UBAYD MALEEK Page 91 to 100 (The End)

Murmushi yasake Ya kalli afian yace”
Thank you princess Afia.
Da ihu farhat tayi kan NURUn tana cewa”
My aunt zata haifamuna baby me kyau kamanta.
Murmushi NURU tasake tana kissing kumatun farhat din.
Tun daga dining din Babu Wanda yakuma ganin NURU sai washe gari da safe dasuka fito cin abinci sai alokacin afia tabada shawaran NURUn tafara ganin likita musamman akan jirin aikuwa ba Bata lokaci Mr Omar dakejin kaman ya taka kan jariri yakira Dr Damien yazo har gida ya duba NURUn daganan yafara zuwa dubata akai akai.
Lokacinda su abal dinta suka samu labarin cikin hadda sadaka ammynta tayi meryam kuwa tuni tafara takura tanason zuwa gurin NURUn saigashi kuwa maleek da kansa yasa jekadi taje har Delah ta daukota dama Kuma itama jekadin tana Shirin zuwa ne harsai NURUn ta haihu.
Zuwan jekadi da meryam da sati biyu maleek ya dauketa suka tafi _Maldives_ inda sukai zamansu acan suna hutawa Saida cikin yashiga wata na budu kafin suka dawo lokacin anfara maganar auren afia Imran Wanda tun kafin suyi tafiya dad din Imran din ya nemesa yayi magana da afia tace da amincewarta take yace ya Basu aka tsaida Rana.
Imran yadawo Paris gabaki daya da lailah sbd gidansa a Nan Paris yake bazai zauna gidan mahaifin matarsa ba ba girma bane Dan Haka murna kan murna agurinsu NURUn da afian sbd bazasuyi nesa da juna ba take aka hau Shirin biki gadan gadan musamman uwar amarya lailah da ba laifi yanzu ta warke harta fara komawa ayyukanta zata fara daga farko Dan ma a qarqashin kamfanin dad din Imran din take aiki.
Sosai akai shagali a gizah na auren afia din Wanda hatta iyayen NURU sun halarto tareda kaleeb sosai tayi farin cikin ganin iyayenta Suma sunyi farin cikin ganinta musamman cikinta daya fara tsufa a gizah kowa yasan MALEEK na gaf da samun magaji kila suke fata.
Padima dai ba laifi tananan sama sama wani lokacin kalau wani lokacin Kuma abin ya Dan juye ahaka aka gama bikin suka tattara suka dawo Paris afia ta tare a babban gidan mijinta Wanda mum dinta take sashe guda na musamman da Imran din ya ware Mata.
Ranarda afia tacika wata hudu cif da aure ranar nakuda ta tasowa NURU
Maleek ya tattara mulkin da sarautar ya ajiye suka dunguma zuwa asibiti sbd ganin gidan zata wahala bazai iya jure ganin hakan ba
Saigashi cikin ikon Allah suna Isa ta haifi qatoton jaririnta me Kama da farhat sak.
Koda maleek ya karbi Dan wata hamdala yasaki Yana godewa ubangiji yayi Masa huduba da sunan Mr Omar tareda yiwa Mr Omar wata gagarumar kyautar datasaka Mr Omar din rungumesa Yana hawayen godiya duk dai yatara tarin dukiya me yawa a qarqashin maleek din Amma sai bazai iya dainawa maleek din aiki ba sbd sunzama kaman jini.
Acikin motarsu ta dawowa gida duk yabita ya lashe da kisses itada baby Omar Wanda hotonsa tuni yafara yaduwa a duniya Matar UBAYD MALEEK me gizah ta haifar Masa baby boy.
Daqyar ya suka iya raba gurin kwanciya sbd jekadi data Dan sako NURUn agaba har aka samu sukai 50days daga Nan delah suka tafi tayi sati biyu gurin iyayenta daganan suka dawo gizah tayi kwana biyar kafin tadawo Paris su afia sukazo aka wuni gidan suna Yan kus kus dinsu na kayan datazo dasu suka raba
Washe garin ranar maleek ya dauketa suka tafiyarsu _Santorini_ sbd wata sabuwar duniyar da NURUn ta jefasa a Daren jiyan inda sukai wata daya kafin suka dawo
Saidai Koda ta dawo da sabon ciki ajikinta wanda yazo Mata da Dan laulayi da son jiki Haka shima duk ya shirirce gurin tattalinta da jinya sbd koyaushe tana lafe ajikinsa karshe dai Mr Omar Dole ya rungumi wasu ayyukan da kansa yakeyi a office.
##MAMUH#
*ALHAMDULILLAH YA ALLAH*
*MUNZO QARSHEN WANNAN LABARIN ME SUNA UBAYD MALEEK WANDA NAKE FATAN KURA KUREN CIKI DA ABUBUWAN DANAYI BA DAIDAIBA ACIKI ALLAH YA YAFEMABA GABAKI DAYA HAKAMA KURAKURAI IRIN NA MANTUWA DA TYPING ERROR DUK INA FATAN ZAKUMIN UZURI HAKAMA WAINDA ZASUGA BAI KAI MUSU INDA SUKESO BA SUYI HAKURI AMMA DAI KYAN L
LABARI AGAMASHI ANA MARMARINSA BASAI MUNKAI INDA ZAKUJI YA GUNDUREKU BA NIMA BASAI NAKAI INDA RUBUTASABA ZAI GUNDURENI DAN HAKA INA FATAN NUSHANDIN YAYI DAIDAI YANDA ZA’A DADE ANA TUNAWA*
*NAGODE SOSAI SOSAI DA KAUNA DA KUKA NUNAWA LABARIN KUMA INSHALLAH INA MANA FATAN HADEWA A GABA DA LABARIN DAZAIFI UBAYD DA NURU DADI* ????????
*NAGODE*
*_MAMUHGEE_* ????
[ad_2]