Uncategorized

A Bakin Aurenki Complete

 BAK’IN AUREN KI…漏Feenat Ja’afar.

1_Sauri take tamkar taci da k’a, kai daga ganinta

ka ga marar gaskiya, a d’ai d’ai layin da zai

sadata da gidanta ta t’saya tamkar munafuka ta

d’an leka, da sauri ta komar da kai tare da dafe

kirjinta mai barazanar fashe mata… “Na

shigesu.. Ja’afar? Ta fad’a tana mai sake

lekawa, sai karaf sukai ido hud’u dashi,tuni

buguwar zuciyar ta ya k’aru, bata ta6a ganin shi

a irin wannan yanayin ba.

“Mey yasa kika fita bayan yace ka’rki fita?…

Bak’in g’yalenta tasa tana t’sane gumin dake

t’sat’safo mata, cikin jihadi ta fito daga inda ta

boye harda d’aure fuskarta tamkar bata ganshi

ba.

Kanta na k’allon gefe tazo d’ai d’ai kofar gidan

zata shige ba tare da ta k’alli yanayin nashi ba..

Turus taja ta t’saya, ganin yadda ya d’aura wani

mukulli kan wanda ta rufe gidan dashi, cikin

k’arfin hali fuskarta na gefe tace “ya haka?

Wanda bai nan ma yafita,hakan yasa ta kara

fad’in “Ya Ja’afar ya haka?.. Tamkar kububuwa

yake cika, ji yake tamkar ya rufeta da duka dan

takaici, Ashe d’uk uban rat’suwar Salma ta mai

kan ta d’aina a fatar baki ya t’saya?..

Mota ya bud’e yana ko’k’arin shiga ta mot’so da

sauri, “Ja’afar magana nake fa… A tunzure ya

juyo da nufin kifa mata mari tai baya da sauri

gabanta na fad’uwa.

Lalle yau ta ta6o ran y’an maza, cikin bacin rai

yai mata k’allon banza, “kin za6i gidan suna

sama da sharad’i na koh? Toh mey kika dawo yi

min gida? Koh kin manta da sharad’in da na baki

na in kin fita toh kin fita “A BAK’IN AURENKI?…

Ido ta zaro tana dubenshi, kawai sai ta dake,

cikin k’arfin hali tace “A BAK’IN AURENA fa kace

Ja’afar? Daga gidan sunan shine har kake

wannan kumfar bak’in?.. Ta karasa tana y’atsine

mishi fuska,kawai sai ya k’ada kai ya shige mota.

Ganin da gaske tafiya zai yasa da sauri t ajiye

t’siwar ta fara kiranshi, ina,tuni ya juya a kalar

motarahi cikin zafin nama, da sauri ta mat’sa

ganin sai ya iya bi ta kanta..

Tana ganin da gaske yake hakan yasa tuni ta

t’sure, hannu ta aza bisa kanta cikin nadamar

fitar da tai sunan da ba’a ma gaiyace ta ba, “na

shiga uku ni Salma.. Na ja ma kaina wani bala’in..

“Yanzu igiyar Aure na biyu ta t’sinke kenan?..

Tuni zufa ta kara zubo mata dan tunawa da

kalaman Babanta, “d’uk randa zaki kara maimaita

haka Salma sai na 6alla kafarki in kin doso

gidana…. Fad’uwar gabanta ta t’sananta,t’saf

Baba zai aikata mata hakan,

ta k’alli gabar,da yamma, ta ma rasa ta ina zata

fara? Gefen dakalin gidan ta d’an dosana, da

d’ukkan hannunta biyu ta dafe kai,tuni kalaman

Ja’afar ya dawo mata, “in kin fita kin fita A

BAK’IN AURENKI….

Ku biyoni Bayan sallah dan jin yadda zata kaya…

By

Feenat

Ja’afar.

9/29/16, 8:46 AM – Queen Safiyyert馃憫: *A BAK’IN AURANKI* *漏 Feenat Ja’afar*. *3*-

Kai ya k’ada mishi, _”aure ba shine mafita ba

Ja’afar,ka g’yara wacce ke hannunka tukun,bana

tunanin wannan shawara ce_. Murmushi yai tare

da k’ada mishi kai _(“I know)_.. _”Amma ka gane

ba dan dad’i zanyi ba,nasan d’uk duniya ba

abinda Salma taki jini irin nace zan kara

aure,dole na d’andana mata mad’acin da ta

d’andana min nima_. Murmushi Garba yai yana

K’allonshi,wai yau Ja’afar ke maganar zai

d’andanawa Salman sa mad’aci?.. Kai ya girgiza,

lalle Salma tai wasa da damarta, dan yasan irin

dimbin son da Ja’afar ke mata, sai dai gashi za a

kaita a baro,dan ta fara sane ma abokinshi..

_”Bana tofa tawa ba nikam,nasan da kai da

Salma sai Allah,ni d’ai kai tunani abokina,kar ka

yanke hukunci cikin fushi azo daga baya ai

nadama_… Baki ya ta6e, kan ya ciro mukulli a

aljihunshi ya mika mishi, _”k’ar6i mukullin

motarka,dan aure kam nayi na ma gama,kuma

*Bintu* zan aura kasa ido_.. Ido waje Garba yake

k’allonshi,kan ya k’yalk’yale da dariya, _”lalle ka

d’ebo aiki..za kuma ka dasa ma Salma zargin ka

cikin ranta tunda kasan komai_… T’saki yai kan

yace _”zanso hakan ya kasance, dan zata fi jin

haushi sosai_.. Kai Garban ya k’ada yana kunshe

dariya, _”muje na sauke ka toh na Salma da

Bintu,kai (scene) din nan zai dad’in k’allo

wallahi_.. Ya karasa da dariyar keta. Murmushi

kawai yai suka shiga mota,har suka isa gida

Garba na mishi t’siya..da ya had’o shi da Salma

zai kicin-kicin. ************************ A wajen

Salma kuwa,sai da dare yai tana k’wance

d’akinsu na da sai juyi take,wanda ita kanta ta

rasa dalili,har yanzun haushin Ja’afar na kasan

ranta na ya mata wulakanci, sai dai da ta tuna

rabuwar igiyarta d’aya sai taji fad’uwar gaba. Yau

gata a katifa ba ta ita da Ja’afar d’inta ba?..yau

d’aya ta raba alakar matashin kanta(kafad’ar

Ja’afar) sai pillow… Hannu takai kuncinta,da

mamakinta hawaye take,kawai sai ta ida

karasawa ta fashe da kuka.. Wanda kai da gani

na k’ewar Jafaririn ta ne da t’sant’sar

nadama,amma ina,zuciya taki amsar hakan.. Ga

uban sauro da ya damu k’unnenta da ihu duk da

da Katanga a t’sakaninta dasu(net), ga uban zafi

ba wuta ba (Gen), d’uk t’siya tasan da a gidanta

ne da yanzu tana shan iskar injin da Ja’afar ke

k’unna mata d’uk dare ta k’wanta dan bata bidar

zafi.. Ga mama tace ba mai tada mata inji

Babanta baya gari, kuma bata kud’in mai…..

Shima hakan take ga Ja’afar, kusan a hali d’aya

suke,sai dai shi kawai ya kura ma fankar d’akin

da ke kad’awa a saman d’akin ido. Tabbas har

yanzun baida sama da Salma koh a kasan

zuciyarshi.. Yana sonta, so marar misali,duba ga

yadda suka gina soyayyar tasu kamin aure.. Da

za’a ce mishi a da Salma zata sauya hali gaba

d’aya musamman akanshi da zai mu sa… Juyi

yai ya jawo filo,d’uk t’siya tanan yai k’ewar

Salma.. Dan karamin t’saki yai kamin ya tashi yai

waje dan kashe inji. *By* *Feenat Ja’afar*

9/29/16, 8:48 AM – Queen Safiyyert馃憫: *A BAK’IN AURANKI* *漏 Feenat Ja’afar*. 4-

Salma Umar Y’a ce ta biyu gun Mama(Haj Rabi’a)

da Baba(Malam Umar),y’an asalin Yobe

ne,kasuwanci ya kawo kakansu Kano da rabon su

Salma. Su biyu kawai ne a gun kakan su Malam

Bukar Mai buhu,baban su Salma ne karami, sai

yayanshi Baba Aji, yaranshi a kallah za suyi

(16),yayin da Baban Salma ke da uku,Aisha

(Aunty A’i)dan tafi Salma sosai,Salma,sai Ummi.

Kasuwanci ne gadon su Baba,dan koh bayan

rasuwar kakan su Salma sun cigaba da juya

abinda ya rage musu. Suna taimakon juna

sosai,hakan yasa kansu yake a had’e, duk da

rufin asiri ne kawai na Allah. Sannan d’ai-d’ai

iyawa sun bama yaran su karatu da tarbiya,suna

da t’sanani musamman Baban su Salma. Sai dai

fa ita Maman su gani take kakarsu ta yanke

saka,tunda Allah ya hore mata yara mata uku

setin samira ta zuba jari,shi yasa d’ukkan wani

abu akan A’i yake karewa dan ita tasa a lokacin.

Ba lefi,ak’wai dan k’yau irin na ainashin mutan

kanuri,sai kuma Maman dake asalin Shuwa,ba

farare bane,za dai mu iya kiransu da _”black

beauties”_sirrin su kuwa,diri ne da yalwar gashin

ka da _”beauty point”_ _(dimples)_.. Wanda

tamkar kowa diga mata ake. Hakan yasa kasuwar

Aunty A’i ta daga da sauri,tuni k’wa Mama abin

nema sai ya samu,hakan yasa ta kara sa ma

sauran Burin da yafi na Aunty A’in.. Barin Salma

dake doguwa ce cikin su. Ita kam Salma bata san

ma ana yi ba. Kasantuwar shagonsu Baba ya

zama biyu sai ya zamana aiki yai musu yawa,

har bai samun damar dawo wa gida cin abinci sai

d’ai Ummi koh Salma su kai mishi. Ranar kaiwar

Salma ne,tai shirin Islamiya ta doshi shagon su

Baba. Tunda ta ajiye abinci taki gaba taki

1 2Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button