UNCLE DATTI 1-END

UNCLE DATTI Page 51 to 60 (The End)

        Idoooo Usman ya waro yana mamakin jarabar Datti” me kake tunanin zata maka idan ta zo? Idan kana tunanin cewa zata baka abunda kake so ne ka sani fa da da yanzu ba d’aya bane, yanzu ta san ciwon kanta ba irin da da kake jujjuya ta bane”.

           “Kuka ya fashe da shi” don Allah Usman ka neman min ita……anya kuwa kasan abunda yake damuna kuwa…….., 

         “Auren ta kayi da sai duk sanda kake so ka same ta zaka samu….ko ka manta an ba ma Fu’ad ita wallahi kayi ma kanka kiyamul laili ka hak’ura da bakin kuddurin ka……….ni shawata ta d’aya da kai ka fad’a ma su Alhaji abunda ya faru tsananin ka da Nana idan ba haka ba kai ka jiyo…….

          Fuuuuu ya fice daga d’akin ya basu wuri         

           B’angare  Nana kuwa haka taci gaba da zama tana rainon cikin ta da kuma baby d’in ta…….har ranta bata son maganar auren amma ganin yanda su baba suka dage mata ya sa ta hak’ura ta mik’a wa sarautar Allah ido…….,

         Tsohuwa kammm duk abun duniya ya dame ta kamar tafi kowa jin zafin abunda ya faru….a duk sanda ta d’aga ido ta ga rusheshen cikin Nana ta rushe da kuka tace” hege d’an hegiya…….,shikenan duk ta ishe kowa da kuka Nana tana jin ta ta tab’e a ranta tace” auuu ashe kina da bakin kuka”.

         Ummi ma samm basa son cikin nan, gashi Nana ta ishe su da jarabar ci sai narkar abinci take yi tana ciyar musu da shege a gida……, idan aka yi abinci ita take cinye kusan rabin shi……., suna kallo abu yafi k’arfin su ba daman hanawa.

       Da Nana ta fahimci irin kiyayyar da suke nuna ma cikin sai ta bare dukan su sun hallara a parlourn kafin nan ta fito tana tura cikin da kyar bata sako hijabi balle ya boye cikin haka zata zauna tana matse fuska irin na masu ciki idan suka ganta sai takaici ya d’ebe su musamman Ummi da Umma sai kaga sun fara wastewa da d’add’aya sun bar parlourn su barta daga ita sai tsohuwa………

        Ita kam kasa hakuri take ta yab’a ma Nana magana” anyi asara an jawo ma mutane abun kunya……., Nana ta sakar mata hararar tare da maida mata da martani” kuma dole a karb’a a matsayin tattab’a kunne ba”, tsohuwa ta rushe da kuka tana sharar kwalla tana shine ma Nana a ranta……..ta bud’e k’afa wani k’ato ya d’ora mata ciki gashi sun an barsu da rainon shege.

          Wata rana Nana na zaune a parlour ita da tsohuwa suna gatsa ma juna magana Fu’ad ya shigo da saurin shi” hearty zo muje ki rak’a ni wani waje………..

        “Cikin ta ta turo waje tana yamutsa fuska” Allah ya Fu’ad na gaji cikin nan na wahalar dani da yawa.

         Tsohuwa na kallon ta ta kasan ido tana so ta tanka mata, sanin kanta idan ta fad’a d’aya Nana zata aika mata da biyu shi yasa tayi shiru tana zumb’uro baki, ji take kamar ta mata wawan shakar da zaisa ta haifo abunda ke cikin ta murd’e wuyan ya mutu kowa ya huta.

        Muryar Fu’ad da taji ne ya dawo da ita cikin hayyacin shi yana cewa  “Kaiiii ban son raki ki taso muje”.

       Nana ta mik’e tayi gaban tsohuwa tace” please tsohuwa ki taimaka min da hijabi a d’akina kin san hawan steer case d’in nan wahala yake bani bana iya d’aga k’afafuwana ciwo suke min.

         Maganar sai ya d’ad’a kular da ita tace” jarrrrr uba a hakan kika iya ware mishi k’afa sama ya dinga danna miki kina karba har kika samo wannan kaddararren abun”. 

         “Kunyar maganar taji sosai ta jiyo tana kallon Fu’ad taga shima ita yake kallo….., taga alamar b’acin rai a tattare da shi dole yaji kishi mana tunda yana son ta…even though ya san cewa da gayya tayi maganar amma bai kamata tayi a gaban shi ba…….., ko d’azu ma da yake mata magana daurewa kawai yake yi.

           Fita yayi da da sauri zuciyar shi nayi mishi zafi……ganin haka tayi d’auki ta d’auko hijabi  ta bi bayan shi da sauri.

        A mota ta tarar da shi yana zaman jiran ta har ta shiga ta zauna baice mata komai ba ya ja motan suka bar gidan.

        Gidan da Amintacce ya kaita shine suka nufa suna isowa yace ta jira shi a parlourn yana zuwa ya haura d’akin tsohuwa suna magana wanda ni kaina ban san me suke tattaunawa ba………..tana parlour tana jiran ya fito taji shiru sai taji tana son ta shiga d’akin da ta yi rayuwa a ciki……..mik’ewa tayi da sauri ta shige ta maida k’ofa ta hau bin ko ina da kallo tana imagining irin life d’in da ta yi a gidan da yanda take rainon cikin ta……., har ranar da Amintacce wato Fu’ad yake zuwar mata a duhu…….., drawer d’inta ta nufa ta d’auko takardun yake rubuto mata notes a ciki ta cusa a cikin jakar ta ta fito parlour da sauri ta koma ta zauna.

        Ba wani dad’ewa tayi da zaman ba sai ga shi ya fito yace ta tashi su tafi, babu musu ta mik’e suka fice daga gidan.

         Gida suka koma ta shige d’akin ta ta cire hijabinta da jakarta ta ajiye a gefe, kana ta maida jakan tana maida numfashi………, takardun ta d’auko ta warware ta fara karantawa kamar haka……..” Na san zaki yi makin dalilin da ganin ki a cikin wannan gida…..kawo ki na sa aka yi domin cimma wani manufa…….dalilin da ya sa ban bayyana a gare ki ba shine a duk lokacin da na ganki kina kina kuka ko nayi ido ke sai naji kin bani tausayi kin k’arya min zuciya har na fara tunanin janye kuddurina a kan ki”.

         Dam dam dammm buguwar zuciyan ta ya yayi dai-dai da lokacin da ta kai k’arshen rubutun ta mayar ta ajiye” maganar ta mugun d’aure mata kai sosai ta kasa fahimtar komai da ke cikin takardar……..d’auko d’aya tayi ta bud’e ta fara karantawa……hotunane na guda uku aka nannad’e a cikin takardar tare da yin rubutu kamar haka” na san baki san dalilin kawo ki cikin gidan nan ba da dalilin da yanda aka yi aka d’auko ba……, shiri ne na musamman domin na cimma burina akan ki”, hotunan ta bud’e taga itace a lokacin da fad’i yashe a kasa a pakin titi, sai taji gaban ta na tsananta bugu…….., sai taji tsoro ya kama ta ta mayar ta ajiye…….,shiri wani irin shiri…..komai nashi managar buri duk abunda zai fad’a sai ya saka k’almar.

        “Takarda na uku ta d’auko ta karanta” hankalin kowa ya tashi a gida kema na san hankalin ki a tashe yake amma ki kwantar da hankalin ki duka biyu nake so nayi na cimma burina.

        Kici gaba da rainon cikin ki da shi zan yi amfani na cimma buri na”, tana gama karanta shi ta mayar ta rufe.

         Takar na hud’u ta bud’e ta fara karantawa” naji yanda kike rayuwa a cikin gidan nan karki damu na kusa na bayyana a gare ki…….., kici gaba da mu’amalar ki har zuwa ranar da burina zai cika………

       Tana bud’e takardar k’arshe taga an rubuto” mission “.

        Menene mission d’in ita dai Fu’ad ya d’aure mata kai sosai, daren ranar ta kwana tana tunanin maganaganun da ta gani a jikin takardar ne, was he gari da abun ya dame ta ta same shi a parlour tace ya gaya mata gaskiyar ma’anar burin da yake son cimmawa a kanta.

            “Cije libs d’in shi yayi yace” barina a kan ki shine na baki tsaro wato na ceto ki a hannun Datti, 

          “Nana na san halin iyayen mu ko da ace kin je musu gida cikin jini a lokacin baza su yarda da ke ba hasali ma tsoro nake jiye miki kar suyi zargin cewa bin maza kike yi, cuz a lokacin kinyi iya k’okarin ki ki fad’a musu gaskiya suka yi kunnen uwar shegu………., musamman Aina da son mijin ta ya gama rufe mata ido shine na sa aboki na Kamal ya d’auko ki ya kawo ki gidan, gida na ne babu wanda ya san mallakina ne, na Samar miki Inna a matsayin wacce zata dinga kula da ke tana d’ebe miki k’ewa.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Leave a Reply

Back to top button