Zee Baby Book 1 Page 5

*Mun dawo cikin labari*
✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨✨
Taku yake cike da izza tamkar ba mutum ya rumgumo a hannusa ba fuskarnan tam ahade mutane cikin Airport din sai kallonsu suke cike da shawa parking spece ya nufa tun daga nesa naga ya danna rimote wata wulwuleliyar motar baka sudik k’irar land range Rover évoque 2020 ta bude bayan motar ya cillata ya rufo ya shiga mazaunin direba yai mata key yaja da karfin gaske ya fice yana hawa kan titi ya kunna sigari yana busa baki da hanci hospital Nasarawa ya nufa ya dauki wayarsa ya danna wata number bugo biyu aka daga saita nutsuwarsa, yayi ” Asallama Dr Yakub ykk” gud kana hospital ne ganinan saman hanya zan duba wata koran makkah ok bey sai nazo kitt ya tsinke Kiran ya maida hankalinsa kan driving har ya isa asibiti parking spèce ya shiga da motar fitowa yayi ya bude bayan motar ya ciccibeta ya rufe motarsa anutse yayi ciki da ita a respections ya hadu da Dr na jiransa ya taresa suka nufi emergancy Dr Sardauna yace” ai ba sai muje canba ba wani matsuwa tayi ba bani room inda ba kowa zan dan duba zata farfado? ” ok Dr muje wani room suka nufa ba kowa tsaf dashi komai na gwaje gwaje akwai ya fita ya bashi guri wurgata yayi saman gadon ya cire gilashin fuskarsa ya shiga aikinsa yada ya dace saida yayi awa, daya cur akanta atsaye yana famar ceton ranta ya samu numfashinta ya dawo amma bacci take tsaki yaja” ai wlh dama kwayoyin sun kasheki shegiya mai ruwa da tsuntsuwa yarinya karama sai masifar shaye shaye toilet ya nufa bai jimaba ya fito ficewa yayi daga d’akin, yafi awa daya kafin ya dawo saida yayi sallah azuhur sosai Dr yakub ya karamashi yako ji dadi hakan tare suka dawo d’akin har yanzu bata tashi ba sun jima suna hira da yakub ya fita zauna bakin gadon yai da niyar kiran mashakura yaji sun isa lafiya Dan yayi niyar yana gama wayar zai tasheta yaci ubanta Kafin su tafi wayarsa ta dau ruri ganin Mahabeer ne yasa ya dauka ya kara akunne” my brother saboda Allah kana ganinta ta ci kwaya har tamata yawa ga yunwa kuma kazo ka banka mata kwayoyin zazzabi suka hadu sukayi mata yawa shegiya tantiriya wlh dama mutuwa tayi masifa Mahabeer ya fara masa karya kuma zaginta murmushin gefen baki yayi baice komai ba ya shiga ciza lips d’insa Mahabeer
Yayi magana cikin lallaba ” Dr Sardauna namu Dan Allah gayamun zee babyna ta farka idan ta farka bani ita na kwantar mata da hankali Dan nasan rigimar nemana zata maka banaso tayi kuka kuma kayi tuki ahankali bata saba da wahalaba ran Dr Sardauna yayi mugun baci amma ya nutsu yana sauraron yada Mahabeer yake kafa masa sharuda a kan banzar yarinyar nan yar kwaya itako lokacin ta farka tana manta da ba Saudia take ba ganin bakaken kayan jikinsa da yanayin sa na Mahabeer duk da taga yau kamar ya Kara girma tunda Sardauna yafi mahabeer girma da cikar halitar Namiji mikewa tayi zaune ta rungumeshi ta baya ta sakalo hannuwanta ta wuyansa ta kwantar da kanta saman wuyansa ashagwabe ta kirashi tana shafa fuskarsa ” ya Ahukhuya me yasameni ta fadi tana Kara rumgumarsa shiru taji kukan shagwaba ta saka masa ” wlh Ahukhuya yunwa nakeji ta fadi tana goga fuskarta kagon bayansa tana kuka k’asa k’asa iya karshan Bacin rai yau Sardauna yaje idanusa sunyi bakikirin ya janyota ya birkitota ta dawo gabansa jikinsa har tsuma yakeyi ya yarfa mata maruka har hudu ajere ya bankare mata hannuwa ta baya saida sukayi Kara bashiri ta Saki ihu ” Dan Allah Ahukhuya yi hakuri me namaka cilata yayi ta hadu da bango saida goshinta ya fashe tunda take bata taba jin azabar da takeji yanzuba ga yunwar da takeji ga cikinta na mata ciwo kafin ta Mike taji ya harbata ” yar iska yar kwaya wlh sai kin gwammaci mutuwa da rayuwa take mata kafafu yayi sai yanzu tasan da wa take idanu ta dago ta kalleshi ido hudu sukayi kauda kansa yayi duk da taji mugun tsoronsa ga wata irin walkiya da take fitowa daga idanusa da yanyin yada taganshin hadiye tsoronsa tayi ranta idan yayi dubu ya baci yinkurawa tayi ta Mike tsaye ta rike kugunta tana girgiza cikin dauriya dan taji azaba ga cikinta na ciwo tace” kutumar babbar buro ubancan kai idan na yafema dukan da kamun ayau Wollah Ba Faisal Hasheem Almahadee bane ubana ta fadi tana tunkarosa shikuma tsaye yake yana wani miskilin murmushi ya tura hannusa cikin kwantacciyar sumar kansa yana shafawa yana ciza lips dinsa Dan ransa yakai kololuwar baci jiranta kawai yakeyi yaga mai zata iya dashi idan ta iso gareshi….
[ad_2]