TUN KAFIN AURE Page 41 to 50 (The End)

Kallon wayar yayi waye ke kiranki? Mtsw rosie ce duk ta dame ni tana son na taimaka mata da kudi. Ina wanda na baki last week baki bata bane? Ta kara yin tsaki kasan gayyar tsiya na rasa me take da kudin. Yace to bari idan na fita zan kawo ki bata. A ranta tace kyayi kya gama bazan bayar ba don yanzu kam yadda yake yawan hade mata rai tasan magani ya fara ja baya kuma da kunya ta koma gidan rosie. Wata biyu rabon da taje kudin da take karba ma account dinta yake shigewa..
Rosie ta kalli wayarta da katon cikin dake gabanta. Kudin abinci ma yanzu gagararta yake amma Tilly taki taimakonta. Gidan da ta tare ma bata sani ba bare tabi sawu. Shawara daya ta yanke ta neme malaminta a warware abinda takewa Junaid ya dawo hayyacinsa ya koreta.
A kasa mai tsarki hafsi da sauran iyalan senator Rufai Bukar sun dage da yawan sallah da adduoi don nemarwa Junaid shiriya. Shi kanshi senator da ya dage da istigfar ba karamin mamaki yayi ba yadda yake jin canji game da al’amuransa. Idan Junaid ya dawo garesu dole su koma a nemi ilimin addini sosai.idan da asiri a jikin junaid to harda sakacinsa ta bangaren addua.
Batul Mamman????
TUN KAFIN AURE????44
Junaid yace kowa ya tuba don wuya fa ba lada. Imran na dariya yace ai wallahi da lada tunda nayi nadama kuma dai ai ba bari saida nazo gargarar mutuwa ba. Yanzu dai abar zancena wane mataki zaka dauka game da Tilly? Gaskiya i cant say for now matsalar tafi yawa idan na ganta. Ita kuma dayar ina sonta sosai amma na rasa me ya hanani nemanta. Bayan dan tunani Imran yace na sama mana mafita. Cikin zakuwa yace wacce? Kana ganin zaka iya hakura da mace indai babu aure a tsakaninku? Jimm yayi na dan lokaci. Tilly ta zame masa jaraba yace in sha Allah. To indai haka ne ka kira ta yanzu a waya. Junaid ya dauko wayar ya kira. Imran yasa speaker kafin ta dauka yace kayi mata saki uku yanzu ka yanke ala…..hello? Juni boy ina ka shiga ina ta jiranka. Imran ya zungure shi yana magana kasa kasa. Saketa mana…a dan tsorace yace Tilly na sakeki saki u..u..uku. wata irin kara suka je imran ya kashe wayar yace to tura mata text don a sami shaida. Jiki ba kwari ya tura Imran yana masa dictating abinda zai rubuta. Yana tura send Junaid yayi wata ajiyar zuciya. Imran yace idan har bazaka iya ba ka barni na biyoka gidan. No ka barni kawai ina zuwa zan koreta.
Hafsi tana ta juya waya a hannunta ta kasa bugawa. Tun a kano Ummati ta bata shawara yanzu ma ta sake kiranta taji ko ta kira tace mata yanzu zata kira. Sai da ta tattaro dukkan courage dinta ta kira. Wayar tayi ringing har ta katse bai dauka ba. Kamar tayiwa ummati Allah Ya isa. Gashi ta zubar da ajinta kuma babu biyan bukata. A lokacin da take wayar Junaid da Tilly fada suke kowa murya a sama don bai ma ji karar wayarsa ba. Nishi take kamar wata kumurcin maciji Juni boy baka isa ba na rantse maka. Ni zaka yiwa wannan rashin mutumcin, saki har uku? Duk da bashi da kwarin gwiwa sosai yace ki fita kawai kafin na kira security. Daki ta shiga da gudu ta barbada dan sauran maganin a hannunta. Saboda kuka bama ta ganin gabanta sosai. Duk duniya babu wanda ya isa ya raba mu. Tana yin kansa cikin zafin nama ya tureta bai san lokacin da ya fara karanta La haula wala quwata illa billah. Zafi sosai jikinsa yayi sosai har yáji kamar kafarsa bazata iya daukarsa ba. Tilly kuwa kan wani muzurunta ta fada daya tureta. Wata kara muzurun yayi tare da yakushin tilly. Hannunta mai magani a jikin magen duk ta shafe masa shi. Ihu tasa sosai tana kuka ganin abinda tayi na shiga uku shine na karshe maganin. Wani irin kallo taga muzurun yana yi mata tare da biyota. Tuni tilly ta dago jirgin badai maganin yana yi jikin kowacce dabba ba. Tsere suka sa ita da muzurun tana gudu yana binta juni help me please. Ko dago kai baiyi ba yadda yake jin jiri na dibarsa. Tilly dai kitchen ta shiga ta rufo kofa tana numfarfashi. Muzuru kowa yana ta meoww daga bakin kofa yana karta iya karfinsa.
Batul Mamman????
TUN KAFIN AURE????43
Kwanansu hudu da dawowa bayan sunyi sati uku a kasa mai tsarki Hafsi ta taje kano tayi sati biyu. Sun sha hira da ummati ta fada mata halin da take ciki. Gashi dai ta kara kyau ga hutu amma babu nutsuwa a tare da ita. Bikin dake gabanta ne duk yasa ta dan manta da halin da take ciki. Ansha shagali don ummati ita kadai ce mace a gidansu. Duk kayan da ta saka da ma wasu abubuwan Hafsi ce tayi mata. Idan aka tambayeta mijinta kuwa sai tace yayi tafiya ne. Haka suka sha biki aka kai amarya gidanta. Bayan an gama biki Alhaji ya turo mata da kudin jirgi tana zuwa mota na jiranta suka wuce gidan Nafisa.
Ya kusa rabin awa yana jiran Imi a kofar super market din sai ga Tanimu wanda yazo gidansu a matsayin baban Tilly yana bin wata mata da kaya niki niki a baya. Tabbas shine don ga uku ukun bakinsa nan. Rufe motar yayi ya fito ya karasa inda Tanimu yake shirin lodawa matar kaya a booth dinta. Assalam alaikum….ai kafin kace kwabo Tanimu ya zura da gudu don kuwa ko a mafarki baya jin zai manta wannan fuskar. Ita kuwa matar kyawun Junaid duk ya dauke mata hankali kana ganinta kasan tana da aure. Wani fari ta rinka yi masa da ido da kwarkwasa. Hafsi ce ta fado masa, gabansa ya fadi. Ya rasa dalilin da yasa baya iya bude bakinsa ya nemeta ko ma yayi zancenta. Hango Tanimu yayi zai tsallaka titi ya bishi da gudu. Wuyan rigarsa ya kama ya fizgo shi. Tanimu duk ya gama rudewa don bai manta yadda senator yace zai iya sa a batar dasu idan suka yi masa karya. Gwiwoyinsa a kasa ya daga hannu sama yallabai kayi min rai wallahi sani suka yi. Junaid yace meye alakar ka dasu? Ya cigaba da magiya faci nake a tsallaken titin gidansu kuma ina hada su da maza. Dama dai yasan matan banza ne amma dai baiyi tunanin iyayen karya ta kawo ba. Sam baya jindadin rayuwarsa yanzu kullum jinsa yake kamar an kulle shi a cikin kwai. Imi yaji ya taba shi ya Juni meke faruwa ne? Junaid ya kalli Tanimu dake zaune gabansa ya fadawa Imran ko shi waye. Imran ya kira waya ba dadewa ta shiga suna zaune police biyu suka zo yace a tafi da Tanimu har ya fadi inda sauran suke. Yallabai ai ba sai an dake ni ba muje na nuna muku su duk abokai na ne. Keyarsa suka tasa a gaba suka tafi shi kuma Imi ya dawo motar junaid ya zauna. Wai meyasa kaki yarda mu hadu a gidanka ne? Wani zafi jikinsa yake yi yace Imran ina cikin problem sosai, wallahi na tsani rayuwata. Ba abinda ke min dadi….yanzu fa ina shiga gida da naga matar nan babu abinda nake so kamar kusantar ta. Tun ana abu da marmari yanzu ya koma kamar cin tuwo. Ita kuma idan ba kudi ta gani ba ta rinka gara ni kenan. Imran yace ai laifinka ne, tun a wurin bikinka nace ka barni nayi maganinta kaki. Yanzu kuma gaskiya na tuba…junaid yayi yar dariya Allah Ya kara shiryamu. Amin dan uwa…ai in fada maka wata shegiya ce. Au wallahi na tuba fa. Hmmm yarinya na dauko bayan an gama abu sai da nayi kwana biyu bansan inda kaina yake ba saboda na kasa fitsari. Wani mugun ciwo tasa min in takaice maka labari sai da aka yi min aiki a Germany. Abinda ya gabata Allah Ya yafe mana amma ni da mace sai matata insha Allah.
Batul Mamman????
TUN KAFIN AURE????46