WAYAFI SONTA 4

WAYAFI SONTA ?????
WANNAN LABARIN NA KUDINE…gamai bukata zata biya naira 300 kachal ta karanta ” tahanya mafi sauk’i Zaki siya Zaki tura kudin ta account number 0089110527 suwaiba Hussaini zakirai access bank… saikiyi screen shot kituro shaidar kin biya ko kuwa kituro MTN ta wannan number na 300″ 08100084251
Domin karanta books namu..
Y’AR SADAKA book2 na mmn sultan dakuka dad’e Kuna nema danjin yazata kasance…naira…200 ne gamai bukata yatura kudin ta wannan account 0089110527
WAYAFI SONTA ( mmn fareesa) naira 300
Induka kakeso naira 400 ne kachal…masu bada kati suyi mgn a wannan number 08100084251….
Inkinsan Zaki fitarmana da books karki siyasa….
Free page
p4
Murmushi Mai ciwo Inna tayi had’e da nuna husna ta dubi Umar tace yimana bayani dangane d ita…..da mamaki Umar yace bayani Kuma Inna?” baba yace Kai dakata! karka maidamu bamuson me mukeyibane…narigada nagama mgn ita zaka aura….tokodan sbd sune zainab ke kuka cewar Maryam tana kallon Umar?” dafe Kai Umar yyi had’e da cewa Wai meke faruwa ne kusanar Dani me wadannan marrassa tarbiyyar sukazo yi anan gdn ??” Inna tace sunxo akan aurenka da itane….najah tayi saurin Jan hannun husna tace zomuje….Umar yace bbu inda zakuje munafukan ALLAH sainaji me kukazo kuka cewa iyayena” kafin nadauki mataki…. yafad’a Yana had’e Rai…baba yace Kai saurara mana dg abin arziki inzainab ka aura uwarme zaka k’aru dashine?…. Inna ta girgiza Kai kawai tafara korama Umar bayani…..cike da mamakinsu yake kallonsu….kafin yace…wlh duk k’aryane Inna ,yadube su yace dake da y’ar tayaki kanfe din duk zaku gane kuranku…wawaye Dana aureki gara na mutu bbu aure har k’arshen rayuwata”aini kinmun tsufa dubeki dallah sannan abin nan dakikayi har media saina yad’ashi sbd yazama iznah gamarasa tarbiyya d kunya irinki….ke ahaukanki iyayen k’warai zasu yarda d’ansu ya aureki….yah isah haka mlm inkafasa yadata baka k’aunar ALLAH Kuma saikaga Mai zai biyo baya wlh! Bbu abinda zai gani sai alkhairi…cewar Inna tanama baba kallon gargadi… yyinda d baba duk jikinsa yyi sanyi yarasa abin cewa har husna d najah suka fice bayan Umar yamusu tas….shima yanufi gdnsu zee dan xuwa ya rarrasheta yabata hkri.
Inna ta dubi baba tace wlh kacanza Hali sbd son abin duniyar ka yyi yawa har kana neman zubda girmanka danamu da yayanka Dan sbd kud’i kaci amanar zumunci…na tabbatar mahaifin zainab bazaiki bawa Umar zainab ba sbd yaga Mai kud’i…. sallamar baffa sule( kaninsu baba) yasaka Inna yin shiru….tana murmushi tace sannu da zuwa mutanen abuja yyi murmushi yazauna kan kujerar tsigunne dasu husna suka tashi…suka gaisa….Inna na tambayarsa Mai dakinsa yace lfy qlau…nan suka hau fira Dan rabonsa d kaduna kusan wata7 kenan acan abuja yake kasuwancinsu shekaran sa 12 da aure har yanxun matar Bata haihuba…********
Koda zainab ta shiga gd” parlourn mama ta nufa ” tazauna kan kujera ta had’a Kai da gwiwa tacigaba da kuka…
Mama dake rabon abincin Rana duk tana hankalce da ita” byn ta idarne ta biyota cikin d’akin t zauna gefenta had’e da cewa kewai lfy Zaki shigo kina kuka tun d’azun meke faruwa ne??” Cikin shashsheka tace bbu komai!
Mama ta tabe baki had’e da cewa nasan be wuce tsaninku d umarba,Kuma nasan bazaimiki komai ba” k’ila wata kika gansu tareko?” Dan nasanki dazafin kishi y’ar ficiciya dake…nifa mama bbu komai! Uhumm kikace ba,aidama ana yin kuka Dan dad’iko?” To Bari kiji ba’a nmj haka! Kuma nmj mijin mace 4 be garama ki sassautawa zuciyar ki wlh ,Danko bayan ya aureki in ALLAH yace zai k’ara aure dole yak’ara Koda kuwa baya son matar….koni nan dakike gani kinsan kishiyata basonta ubanku yakeyi Amma dayake matar mutum kabarinsa saigashi taja raayinsa ta hanyar surkulle ya aureta gashi harda zuria atsakaninsu to wlh kibi ahankali sbd shi nmj… sallamar Yaya Umar tasaka mama yin shiru…ta amsa yashigo yazauna suka gaisa ta fice dg parlourn.,,,,
Kusada zainab yadawo yazauna ahankali ya janye hannunta data rufe fuskarta dashi ,cikin taushin murya yace haba zee! sbd wata banxa can Zaki zubar mun da hawayenki masu tsada da…fisge hannunta tayi tana maka Masa harara tace malam sakeni…. murmushi yyi Yana kallonta yace in ank’i sakekinfa?wlh zainab banida wata alak’a da yarinyar nan ki yarda Dani…baza a yarda d’in ba ainaji komai da suke fad’a itada k’awarta saika hanzarta tura magabatanka tunda baba yace yagama mgn ita zaka aura….Wai mekike fad’a hakane zeetah ? Kinsan halin baba karsaka maganar shi aranki har ta b’ata Miki Rai kiyi hkri Dan ALLAH ” wlh banason husna tazone dama Dan ta hargitsamun family ne” akan abinda yafaru kwanaki to ko yanzunma nazageta da gargad’arta karta koma zuwa gdnmu…inta sake mezaka Mata?” Duk hukuncin da zeetah ta yanke shi zanmata… yafad’a Yana murmushi had’e da sake Mata hannu yasaka handcheef yagoge Mata hawayenta ,kafin yace kin hak’ura?” d’aga Masa Kai tayi alamar eh”yace sai kinyi murmushi tukum sannan Zan yarda….kallonsa tayi suka had’a ido…atare sukayi murmushi… adedenan Kuma khalifa yashigo da plate din wake da shinkafa da Miya da latuce ya ajiye gaban Umar,yace gashi Yaya” kafin yafice..
Umar yajawo abincin yace nasan bakici abinciba ko? Tace eh…yamotsa yadebo cokali guda yakai bakinta…bbu musu ta karb’a ! Tare suka cinye abincin suna dariya tamkar wani Abu be faru ba….ta rakosa suna asoro saiga baffa sule….yakallesu yyi murmushi yace love birds…suna dariya suka gaidashi d tambayarsa anty mariya matarsa yace lfy qlau,kafin yashiga ciki Dan gaisawa dasu mama…Umar yarubi zainab yace kikoma ciki anjima da dare zandawo naka miki d’ inkunan nan kinjiko”” to shikenan nagode Yaya saika dawo ALLAH ya yatsare” Yana murmushi yace ameen my real one…Kamar yadda Umar yace haka kuwa yadawo da dare…awaya yakira zainab dan yasan goggo haule tana tsakar gd tun yau itake girkin dare…sai k’amshi ketashi ajikin zainab ” bayan tasaka doguwar riga ta atamfa ajikinta ta Dora karamin mayafi tasamesa zaune kan dadduma asoron gdn ga fitila ya kunna”sallama tayi cikin siririyar muryanta ,ya amsa Yana cewa sannunki da zuwa gimbiyya ai shanyar dakikayi t bushe, yafad’a cikeda tsokana” tayi y’ar dariya ta zauna agefensa tana cewa Ina wuni ?” Ya amsa da lfy lau y’anmatana!yana bud’e ledar hannunsa yace duba kiga d’inkunan kigani sunmiki ?” Tana murmushi tace namasan sunyi “Dogayen ruguna ne kala3 biyu na material guda ta atamfa sai hijab kala2…d’aga kayan take tana yabawa cike da d’okinsu da nuna jin dad’in ta” yakafeta d Ido…Yana murmushin jin dad’in yasakata farin ciki…cikeda zumud’i tace Yaya Ina zuwa tayi cikin gdn da kayan…tasami mama kan tabarma zaune d khalifa suna Shan iska tayi saurin azamata kayan gabanta tana cewa mama duba ki gani Yaya yamun.
Tafad’a cike da faraa…fuska sake mama ke duba kayan tace Masha ALLAH gsky sunyi kyau” kingode ALLAH yasa ki kashe d kanki….uhumm dabaa San asalin angulaba dasai ace dg masar take duk mace Mai rokon nmj Bata daraja wlh…cewar goggo haule cike da nuna tsantsar hassadarta k’arara…mama tayi murmushi tace oh ALLAH ya shirya mutumin dake shiga abinda beshafeshiba….yo ai gara wacce zata roki saurayi da wacce zatace tanason saurayi yace bayasonta….tahad’a asiri yasota adole…gum goggo haule ta yi d bakinta Dan batasan mama zata Fadi hakaba ..( inbaki yasan abin fad’a besan Wanda za’a maida mishiba)
Zainab kuwa soro ta koma suka cigaba da firarsu da yah Umar har 10:pm tukum sukayi sallama….
*********
Sanye zainab take da yunifoam na islamiyya ajikinta”gaba d’aya yau tarasa meke damunta ?” Batajin dad’in jikinta ga faduwar gaba datake yawan ji, sannan duk taji batasan fita…wayarta spack 2 da Yaya Umar yabarmata kyauta ta dauka tayi calling D’insa… salamu alaikum gimbiyya yata !ta amsa cike da shagwaba tace Yaya nikazo karakani islamiyya ! Murmushi yyi yace wato yau sarauta kkji kenan ko?” Kina raina ,inatunaninki kika Kira” nigashi dinkin mutane nakeyi”to shikenan tunda d’inkin yafini. Matsayi agunka”maida wukar gimbiyya wasanake bara nazo sai muje ko?” Yauwa Yaya ta fad’a tana murmushi ta yanke wayar….befi 10 minit ba” yakira ta fito su wuce…
Kallonta yyi byn tafito dg gd yace INASONKI zainab! Dan ALLAH innamiki laifi kiyafemun kinji?” Arikice tace banganeba Yaya?” Kamar ya nayafe maka?” saikace Wanda zai mutu har kaja gabana yafad’i…uhum zeetah ai basai Wanda zai mutu keneman yafiyaba…inaso kimin Abu 2 arayuwa zainab” cike da mamakin kalamansa tace kamar me? na 1 karki manta dani arayuwarki na2 kimun addua…gsky Yaya kabari kamar Wanda zai mutu sokake katayarmun da hankali,nima ai INASON KA! tafad’a cike da kunya…..kafin ta juyo Dan ganin Mesa yaki mgn,taga wata bak’ar mota ta nufota da gudu….da sauri yah Umar yature zainab dake gabansa tafad’a bayan wasu yara,itada yaran suka fad’a kwatar dake bayansu… shikuma motar ta bankesa yyi sama yafad’o k’asa…atake motar tabargun atsiyace….yah Umar na kwance cikin jini…. arikice zainab ta fito dg cikin kwatar kamar mahaukaciya ta nufesa da gudu,tarike Masa hannu… alokacin har mutane sun taru agun….cikin kuka tace Yaya! Tana kallonsa” Yana wani irin nishi yamatse hannunta” yyi murmushi cike da azaba yace INASONKI zainab! ALLAH ya Baki Wanda…be Ida fad’a ba yarik’a kalmar shahada….atake Rai yyi halinsa….mutanen dake tsaye Gurin sukayi kabbara suna cewa ALLAH yakikanka bawan ALLAH! Arazane zainab ke kallonsu ta tashi tsaye tana girgiza Kai had’e da sakin wata gigitacciyar k’ara ta dafe Kai sbd yadda taga duniyar na juyamata…atake ta sulale k’asa su mammiya….???????????? Kuyi hakuri haka yafaru badaga gareni bane…
Share
BY MMN FAREESA????️