UBAYD MALEEK Page 41 to 50

Qamshin NURUn daya cika gurin yasata dagowa sukai ido biyu kowa yakasa motsawa suka tsurawa juna ido kafin Afia ta taso ahankali ta qaraso gaban NURUn ga mamakinta saitaji afia din ta rumgumeta tana cewa”
Thank God you’re back NURU nayi kewarki.
Mamaki yasata daskarewa batareda tace komaiba ko motsawa.
Afia kuwa tarigada tasan zaman aure ko rayuwar aure tsakanin NURU da dad dinta bamai yiyuwa bane har abada Dan haka Bata sawa ranta damuwaba Dan duk duniya Babu Wadda dad dinta zaiso idan ba mum dintaba Dan haka tasan shima idan har aka koma Babu wani maganar aure dazaibi hakama NURU tana komawa Imran yadawo bazata yarda ba Imran zataso komawa Dan haka ta daure tacire damuwar komai aranta.
##MAMUH#
_ZAFAFA BIYAR_????????????
_Alkiblah–SAFIYYAH HUGUMA_
_Makauniyar qaddara–BILLYN ABDULL_
_Dalaal–MISS XOXO_
_Mabudin zuciya–HAFSAT RANO_
_Ubayd Maleek–MAMUH GEE_
_DUKA KUDIN WANNAN DADADAN BOOKS DIN SUNA KAN FARASHIN NERA 700. WATO KUDIN PAGES KENAN. DOCUMENTS IDAN AN KAMMALA SUMA KUDIN SU DABAN.._
Ɗaya___300
Biyu____400
Uku_____450
Huɗu____500
Biyar_____700
Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki????????
0225878823 Hafsat Kabir Umar GTB
saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)????????
*_08085405215_*
IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN qNUMBER TAREDA SHEDARKU????????
0903 234 5899
*_Mamuhgee 23_*
Abdul-rahman (sudais) is a young boy who’s so passionate about putting the Holy Qur’an into memory. Please help this little boy grow his YouTube channel *ABDUL-RAHMAAN* you got nothing to lose in sha Allah thank you and Jazakumullah khair????????
Do subscribe please
****************
Kodata fito kasa zuwa dakin farhat tayi sbd gabaki daya kafafunta sunyi sanyi toilet dinma tana fitowa ta zube kan gado a kife tana sauke ajiyar zuciya a jejjere Dan Kamar har lokacin tanajin dumi da softness na hannunsa akan mararta.
Bude kofar da akaine yasata Dan juyowa ahankali taga afia ce ta tashi zaune da sauri tana cewa”
Princess tadawo.
Dariya afia tayi tana qarasowa ta aje shopping bags din dake hannunta tace”
Harkinji sauki kenan?
Waskewa NURU tayi da cewa”
Eh” tajawo kayan tana budewa Dan mantar da kanta tunanin abinda yafaru din.
Duk abinda take buqata afian tasiyo Mata ta tashi ta tattara kayan tasa musu su a inda suke aje kowanne tayi sallah tazo ta zauna suna duba wani sabon Francie’s program na likitoci da lawyers tareda engineers a laptop.
Sai la’asar lis tayi wanka ta sauya cikin White three quarter da farar top me laushi ta fita tayi dakin farhat afia tabi bayanta da kallo sbd kusan kome NURU tasaka kyau yake Mata inama ace Imran dinta tafara aura dashine zata more rayuwa sbd yanda yake Sonta Amma dad dinta bazata taba samun so agaresaba har abada sbd mum ce kawai a zuciyarsa.
NURU na shiga dakin farhat ta taddata itama sanye da fararen qananun Kaya tana jiranta har ta fidda kayan drwing din Nan suka baje suka fara.
Sai bayan magriba suka gama
Farhat ta dauka da gudu taje nunawa dadynta ya duba Masu idan sunyi daidai Amma bayanan kusan so uku tana komawa bayanan ta karba wayar NURU ta saka numbernsa dake cikin kanta ta Kira Bai dagaba tukuna ta hakura anan dakin sukai sallarsu suka kunna cartoon suka baje abinsu adakin suna kallo Saida lokacin cin abincinsu na dare yayi suka fito zuwa dining suka zazzauna sukaci suka koshi suka shige anan dakin farhat NURU tayi barci Bata koma nasu ba Dan dama hakan takeyi wani lokacin.
Qarfe goma Sha biyu da mintuna ya nufo dakin farhat din wadda kusan kullum idan haryana gida saiyazo ya dubata da daddare sbd qarancin shekarunta musamman yau dayasan saitayi nemansa sbd zanenta yaduba Mata Dan haka ya nufa dakin Kai tsaye ya bude yashigo tareda rufe kofar har zai kunna wuta gudun kada ya tadata yasa Bai kunna dinbaya qaraso bakin gadonta tareda zaunawa bakin gadon ya Kai hannu yakunna bedside lamp kadan haske ya ‘dan bayyana yana waiwayowa yaganta itace kwance abakin gadon farhat na quryar gadon ya sauke sahirtaccen numfashi Yana kallon kayan baccin jikinsu itadai farhat komai iri daya riga da guntun wando royal blue bacci suke duk su duka hankali kwance.
Dan qara rage hasken wutar yayi sbd kaman hasken zai damesu yajanyo musu bargo ya lullubesu ko Gama janye hannunsa baiyiba NURU tasa kada ta yaye lullubin Dan dama Bata cikason rufaba cikin bacci.
Fuskarta yayiwa kallon minti biyu ya dauke Kai tareda Miqewa ya nufi hanyar ficewa harya taba kofa zai fita saiya tsaya tareda Dan rufe ido ya bude tunanin Dole wani daga cikin masu aiki zasu tadasu da asuba yasashi dawowa yasake Jan bargon ya rufa Mata saidai Yana dauke hannu takai hannu cikin baccin zata yaye yakai hannu zai danne hannuwansu suka sauka atareda nashi akan nata Wanda Kai tsaye yasata bude manyan idanuwanta dake cikeda bacci ta dagosu.
Kasa yadda tayi da abinda tagani tasan mafarkine kawai take Dan haka saita juya hannunta tasanya tafin hannunta tana sake tattaba hannunsa Dan Jin tsananin taushinsu ta lumshe ido baccinta na fizgarta har lokacin tafin hannuwansu na hade.
Dan sarquwa yayi da yawu kadan yasaki Dan qaramin tari Mara dogon sauti Wanda yasata bude idanuwanta duka da qarfi tareda zaburowa daidai motsawar farhat sai yayi saurin dafeta Takoma kwance sbd kada ta tada farhat ga farhat din da surutu zata iya jeho wani zance akan hakan.
Kallonsa takeyi face to face akaro na farko a rayuwarta zuciyarta na harbawa a tsorace yayi Mata kallo daya da idanuwansa da yau suka shiga daidai cikin nata take taji jikinta ya sake gabaki daya sai kawai ta sake a jikinsa ya hadiye wani mugun yawu a maqogaransa Wanda yasata kallon moqoshinsa sbd yanda Adams apple dinsa yayi sama yayi qasa ta maqoshin nasa.
Miqewa yayi tsaye yaraba jikinsu sbd asthma dinsa dayakejin kaman zata tashi ya juya ya fice adakin yabarta kwance Bata iya ko daga hannunta sbd mutuwar jiki saidai ido databisa dashi cikin wani irin yanayi na kunyane ko na menene ta Bata saniba illa dai Abu daya data tabbatar ayau shine kyawun da Allah yabasa Wanda ko rabinsa ‘yayansa Basu daukoba cikin yama manyanta kenan…daganan baccinta ya watse har kusan asuba Bata samu baccinba gashi gobe tanada zuwa makaranta Dole ta rintse idanuwanta Dan tayi baccin Kona Dole ne.
Qarfe shida ta farka ta sauko gado tashiga toilet tayo alwala ta tada farhat sukai sallah ta fice.
Tana shiga dakinsu ta tada afia sallah kafin ta fito ita ta fice zuwa kitchen aikin breakfast.
Tana gamawa ta jere a dining takoma daki tayi wanka tashirya cikin black riga da wando ta doro doguwar kimono fara akai ta daura black scarf me kauri tafito sukayi breakfast itadasu afia da farhat suna gamawa kowa yaje ya dauko jakarsa suka fito.
Da Mr Omar suka fara cin Karo tsaye jikin motar dazasu tafi da ita makaranta tareda sabon driver cikin girmamawa yana Dan taudasa harshe cikin sakin fuska yace”
Gud morning Mrs MALEEK.
Gud morning princess.
Kallonsa AFIA tayi Jin abinda yace itadai NURU sidadawa tayi ta wuce Jin kalmar tamata girma ta shige mota tana kunna wayarta da Imran yahanata sakat da kira saigashi tana kunnawar kiransa na shigowa ta dannata silent tana Dan kallon gefen Mr Omar dake tsaye idanuwansa kuwa quru akan wayarta tana juyowa ya dauke Kai Yana cewa”