MAKAUNIYAR KADDARA 48

 *Page 48*

Duk wacce batayi anfani da sabulunnan ba anbarta abaya acan karshen bayama kuwa duk Mai tantama akan sabulai nagyaranjiki cewa basa Aiki toh yacire mg’s domin kankat ne insha Allah babu Wanda yayi anfani dasabulunmu yace baiyi ba koyaushe mg’s sai sanbarka amare da uwargidaye hardama yanmata kuhanzarta kusamu naku ba karya domin bama cika Baki kugwada kubada labari da bakunanku sabulu daya tamkar dubu wadandama basasan using cream sabulun mg’s herbal whitening black soap yawadacemuku jikinku zaiyi kyau koyaushe kukasance clean cikin kamshi Kuna glowing koda bakusa turare ba????

Kayanmu bana bleaching bn organic ne sunagyarajiki fiye da tsammaninku  zaifiddomuku da ainihin natural beauty dinkine Wanda yagwada shi zaitabbar amare kuyi kokari kumallaki mg’s domin baruwanku da zuwa adirjemuku jiki zakuga yanda fatarku zata dinga walwali 

Ina masu pimples 

Tabo(spot)

Sunburn dama dukwani matsalar fata kuyi kokari kunemi soap dinnan before 2weeks zaisharemuku hawaye kuzama abun kwatance 

Sister’s masu nankarwa kuma kunemi soap dinnan Yana rage nankarwa sosai????????‍♀️duk me shakku tayi kokari tagwada mg’s insha Allah bazakiso rabuwa dashi ba 

Akwai maisa haske Amma kayanmu nafada bana bleaching bn zaifiddomiki d ainihin halittarkine yagoge dukkan dattin jiki 

Akwai Kuma Wanda zaimiki maintaining skin dinki yasaki fresh fatanki tazama kalar hutu

Sannan munada beauty kit????duk me bukatan (flawless skin/perfect glow) toh yy  kokari yamallaki set dinnan wn zncn baa mgn????????‍♀️cuz duk inda kayi se ankalleka????

Buh gsky wnd besan yy haske karyayi using set din cuz gsky yn sa haske buh bn bleaching ne b zaidai murje fatane nd bring out that hidden beauty in you????

Pls bamacika Baki you HV to try it and see for yourself

100%tested nd trusted 

Beauty kit:11k

Soap price:3k

Location:kaduna buh munaturawa ko Ina Amma delivery is not free

Maiso kindly message 08062991549

Call 08064532391

Note:Babu inda zakusami mg’s herbal whitening black soap sai a number dinnan bairiga yakai market  b inyakai we will let you know buh as for now wnn numbern ne kawai????

Maiso yahanzarta before yaji sold out akwaisu available now insunkare you HV to wait akawo so maiso yahanzarta????adade anayi sai gsky????????

Mg’s skincare

_________________________

*Page 48*

………..Lefe kam yayi sai dai makiyi ya kushe, dan daga na Momie harna Mahma sai dai ace ALLAH ya saka musu da alkairi, da AK yace sunyi yawa akai ɗaya Baffah cayay duka za’a kai, idan yay wasama shima sai ya haɗa nashi dole an haɗa an kai. Dole AK yay gum da bakinsa dan yaga waɗanan iyayen amaryar sai da lallaɓa.

       

     Kamar yanda ake shiri gagarumi a shira’s family da gayyatar dangi lungu da saƙo hakama su mmn sadiq suke nasu shirin, dan tuni Gwaggo Maryam ta iso kano sun ɗinke itada ƴar uwarta suna shawararsu, hakama Abba ba’a barsa a bayaba wajen gayyatar dangi da shirya yima Zinneerah kayan ɗaki duk da AK yace basai sunyi komaiba, dan koba shine ya auri zinneerah ba dole shine mai mata kayan ɗaki matsayinsa na babban yaya. 

         Lokacin daya ambata hakan murmushi kawai Abba yay da sanya masa albarka, a zuciyarsa yana mai jin daɗi da taya Zinneerah samun miji irinsa.

   A danya ma baba shirinsa yake da ƴan uwansa batare da sanin Inna ba, dan Baffah da kansa ya kira Baban a waya ya sanar masa hukuncin da hajiya iya ta yanke akan tarewar, baba baiji komaiba yace ALLAH ya kaimu. Daga haka suka fara shirye-shirye.

     Akan zuwan su mmn sadiq can kuwa har agama biki sun gama magana da Abba. Dan ana gobe tariya can zataje, danginsu na ɗanmusa ma acan zasu sameta, idan za’a ɗakko amarya washe gari su biyota zuwa kano insha ALLAH.

     Zinneerah dai nacam nashan gyaran wajen hajiya falmata lungu da saƙo, ita kanta tasan ta gyaru sai dai Alhmdllh, har tsara yanda zataima su meenal yanga take a ranta tana murmushi. Sai dai kuma iya hasashenta ta rasa dalilin wannan gyara haka, duk da yanda hajiya falmata kan zauna tana mata lectures akan abinda ya shafi aure kan tsunduma zuciyarta a dogon tunani da nazari. Har takan tambayi kanta anya ba aure akai mataba kuwa?. Rashin samun amsa ke sakata jefar da tunanin ta kama wani daban.

    A randa Zinneerah ke cika kwanaki shidda gidan hajiya Falmata aka kwashi akwatinan lefenta zuwa gidan Abba. kasancewar ansan da zuwansu sun sami tarba mai ƙyau duk da dai daga nan Danya zasu wuce. Sai da aka buɗe kaya Abba dasu Mmn halima suka gani. Su mmn sakina ma dai sun shiga layin ƴan kallo suna haɗiyar zuciya, daga ƙarshe suna shiga ɗaki Sakina harda kukanta rurus. Ita kanta maman tasu kukan zucin take wanda yafi na fili ciwo dacin rai.

         Maƙwafta sun shishshigo suma suka sanya albarka kafin masu binsu Danya su kammala shiri su sake ɗunguma domin kaiwa can. Dole badan mmn sakina tasoba akai tafiyar da ita, itako mmn halima da yaranta biyu ai sune ƴan gaba-gaba, sai maƙwafta da ake gaisawar mutunci da matar Nazifi da suma za’aje dasu.

     A ƴan gidansu AK kuwa Mommy ce, sai Adilah data maƙale, sai Momie da Ummi, da su Aunty Khadija yaran Momie na farko su biyu. Sai matar Alhaji Yusif. Sai kuma mahaifiyar Dr Mahmud. Gaba ɗayansu dai mota huɗu sukayi harda ta kaya, suka tafi a jere gwanin sha’awa dan su Khalipha ne masu kaisun, karan farko da zaije tushen Zinneerah.

       Anan ɗinma dai ansan da zuwansu, dan sai da safe baba yake sanarma Inna, amaryarsa kuwa tasani kusan kwana biyu, da itama akai aikin abincin baƙin a gidan Gwaggo Laritu harda Yaya Gajeje ma.

     Ƙarfe ɗaya da wasu mintuna motocin su Khalipha suka shiga cikin garin Danya. Gidan maigari suka fara isa dan can su Haneef suka sani, daga can aka saka yaro musu rakkiya dan babu wanda yako fito a motama a cikin matan.

      Cike gidan yake da ƴan uwa domin amsar lefe, dawowar su Gwaggo Laritu gidan kenan su Mommy suka iso, an musu tarba ta mutuntawa da girmamawa, inna dai shigowar waɗan nan ƴan gayun matama neman birkitata yayi. dan duk iya jarabarta sai gata tai muƙus sai kallo da idanu.

        Gidan baba yasha gyara aƴan kwanakin nan, dan ɗakuna ya sake zubawa sabbi aka kuma siminte tsakar gidan tsaf, ga amaryar baba akwai tsafta dan tunda tazo gidan ya ƙara ɗaukar saiti. Musamman yau ma datai masa gyara na musamman ita da Sa’a. Dan jiya akai taron sunan Karima duk da dai baimayi wani armashiba. Sai uwar rigima da aka kwasa tsakanin dangin Babawo dana Inna. Saboda Babawo har yau baizoba yakumaƙi cewa komai, ita kuma idan an tambayeta sai tace bata masa komaiba.

       A ƙarƙashin bishiyar gidan aka shimfiɗa musu tabarmi dansu sha iska, aka kawo musu lemuka da ruwan leda da su baba suka tanada domin su kawai. Ba ƙaramin daɗi su Mommy sukaji ba a yanda aka tarbesu da girmamawa da mutunci. Bayan anyi gaisuwa da tanbayar iyalan juna aka shigo da akwatunan da suka saka ƴan uwa fara callara guɗe-guɗen da suka nema jefa Inna a hauka. Dan duk yanda taso ta daure ta kasa sai gata ta shiga zage-zage.

1 2 3 4Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button