Uncategorized

SAMEEHA G


_????SÂMÊÊHÂ????*_

              (G)

Ko da momy ta shigo ɓarin Sameeha zaune ta iske su Sameer na tillastawa Sameeha cin indomi daya dafa mata ran ta a ɓace ta ƙaraso wajan tana.”””

“”””Ɗiya ta sannu,ya jikin daure mana ki ɗan saka ko loma biyu ne zaki ji ɗan ƙarfi a jikin naki,ka ga wannan,momy ta fito da ƙullin magani da rubutu a jarka ta miƙawa Sameer,Sameer yasaka hannu ya karɓa ya na.


“Ya tsarin maganin yake momy tun yanzu tasha walahi bayan fitar ki abun yasake tashi har hawaye sai da na zubda tsabar wahalar da Samee tasha……..


Hawaye kuma Sameer kamar wani me zuciyar mata.


Momy baki ga yanda Samee tayi bane abun fa har yafi na farko muni.


To Allah ya bata lafiya gashi wannan sha zatayi yanzu nan sai kuma da daddare idan Allah ya kai mu tayi turare idan zata kwanta shima safe da dare insha Allahu zata samu lafiya wajan wani alarama na amso mata danayi masa bayani yadda takeyi yace jinni ne ke wahalar da ita tun tana yarinya rabuwa dasu kuwa sai a hankali amma yace kar ayi wasa da wannan maganin yana ƙarewa idan ba adace ba a koma ya bada wani, dan Allah kayi yadda na faɗa maka kaji Sameer dan mu samawa yarinyar mutane lafiya wallahi tausayi take bani ina kallon ta kamar yanda nake kallon Zee a guna,”insha Allah momy zanyi fatan mu Allah yasa adace..


Amin kam Sameeha ki daure mana ki ɗan ci ko kaɗan ne ko ni zan baki a baki ne naga ba ƙarfi a jikin ki,da sauri Sameeha ta gyaɗa kai haɗe da ɗora hannun ta kan cokalin indomin ta soma ci a hankali,ci take kamar magani bakin gaba ɗaya baya mata daɗi amma dole a haka take turawa dan kawai momy kar ta taɓa ta,da sunyi ido biyu da momy sai taji wani abu na mata yawo ajiki a haka har ta ɗanci kaɗan ta bari Sameer ya tsiyayo mata rubutun a kofi ya bata ta karɓa ta shanye gaba ɗaya………


     “Ko da rubutun ya ratsa jikin Sameeha hamma ta soma yi,momy ta kama ta””””.


“”Tashi ki je ki kwanta tunda kin sha rubutun an jima zan dawo nayi miki turaren.


Wash Allah momy ciwo jikina ki sake ni dan Allah.. 


Yi haƙuri sauƙi ne yake samuwa gashi har kin fara magana…….abu kamar wasa Sameeha sai kuka tana momy ta cika ta jikin ta ciwo momy kuma ta dage sai ƙwa ƙwumar Sameeha take a dole sai ta kai ta ɗakin Sameer ta kwantar a hakan kuwa suka shiga ta kwantar da Sameeha tana wayo wayo ta fito da zumar zata je tayi girki ta dawo,Sameer ya amsa da to ya shiga ɗakin.



“”A chan saman ɗakin ya hanyo Sameeha an maƙure ta a jikin bango  sai shure shuren ƙafa takeyi da miƙo wa Sameer hannu,a razane ya fito daga ɗakin yayi ɓangaran momy da gudu…..


yana shiga yabi takan zee ya tsallake tsabar gigicewa Allah yaso bai taka taba yayi ɗakin momy da tuni ita ma zee ɗin tabi bayan sa tana””Ya Sameer lafiya me ya faru??????


Ko ta kan ta bai bi ba ya shige ɗakin sai haki yake yana…….


“”Momy Sameeha zata mutu,momy,zata mutu……..ya na faɗa yana nuna hanyar waje,da sauri momy ta miƙe ta kama hannunsa suka juyo nashi ɓangaran a tare zee ta shige ɗakin ta dataji matsalar ta Sameeha ce tayi tsakiiiii.


       “”Turusss Sameer yayi ya zubawa Sameeha ido dake kwance akan gode sai baci take hankalin ta a kwance,momy ta dube shi ta ce….


“”Meye hakan Sameer,ko dan ka ɗaga min hankali.


Wallahi Allah momy kinga chan,”Sameer ya nuna saman bangon ɗakin,””a nan naganta ashaƙe sai shure shure take tana miƙo mini hannu..


Hmmm to yanzu waya dawo da ita kan gadon kai da kace tana manne asama kamar gemage……


  Na rantse da Allah momy anan na ganta.,harara momy ta jefa wa Sameer,a zuciyar ta ta furta.


“Alhamdulillah,aiki yayi,,afili kuwa ta ce,””””ko kai ma bakada lafiyar mu soma yi muku maganin tare anya idon ka bai sami matsala ba Sameer ko duk furgicewa ce.


Ajiyar zuciya Sameer ya sauke,haɗe da goge gumin daya tsatssafo masa daga goshin sa ya dubi Sameeha dake bacci kashirɓan har da gyara kwanciyar ta ya sake duban momy dake hararar sa ya numfasa ya ce”””””


Gaskiya momy a mai da Samee gidan su ko ta samu kulawa ta musamman.


Sai ka ɗauke ta ka maida tunda ni ban iya kulawa ta musamman ba duk ƙoƙarin danakeyi akai ni zaka dubi tsabar ido na kace a mai da Samee gidan su Sameer,da wannan hannun na reneka har ka kawo munzalin da zaka nuna ni ban iya ba sai kai saboda ka girma.


Ba haka nake nufi ba naga abun ne yafara wucewa yand nake tunani,kin ce lalurar nan tun tana ƙarama ce to kinga ai ya kamata iyayen ta su san da matsalar tun kan abin ya girmama,kuma momy……….dallah rufe min baki ɗan iya to babu inda za akai ta,kai ba abin kunya da gori bane ace ka kasa lura da matar da ko cikakken wata (2) batayi a hannun ka ba zaka mai dawa iyayen ta ita wato su ne wahalallu ta warke ka kwashi ƙafa kaje ka ɗaƙƙo ta ko to ka shirya  jiyewa kunnuwan ka zagi kala kala dan ka fara ji kenan tun daga gidan ku,,,,kai babu inda za akai ta har sai munyi iya bakin ƙoƙarin mu a kai munga abun yaƙi ci yaƙi cinyewa ban yafe kuma kaje ka sanar da iyayen ta ba kaji na faɗa maka kuma yanzun nan zan ɗauke ta ta koma nawa ɓangaran tunda kai ka ƙosa…


“kiyi haƙuri momy wallahi ba haka nake nufi ba Allah ya huci zuciyar ki na bar maganar har Allah ya bata lafiya,


Da dai yafi maka bazaka ja mana zagi muna ji muna gani ba,kaje ka kira min zee tazo ta kama mun ita.


To.

Sameer ya furta ya fita da sauri,Sameer na fita daga ɗakin Sarkin Hatsabibai ya bayyana da wata koriyar tukunya sai zaɓalɓala cikin ta take,momy na ganin sa ta miƙe haɗe da washe haƙora ta ce.


“”Tsafi ya dafa maka ya sarkin hatsabibai a baje da ita har sai tabar duniyar gaba ɗaya????,nan da nan sarkin hatsabibai yafar furta wazu lazumai yana hura tukunyar dake hannunsa a take hoton Sameeha ya bayyan a kai ya soma juya tukunyar zaɓalɓalar na ƙara yawai ta ga tirire dake tashi gaba ɗaya ya turnuƙe ɗakin,,kamar wace aka muntsila Sameeha ta fara motsi chan kuma ta soma juyawa ita kaɗai akan gadon tana wani irin nishi me ban tsoro…………




*Afuwan Fans ina busy ne hakan ma nayi ne dan kawai kuji daɗi.*










_*By*_

_*Maman Dr*_




“””

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button