UNCLE DATTI Page 51 to 60 (The End)

” Ashe ban san baki da haunkali ba sai yau, ko kad’an baki san ciwon kanki ba….., idan har ma Datti kike nema a ba shi Auren Nana ki sani abunda kike nema ba zaki samu ba sakarai kawai shashasha, ya kare maganar tare da jan tsaki mai k’arfi, har ga Allah ranshi ya matuk’ar baci sosai.
Jikin ta ne yayi matuk’ar sanyi sosai cikin dakiyar zuciya tace” yi hakuri baba ba wai dan na b’ata muku bane ya sa na fad’a hakan, duba nayi da yanda matsalar Datti yake yanzu baba idan ba’a aura mishi ita ba wa kuke tunanin za’a zai aura yayi zaman aure da ita wacce zai samu nutsuwa da kwanciyar a tattare da ita?
“Babaaaaa” ta fad’a cikin sanyin murya tare da jan sunan kana ta cigaba da cewa” ba laifin shi kad’ai zaku duba ba lalurar ce kuma na tabbata wasu abubuwan ba yin kanshi bane……., ya yi dan nemar ma kanshi mafita yake yi”.
“Murmushin yake baba babba yayi” Aina lalura bata ce ayi zalunci ba, Dattin nan fa kema ya cutar da ke tunda yayi taraiya da y’ar uwar ki kuma a cikin gidan ki, bayan haka idan aka aura mishi Nana ba’a mata adalci ba”.
“Ehhh haka ne amma ban k’i naku ba amma mafita d’aya ne shine ayi k’ok’arin samo shi daga cikin matsalar da yake ciki idan aka yi hakan hankalin mu zai kwanta shima zai koma kamar ko wani namiji magidanci”.
” Shi kuma Fu’ad d’in da ya taimaka mata yaya kike son ayi da shi?”, sannan kuma idan aka yi mishi haka kina tunanin an kyauta mishi? cewar Alhaji kenan yayin da yake gyara zama.
“Rashin kyautawa ba’a mishi ba amma wani bukatan yana danne wani bukatan, alfarma ne nake nema, kun min auren had’i da Datti kuna sane da matsalar shi amma haka nayi muku biyayya na zauna da shi bil hakki, ina so ku min alfarmar biyayyar da nayi muku ku aura mishi Nana………, baba nima fa kun cutar da ni da kuka had’a ni aure da wanda ba lafiyayyen namiji ba kuma na zauna da shi…….., idan har nayi muku biyayyar nan ya kamata ku dubi lamarina……..mafita ne nake samar mana baki d’aya ta yanda kowa ba zai cutu ba”.
Shiru suka yi duk jikin su yayi sanyi, baba karami kam rasa abun fad’a yayi cuz bai san ta yanda zai fara ba.
” Shikenan jeki Aina’u”, ta mik’e tayi musu sallama ta tafi.
Bayan fitan ta suka ci gaba da tattaunawa a tsakanin su kowa na kawo nashi dalilai da hujjoji daga k’arshe suka yanke hukuncin su tuntub’e Nana da maganar su ji ta bakin ta.
B’angaren Aina bayan ta bar wajen main patlour ta nufa ta tarar da Nana na zaune a parlour ta jingina kanta da jikin kujerar tanta na kallon sama ta lula duniyar tunani.
Kafad’an ta Aina ta dafa a sanyaye ta k’afa mata ido har ranta tana jin tausayin Nana a ranta” rau-rau tayi da fuska kamar zata yi kuka”Aunty don Allah ki daina zargina wallahi ban yi abunda kuke tsammani ba hasalima ma raping d’ina yayi niyar yi fa”.
“Libs Aina ta cije tana mai jin zafi a ranta, she have no choice than ta sadauk’ar ma y’ar uwar ta mijin ta ko da kuwa zai zama ajalin ta tunda Uncle Datti jikin Nana kad’ai yake so yayi rayuwa da ita”.
” Hakan ne kad’ai zai saka ta cece Datti da Nana daga sharrin fad’awa halaka a k’aro na biyu, sanin kanta ne ko da ace Fu’ad ya aure Nana babu abunda zai canja zani domin hakan ba zai hana Datti ya fasa neman Nanar ba, kenan rayuwar ta yana cikin hatsari babba”.
Idanuwan ta ne suka fara kad’aya suna neman turning read, tana breathing kamar zai yanke tace” Na san abunda zan fad’a zai miki zafi ko kiyi tunanin bana tausaya miki…..wallahi Nana ina matuk’ar tausayin ki hasalima shi ya sa kika ta nayi hakan……..shiru tayi tana kallon Nana cike da fargabar abunda zata fad’a mata, sai taji gaban ta ya fad’i ta hau jujjuyar maganar Auntyn tata a kasan zuciyar ta.
“Nana ki amince ki aure Datti shine kad’ai abunda zai saka na daina zargin ki, idan baki min hakan ba baki da wani hujjan da zaki kare kanki daga zargin da nake miki, bayan haka idan kika bijire ma bukatata zan fad’awa wa su baba su san cewa kina kai kanki ma Datti kuna aikata abunda kuka saba………., saurin toshe kunnuwan ta tayi tare da runtse idanuwan ta cuz bata jin zata iya jure maganganun ta.
Mamaki ne ya cika ta karara, a matsayin ta na y’ar uwar ta bata tausayin ta take cewa ta aure mijin ta……….., ko ta manta ne har yanzu da auren Datti a kanta………., ko tafi son ta faranta ma Dattin fiye da ranta………., a gaskiya Aunty Aina ta jefa ta a tsananin rud’ewa ta jefa ta a ramin da baza ta iya kubuta ba……..yaya take son tayi da Fu’ad wanda yake sonta da gaskiya kuma itama ta koya ma zuciyan ta son shi”.
” A wani matsayi zata karb’e bukatar y’ar uwar ta?
Tana cikin tunanin taji muryar Aina tana magana da kakkausan murya” Idan kika ki bin abunda da na fad’a miki kin san me? ta ja kwafa ta girgiza kai kana ta d’ora da cewa”zumuncin mu da ke har abada babu ita……zan saka almakaci na datse komai.
Da sauri nana ta kafa mata ido tana ruwan hawaye……ganin haka Aina ta sa kai ta bar wajen cikin sauri ta nufi d’akin ta ta fad’a saman wani uncontrollable kuka ya kwace mata ta hau rerawa.
“Anya idan ta had’a Datti da Nana tayi ma kanta adalci kenan? Anya zata iya rayuwa babu Datti? Matsanancin kuka ta fashe da shi tana cewa” why!!! why!!!!! me yasa baka son jikina sai na yar’uwata after all zaman da muka d’eba da kai kana cikin lalura nake rokar maka Allah ya yaye maka ita mu more zaman auren mu?
Ashe dama har abada jikin ka ba zai zama mamora a gare ni ba?
*”JIKIN KA NAKE SO KAI KUMA JIKIN TA KAKE SO?”* ashe ba zan tab’a mallakar jikin ka ba?
Haka ta ci gaba da kukan nata tana surutai kamar zautacciya ita kad’ai.
B’angaren Fu’ad kuwa duk yanda ya so ya cire zargin Nana a zuciyan shi abu yaci tura yana tsananin kishin ta fiye da tsammani, idan ya ganta ko a hanya sai abun ya fad’o mishi a rai yayi ta jin haushin ta gani yake ita ta kaimi kanta dama tuni suke shirya plan d’in su suyi ta abubuwan su.
Cikin lokaci kankani har ya fara rama watarana suna zaune da Kamal yace” me yake faruwa ne two days ina ganin ka cikin damuwa baka da aiki sai na tunanin……kamar wanda aka ce za’a raba ka da amanar ka?
“Doguwar ajiyar zuciya ya ja ya sauke a hankali kana ya d’ago jajayen idanuwan shi ya sauke kan Kamal da shi d’in ma shi yake kallo” Wallahi Kamal auren nan duk ya fitan min a rai…….idan na tuna da abunda Nana tayi min sai na ji na tsane ta……..ka san kuwa Nana Datti take so ba ni ba?
“Whattttt ka san abunda kake fad’a kuwa? Na tabbata kai take so ba shi ba domin kuwa fuskar ta kad’a mutum zai kalla ya gano hakan”.
” Hmmmmm”, ya fad’a cikin kunan rai tare da fuzar da iska mai zafi ya dora da cewa” da nayi tsammanin hakan amma yanzu na gano cewa ba ni d’in take so ba, hasalima taumakon da nake yi mata ne shi yasa take kokarin b’oye son da take mishi dan ta kyautata min.
“Bana tunanin haka Fu’ad domin kuwa na san halin ku d’aya da Nana baku iya b’oye so ba sannan baku iya kin abu ba idan kun tashi yi da zuciyan ku kuke yi”.