UBAYD MALEEK Page 41 to 50

Cikin iko da muryarta me taushi ta katse afia da cewa”
Zandawo wa MALEEK Amma ba yanxuba haryanxu akwai abubuwan dake gabana,afia kinada naci akan zance daya koyaushe bayan nace Miki zandawo Amma ba yanzu ba idan akwai abinda yafi cancanta yanzu dakiyi shine ki raba maleek da yarinyar daya aura Kuma tabar gidan gabaki daya sbd matuqar tananan koya saketa bazan iya dawowaba infact inason sauyin gida tunda harta zauna a wannan gidan koba komai idan haryanzu kunason aikinta zaku iya zama da ita acan Amma dai Ni Kam a sauyamin gida musamman farhat da lalurorinta sunyi yawa yau ciwo gobe lafiya….
Cikin mamaki,takaici da baqin ciki daya Gama kashe afia tabude Baki tace”
Mum shin akan abindake gabanki kika watsar da ‘yayanki musamman Yar qanqanuwa Kamar farhat harkina cewa lalurarta yayi yawa?
Ciwone fa atareda ita Wanda Allah ne ya Dora Mata ba ita tadorawa kantaba, badan NURU ba da yanzu dukkanin mu munshiga wani hali and now kina cewa akoreta?a koreta kokuma mubita can mu zauna kenan kin yafemu?
Mum inasonku keda dad duka saidai I’m sorry to say this to you yau nafi son dad ayanzu fiyedake da duk wani tunaninki Dan kuwa koba komai shi yasan haqqinmu ‘yayansa akanshi Yana bamu Dan haka mum tunda haryanxu Bakida mijinki da yayanki aranki inaga zaifi idan na karbi hakan na runguma nakuma amince Dan kuwa na tabbatarda dana amince da hakan tuntuni da bazan cutatu hakaba,
Na lalata rayuwar mutum uku sbd hope din Zaki dawo saidai Ashe mafarkinane kawai….hawayen baqin ciki me tsanani ne suka gangaro Mata ta kashe wayar da qarfi tareda wurgi da ita sbd Jin mum din na cewa”
Afia ke yarinyace haryanxu bazaki ganeba Dan haka please don’t call again idan Baki shirya daukan abubuwan dazan fada mikiba.
Kuka me qarfi ta sake tareda daukar wayar taqara kwadawa da qasa tana qoqarin sulalewa qasa cikin kuka taji hannuwan dad dinta duka biyu ya riqota Yana kallon kyakkyawar fuskarta ya girgiza Mata Kai ahankali ya bude Baki cikin muryarsa me nutsuwa da dadin sauti yace”
AFIA MALEEK karki manta ke ‘yar maleek ce jikar kaleeb our beautiful and brave lioness and you know wat thats means right princess??
Da jajayen idanuwanta ta dago ta kallesa zatayi mgn yace”
Ya Isa haka banason Jin komai all I want from you shine ki maida hankali akan karatunki ki Gina career dinki da kanki.
Sakinta yayi tareda juyawa zai fice saikuma ya dakata batareda ya juyoba ya bude Baki wannan karon cikin cikakken iko da bada umarni cikin sautinsa me daidaita nutsuwarta yace”
Wannan shine Karo na karshe daza’a Kuma maganarta acikin gidan Nan.
Karo na karshe.
Gyada Kai tayi tana sawa ranta batada uwa araye daga yau itama sbd dukkanin inda take tunanin mum dinta yau ta kai limit Dan Bata taba daukar uwa zata iya yafe har yayanta ba datake ikirarin Bata buqatar farhat sbd tacika ciwo, wannan kalmar ta rusa duk wata sauran hope datake dashi akan mahaifiyarsu.
Fitowa tayi tana shigowa Palo ta tararda farhat zaune apalon tana kallon cartoon cikin walwala abinta tana ganin afia din tasake murmushin farin cikin ganinta tana cewa”
Afia bakije makaranta ba kina inane tun dazu?
Aunt NURU ta tafi ta dauka kintafine.
Kasa magana afia tayi tausayin qanwarta me tsanani na shigarta har batasan sanda hawaye suka ciko Mata idoba suna gangarowa ta qaraso ta zauna gefen farhat din tareda rungumeta jikinta tanajin tsananin so da kaunar yarinyar tareda tausayinta,tayaya uwa zatace Bata buqatar ‘danta sbd wani ciwo na harbawa da Allah ya sako Masa,
Ta Yaya mum dinsu zatace Bata buqatar farhat?
Kamar farhat din tasani saita lafe jikin afian batace komaiba hawayen afian Bata sauka kan jikinta sun Jima ahaka kafin Afia ta zame tareda Miqewa yayi daki ta rufe kanta tana wani irin kuka me ciwo da baqin cikin rayuwa,
Babu abinda Allah be basuba najin dadin duniya sai rashin uwa tagari da soyayyar uwa da Basu samuba kwata kwata,
Suna cikin ni’imar dukiya me yawa,
Mulki na sarauta me girma,uba nagari da soyayyarsa,ilimi na Boko Dana addini,kyawun jiki Dana fuska taredana zuciya daidai gwargwado Amma uwa Basu samu komai daga garetaba bayan dawainiyar daukan ciki da haihuwa duk cikinsu Babu Wanda yayi shekara yanashan nononta take zaresu tabarwa masu aikisu sune komai nasu tayaya zasu qarar da soyayyar uwa.
Sai yamma NURU tadawo tun apalo ta sake tabbatarda farhat ta warware Dan da gudu ta tarbeta suka fada kan kujera cikin murna take bawa NURU labarin yau dad yafita da ita Amma Basu dadeba suka dawo.
Miqewa NURU tayi tana cewa”
Iyye yau Daddy ya kyauta Mana sweetie taje yawon datake so.
Duk da haka fa aunt NURU alqawarin mu Yananan fa dakikace Zaki kaini yawo har wani qasa daban.
Hanyar daki suka nufa tana cewa”
Eh banmantaba saina gama karatu idan zanje Vegas attaching papers Dina na Gina career Dina dake zanje Inshallah sweetie.
Tsalle tasaki tana cewa”
Yes yes my Lewa
Suna shiga daki afia na zaune tayi wanka sanyeda gajeran wando da shimi tana aiki da laptop tana ganinsu ta sake fuska tana cewa NURU”
Welcome baby.
Thank you princess”NURU tace tana zare kayan jikinta tana fadawa Afia zancen dasuke da farhat suna dariya.
Wanka tayi tazo yayi sallah ta Sanya qananun kayan Shan iska itama tasha coke daya ta Dan kwanta sbd ta Dan gaji Kuma batajin yunwa Dan taji snacks a wani coffee shop.
Tana bacci wayarta tadauki ringing afia dake zaune ta kalli wayar saitaga sunan padima.
Murmushi tasaki sbd tasan padima abakin NURU Amma Basu taba gaisawaba Dan haka ta dauka Kai tsaye tareda cewa”
Assalm alaikm padima ānichī gini inidēti neshi? (ya kike ya gida/hw are you doing and family).
Tsit padima data Kira da Dan qungun kukanta tayi Jin muryar afia wadda takeda tabbacin itace ‘yar maleek da ake fada Dan haka saita Dan saita murya cikin girmamawa da kulawa da sautin muryarta daya tabbatarda tayi kuka tace”
Lafiya kalau alhmdlh li’iliti.
Ya karatu da hidima?
Murmushi me sauti afia tayi tace”
Ba hidima saidai karatu shima munatayi inshallah munkusa gamawa, NURU na bacci yanzu saidai ko Zaki sake Kira anjima kokuma idan ta tashi saina fada Mata ok?
Dan kame kame padiman tafara tana cewa”
Eh baza’a tada ita bane yanzu da magana zamuyi me mahimmanci ne?
Kai tsaye afia tace”
Aa baza’a tashetaba yanzu dai lokacinda ta tashi dakanta kokin manta Matar maleek ce?
Koma yayane bazan tashetaba saita tashi da kanta matuqar ba lokacin sallah bane kawai ya isa yasa na tasheta sai idan dad ne dakansa yake nemanta which kuma is not possible for now dai.
Wani Abu padima taji yataso Mata kamar zata ashararo ashar ta danne tana cewa” Sabala ibilis cikin ranta.
Wato NURU har matsayin nata yafara kaiwa haka tun wuri.
Jin shiru yasa afia cewa”
Ko da akwai matsale ne a gida?
Kifadamun zanyi maganan da ita idan ta tashi.
Shiyafi komai sauki ‘yar maleek padima tafada cikin ranta tareda sauke wani wahalallen numfashi tana karye murya zuwa rawa rawar son kuka tace”
Dama nafada Mata maganar rashin lafiyan danake fama dashine abin yafara tsanani anyi magani anan gida baiyiba shine tace zata kaini Inga likita anan ko za’a dace.
Da mamaki a bayyane afia tace”
Anan Kuma?
Tun yaushe ne ciwon?
Tsawon shekara”padima tafada tana hawaye.
Gyara zama afia tayi tana cewa”