummati sun kusa rabin awa a waya suna ta shawarwari don yanzu kam Hafsi tasan bazata iya zama haka babu abokin shawara ba duk da cewa su Hamida suna iya kokarinsu. Yayarta Hadiza ma ta bugu sun dade suna magana. Tana wayar Nafisa ta shigo da wata karamar jaka a hannunta ta zauna kan kujera. Hafsi ta gama waya suka gaisa. Nafisa tace kanwata kinga yadda Allah Yake ta jarrabar mu da abubuwa kullum ko? Yauma hakuri dai zan kara baki. Da yar shawara kadan. Kinga wadanan kayan masu tsada ne amma fa idan kika sha baza ayi asarar kudin tara ba. Suna gyara mace sosai sannan ki rika shan fruits musamman kankana. Akwai kunun aya ma da ake hadawa da ita da cucumber, dabino, kaninfari, citta da kwakwa. Zan hada miki da kaina kafin anjima. Munyi magana da Mommy ke zaki fara tarewa sannan bayan sati daya talatu ta tare amma gidanta daban ne. Kiyi iya kokarinki ki zama tamkar karuwa kema a wurin mijinki kinga ya san wasu matan so raba shi da irinsu sai kin dage sosai. Kan Hafsi a kasa duk kunya ta kamata ta kasa magana. Nafisa ta nuna mata yadda zata yi amfani da kayan data kawo mata. Ke ni ki dena jin kunyata bazan taba bari matan banza su rabaki da mijinki ba. Tunda kika auri Junaid kin gama mana komai.

Talatu yar gidan Mal Jibo mai faskare amaryar Junaidu dan sanata. Kirari ne Rosie da ke zaune kan kujera take wa aminiyarta. Tilly tace yanzu fa dole inyi ta amsa sunan Talatu sunan dana manta dashi tun a kauye. Suka tafa sanan rosie ta miko mata kullin magani. Ga wanan kawata ki shafa hannu ne ki taba shegen. Wallahi zaki sha mamaki don watarana ma sai ya gundireki idan ya fara like miki. Wata shewa suka yi tace Rosie ba kyau. Gara tun wuri na fara kiranki Samiranki kada ayi subutar baki a gaban surukai. Hakane, yanzu dai zan kira shi yazo a sunan kina zubar da jini sai ki fara gwada saarki. Bikin ma da akace muyi a garinmu zasu sha mamaki don sai munyi kara’i. Sake tafawa sukayi sannan Tilly wadanda sun koma dakin da Rosie ta kama musu ta dauki waya ta kira shi.

Tun safe ya kasa zaune ya kasa tsaye saboda tsananin farinciki yau Hafsin sa zata tare. Ya fito daga wanka yaji karar waya a zatonsa ma Hafsi ce don tun dare take tsokanarshi da flashing. Tsaki yayi kamar tana gabansa daya ga number din Tilly. Yana dauka Rosie ra kwarma ihu tace yazo Tilly tana ta zubar da jini. Wani tsakin yayi ya ajiye wayar ya cigaba da shiryawa. Sake buguwa suka yi har sau biyar sannan ya dauko a wulakance yace gani nan zuwa. Cikin gidansu ya shigo ya fadawa Mommy inda zashi. Ta tabe baki sai ka dawo. Kada dai ka dade yace to. Shi har a ce masa kada ya dade yadda yake zumudin nan.

Suna jin tsayuwar motarsa Tilly ta kwanta a kasa tana wai wai. Kudi ya jefa mata yana mata kallon banza gashi nan nasan abinda kike nema kenan. Ganin bashi da niyar taimaka mata ta tashi ta mike ta riko shi. Juni boy ka saki jikinka mana ai an riga an daura. Ina jiranka anjima kazo mu tafi namu gidan don a sannu zansa ka manta wannan kwailar. Hankadeta yayi har ta fadi kamar zaiyi magana ya fasa ya fice. Rosie dake kitchen ta fito da sauri tana mata sannu. Tilly tace aikin banza maganin naki baya komai ji yadda ya ture ni.

Batul Mamman????

TUN KAFIN AURE????39

Wani azababben ciwon kai ta farka dashi lokacin da taji bugun kofa. Sai bayan asuba bacci ya sace ta, dan goge fuska tayi ta bude kofar. Amaka ce dauke da tray ga wani a kasa shima duk kwanukan abinci ne a ciki. Tace Amariya goodmorning…Hafsi ta dan saki fuska ta amsa tare da daukar tray din kasan suka shigo dashi. Amaka tace Madam say make you tell me wetin you wan chop for lunch. Hafsi tace what? Ita fa bajin pidgin english take ba. Ta dai gane lunch ta ce mata ta tafi kawai zata shigo. Har shabiyu tana jira ganin dai bashi da niyar dawowa gashi wayoyinsa duk ta kasa samu ta fito ta tafi main house. Babu kowa a falon sai akwatuna guda uku daga bakin kujera. Dakin Hajiya ta fara leqawa ta ganta tana daura laffaya. A’a mamana keda kike amarya me ya fito dake kuma. Nima shirin komawa Kano nake yi yanzu Rufai nake jira yazo muyi sallama sai a kaini iyaport. Hafsi tayi dan murmushi tace Hajiya bana son ki tafi. Allah sarki Mamana bakya so naje na gyara nawa auren ne? Tare fa aka kawo mu dake gashi muna neman wata daya. Wasu hawaye masu zafi ne suka sauko mata Hajiya a rude tace haba Hafsatu kada ki karyar min da zuciya mana. Ki kara hakuri in Allah Ya yarda zaku sami zaman lafiya da Junaidu. Kirawo min shi mu yi sallama sannan ki goge idonki kada yace na taba masa mata. Kanta a kasa tace baya nan Hajiya. Dan bata rai tayi ina yaje kuma daga kai masa amarya. Mummy dake tsaye a bakin kofa tace garin yaya kika bari ya fita amarsu. Har kasa ta kai ta gaishe da mummy sannan soma kuka. Duk hankalinsu ya tashi aka suna tambayarta ko lafiya. Da kyar tace musu bai kwana a gida ba. Sai suka fara salati. Mummy ta dauki waya ta kira shi aka yi sa’a a kunne wayar take.

Tilly ta kalli wayar bari na daukar maka Juni boy. Kasan yau rana ta ce so duk mai kira yayi hakuri. Ba musu ya mika mata batare da yasan mai kiran ba. Hello ta fada bayan ta amsa wayar. Mummy a dan razane tace wacece? Ahhh tuni ta gane muryar jarababbiyar babar tashi. Tace matarsa ce Talatu don Allah a dena kira yana bacci ne idan da sako ki fada na gaya masa. Yadda take maganar a ladabce shi yasa Junaid ta kara lafewa jikinta yana mata cakulkuli please ki ajiye wayar anjima na kira. Karaf maganar sai a kunnen mummy tace Junaid da karfi. Tilly bata bare yaji ba ta ajiye wayar ba tare da ta kashe ba tana ta dariya please baby ka bari kaga jiya baka barni na runtsa ba.

Jefa mummy tayi da wayarta tana kuka mai tsuma zuciya. Maganar Junaid ta tabbata karuwa ce yarinyar nan. Suna tare bansan ko a ina ba amma suna tare. Hajiya tace inna lillahi wa inna ilaihi rajiun. Anya zan iya komawa kano kuwa salma? Yarona yana cikin matsala. Mummy tace ki tafi hajiya ai tsuntsun daya ja ruwa shi ruwa zai daka. Rashin jin maganar iyaye yasa ya kwaso mana balai. Bari na tado Yallabai wallahi a nemarwa yarinyar nan saki tun wuri. Ni bazan iya kallon Safiya ba ina kallo dana yana wulakanta musu ‘ya.

Previous page 1 2 3 4 5Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button