UBAYD MALEEK Page 1 to 10

Zakuyi alfahari da mum dinki idan kukaga tazama cikin top 20s Inshallah.
Zamewa tayi zata wuce farhat ta maqalqaleta tana sakin sabon kuka cikin firgici tana Kiran sunanta.
Ganin haka hankalin afia yatashi taga mum din dagaske tafiya zatayi batasan yazatayi ta hanata tafiya ba batada zabin daya wuce takira _NEGES MUHAMMAD KALEEB DELAH_ asalin kakan dad dinta, tsohon NEGES(sarki) Wanda shine mafi soyuwa da shaquwa agurin dad dinsu sbd shine ya riqesa tun yarinyarsa sbd mahaifinsa dashine yakama yazama sarkin yanxu ya rasu sai qaninsa ya hau bayan an aura Masa mahaifiyarsa Wanda haryanxu shine asalin sarkin delah gizah na yanxu mahaifiyarsa Kuma sarauniyar delah gizah hakan yasa kakansa shine mafi kusanci dashi arayuwarsa danma shine ya tsaya Masa aka taka dokar mulki yabari ya auri LAILAH OMAR masoyiyarsa dasukai karatu tare ‘yar asalin ghana dasuka hadu a San Francisco.
Duk da ba wani yabawa KALEEB yayi da LAILAH ba Amma sbd farin cikin ubayd yasashi amincewa yakuma rufe idonsa ya taka doka Dan haka yakeda burin qarawa ubayd maleek Mata Amma ubayd Yana qaidojin rayuwarsa Dan haka abin be yiyuba.
Akwai lokutan da ba’a Kiran KALEEB kaman dad dinta dashima akwai lokacinda ba’a kiransa Amma yau dole zata kirasa sbd shikadaine zai Hana wannan rabuwar sbd iyayen nata Babu Wanda ya tsaya ya saurareta.
Cikin sa’a Kira biyu a na uku aka daga cikin sauri tayi bayanin ita wacece tanason mgn da KALEEB sanin matsayin UBAYD da iyalansa agurin KALEEB yasa aka Kai Masa wayar cikin girmamawa aka miqa Masa ya karba sbd sanin ba’a kawo Masa waya sai me mahimmanci idan bashi yace akawoba.
Tanajin nutsatsiyar muryar Kaleb ta nutsu jikinta na rawa zata fara Masa bayani taji durin motar dad dinta yadawo Wanda yasa gabanta faduwa.
A nutse ya zuro dogayen qafafuwansa dake sanye cikin black brian Atwood brand loafers kafin yafito gabaki dayansa cikin Ralph Lauren brown suit data fiddo da dukkanin hasken fatarsa ta asalin amhara ethopiano.
Kallo daya zakai Masa kasan shine ya haifi AFIA sbd Kamar dasukeyi tayi yawa duk da Kamar yanda bazakace LAILAH ce ta haifi budurwa kamar afia ba haka Kai tsaye Shima bazakace shine ya aje budurwar ‘ya ba sbd kyawun jikinsa da dukda yafara girma bai rabu da geamin ba ma’ana motsa jiki uwa uba ajinsa da asalin kyawunsa tareda izzarsa datake cikin jininsa da har gobe fresh take zamar masa Dan ko ita lailar har gobe duk gayunta da kyanta da Jan ajinta Rena kanta take agabansa shiyasa har gobe take kishin tazama wadda zata tsayu da kanta duniya tasanta da sunanta bada sunan waniba.
Ciki ya nufo qanshinsa na sauya atmosphere din gidan afia na ganin hakan tafara fadawa Kaleb abinda yake faruwa cikin nutsuwa da sauri….
Daidai shigowarsa farhat tasaki Laila tayo kansa da gudu ta fada jikinsa tana sakin sabon kuka Wanda yasashi sake tsuke fuskarsa tsaf wadda tasa Laila dauke Kai daga kallonsa ta nufi qofa zata fita baice Mata qala ba hakama AFIA qafafun lailan dasuka fita ta qurawa ido daidai Kaleb yagama jin komai zaiyi mgn sukaji daddadar muryar dad dinta data ratsa har cikin wayar zuwa kunnen Kaleb yace”
Na datse igiyan aurena dake kanki na sake ki you’re free to go MSS LAILAH OMAR.
Dif afia ta dauke wuta cikin tsananin tashin hankalin jin abinda dad dinta yafada Kamar daga sama taji muryar Kaleb cikin ikonsa na tsohon sarki yace”
Ki dakatar da ita injini.
Muryarta na rawa idanuwanta na dishi dishi tace”
Mum Kaleb yace ki tsaya karki tafi Injishi.
Qin juyowa tayi bayan Sarai taji me afia tace saidai bazata iyaba ta daga qafafunta ta isa bakin mota aka bude Mata tashige suna kallo ta tafiyarta idanuwanta na cikowa da hawaye ta maida tana qoqarin kawarda abinda yake taso Mata saidai takasa Saida ta fashe da qaramin kuka tana rufe fuskarta da hannuwanta har suka fice daga qatuwar harabar gidan.
Murya na rawa cikeda firgici afia tace”
Kaleb Ta fita,ta tafi tabarmu.
Wani numfashi Kaleb ya sauke akaro na farko a tarihin rayuwarsa da wani ya bijire Masa Kai tsaye Kamar agaban idonsa Wanda shikansa ubayd hakan yasa dukkanin wata sauran kaunar Laila yaqarasa fice Masa daga zuciya har abada.
Cikin wata irin murya me babban sauti Kaleb yace”
Ki sanarwa da mahaifinki Ina buqatar ganinsa cikin gaggawa zuwa delah.
#MAMUH#
Share this
[ad_2]