MAKAUNIYAR KADDARA 47

*Page 47*
………..Cike da ɗokin zuwa ganin mmn sadiq dasu Aliyu Zinneerah ta
shirya cikin wando da riga na parkistan red and white, sai gyale red
data naɗa a kanta wanda ya fiddo mata ƙyawun da fuskrta ta ƙara. Kayan
sun zauna mata ɗas a jiki kasancewarta mace mai mulmulallan jiki da
ƙyawun surarta ta ƙuruciya. Babu wani kwalliya a fuskarta, amma ta saka
lipstick kaɗan da yayma lips ɗinta ƙyau, dan tanada lips masu ƙyau da
tsarinsu ya fita sosai yanda suke ɗaukar jambaki kamar wata babyn roba.
Takalmi tasa mai ɗan tudu da igiya, sai side bag ɗinta ƙarama. A yanda
tai ƙyau dolene ka kalleta ka sake kallo, ga ƙamshi tana bazawa dan
Zinneerah gwanace wajen ɓarnar turare, idan ta samu batai masa da sauƙi.
Ƴar jikkar data zuba kayanta kala biyu da tsarabar chocolates ɗin su
Abdul ta ɗauka, dama hajiya iya ta fice ita tana falo tuni.
Hajiya iya kawai ta samu a falon itama tana ƙoƙarin fita, samarin
gidan tun bayan breakfast suka fice, hakama ƴammatan, su Jamal kuwa
batasan ina suka dosaba. Hajiya iya dake ƙoƙarin fita tace, “Inno kashe
tvn nan ki taho nasan Moddibo nacan ya cika da hasahinmu”.
Da to Zinneerah ta amsa tana ɗaukar remote, bayan ta kashe tvn ta
gyara labulolin sannan ta fito, ƙofar ta rufe dan masu aikin Hajiya iya
basu dawoba, maybe sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Tafiya ta fara
cikin nutauwarta tana ƙoƙarin ɗaura agogo data ɗakko a tsintsiyar
hannunta da dosar inda ta hango Hajiya iya da Mommy tsaye da alama harda
ita zasuje. Idonta bai lura da AK ba sai da tazo dab dasu tana ɗagowa da
shi ta fara tozali yana ɓullowa daga ta gaban motar waya a kunnensa
alamar magana yakeyi.
Kallon nata yayi dai-dai da saukar nasa idanun a kanta. A take ƴar
sakewar data hango akan fuskar tasa ta ɓace ɓat, ya tsuke fuska yana
mata kallon data nema kifawa saboda harɗewa da ƙafafunta suka shigayi.
Saurin maida kanta tai ƙasa tana cigaba da takowa ranta fal nauyinsa da
kwarjini, sai mita take a ranta kuwa. (Haka kawai bakama mutum komaiba
yayta hararka, shi wai baya ganin waɗanan idanun nasa manya da ƙarfinsu
yay yawa suna tsorata mutane)…….
Da wannan tunanin ta ƙaraso Mommy dake kallonta tana ambaton,
“Masha ALLAH ɗiyata irin wannan ƙyau haka”.
Ƙasa Zinneerah ta ƙarayi da kanta tana murmushi, hakama Hajiya iya
murmushi take tana kallonta itama. A bazata sukaji AK ya saki tsaki,
cikin faɗa-faɗa yace, “K! Koma kisa hijjab”.
Ba Zinneerah ba hatta su Mommy sai da suka dubesa, shiko ya fuske ya
buɗe murfin motar ma a fusace ya shige abinsa. A sanyaye Zinneerah ta
juya zata koma dan shi ba abin wasanta bane, waɗandama suka girmeta da
shekaru masu yawa a gidan sunabin dukkan dokarsa balle ita ƴar jiya.
Dakatar da ita Hajiya iya tayi ganin yanda tai ƙwalƙwal da idanu kamar
zatai kuka, ta kamo hanunta tana matsawa saitin driver da yake zaune.
“Haba Moddibo aimata haƙuri tunda ta rigada ta fito, ai kaga gyalen ya
rufe mata jiki, kuma naga daga mota sai gida”.
Shiru yay kamar baiji mi Granny ta fadaba, sai da ta ƙara leƙasa
tana faɗin, “Oh nima yarfin daka iya zakamin?”.
Idanunsa da suka canja launi ya ɗago ya dubi Hajiya iyan, “Amma
Granny …….”
“Dan ALLAH ai nace”. Tai saurin katsesa dan tasan shegen taurin
kansa da dagiya akan abinda duk ya kafama sharaɗi. Badan yasoba ya ɗauke
kai daga kallonta yan yima motar key. Murmushi Hajiya iya tayi da duban
Zinneerah. “Kinga zagaya can kusa dashi ki zauna Inno, mu saimu zauna
baya da Mommynku”.
Kamar Zinneerah ta fasa ihu taji, dan yanda taga fuskarsa batai
zaton ya haƙuraba, kawai dai yayi shirune dan Granny ɗin. Amma yata iya,
dole ta zagaya tabi umarni. Zama tai maƙure jikin murfin mota, zuciyarta
na mata hasashen ko ina little yake? Dan tayi tsammanin dashi zasuje
itakam. Yanda AK ya figa motar da ɗan ƙarfi yasata saurin dubansa, sai
dai da sauri ta ɗauke idonta ganin wani shegen harara daya watso mata
laɓɓansa na motsawa tamkar mai magana komai son cewa wani abu amma ya
gagara furtawa.
“Kai malam wlhy karka zubar damu, dan idan ka kasheni banga sake
ganin ɗan inno ba ALLAH ya isa mai kishin tsiya”. Hajiya iya ta faɗa da
iya gaskiyarta tana zazzagama AK masifa. Dariya Mommy ta sanya ganin
yanda AK ɗin ya hararo Hajiya iya ta mirror.
Zinneerah kanta sai da zancen hajiya iya ya bata dariya, amma sai
tai murmushi kawai tana kauda kanta gefe, dan zuwa yanzu ta fahimci
Yayansu da Granny ba’a haɗuwa ba’ai faɗa ba. Kuma itace mai takalar
faɗan shi kuma yayta mazurai, idan kuma ya magantu ya rama sau ɗaya yay
mata banza.
A nutse yake tuƙin cike da ƙwarewa da bin dokoki, sai da suka hau
titi sosai ya fara amsama Mommy maganar da take masa daga can baya,
hajiya iya na tayata. Zinneerah dai bakinta gum, sai strawberry sweet
ɗin dake bakinta take ta faman juyawa tana kallon hanya, tana jiran taji
ya tambayeta ina suka dosa taga ya ɗau hanyar anguwar kai tsaye.
Mamakine ya kamata sai dai babu damar magana, sunyi kusan rabin tafiya
taga ya gangara dasu wani super market, sai da ya samu waje yay fakin
sannan yay magana batare da ya kalli kowa a cikinsu ba. “Mommy muna zuwa
Please”.
Cike dajin daɗi tace, “A fito lafiya”.
Hajiya iya kam baki ta taɓe da ɗauke kai tana maganar da su dake
gaba ba jinta sukeba. “Muje”. Ya faɗa yana buɗe murfin ya fice.
Zinneerah bata fahimci da ita yakeba sai da Mommy tace, “Ɗiyata fita
kuje ku dawo kinji”.
Sai da Zinni taɗan waro idanunta waje, tace, “Mommy amma…..”
“Maza kije karyayi faɗa”.
Mommy ta katseta kafinma tace komai. Dole Zinneerah ta yunƙura ta fita
zuciyarta na dukan goma-goma. Idanunta kuwa harsun tara ruwa. Ina ita
ina shiga irin wannan wajen da Yayansu, itakam yau tana cikin abba-tuwa,
shikenan ya samu damar dazai cimata uwa akan ƙin bin maganarsa na saka
hijjab duk da Granny ce tai bell nata dai.
Koda ta fito da birkitattun idanunsa ta fara cin karo, ga
fuskarnan kamar zatai aman abinda kecin ransa. Ƙasa tai da kanta tana
ƙoƙarin haɗiye rauninta dake son bayyana. Ta fiske abinta da takowa inda
yake a hankali batare data sake yarda sun haɗa ido ba. Tana isowa wajen
ya miƙa mata handkerchief ɗin hannunsa, “Kwashe wannan abun na bakinki”.
Idanunta dake tara ruwan hawaye ta ɗago ta kallesa. ya zuba mata
hararar data sakata amsar handky ɗin babu shiri, cikin ɗan tura baki ta
fara kwashe ɗan janbakin dabai taka kara ya karya ba. Handky ɗin ta miƙa