MAKAUNIYAR KADDARA 47

 

*Page 47*

………..Cike da ɗokin zuwa ganin mmn sadiq dasu Aliyu Zinneerah ta 

shirya cikin wando da riga na parkistan red and white, sai gyale red 

data naɗa a kanta wanda ya fiddo mata ƙyawun da fuskrta ta ƙara. Kayan 

sun zauna mata ɗas a jiki kasancewarta mace mai mulmulallan jiki da 

ƙyawun surarta ta ƙuruciya. Babu wani kwalliya a fuskarta, amma ta saka 

lipstick kaɗan da yayma lips ɗinta ƙyau, dan tanada lips masu ƙyau da 

tsarinsu ya fita sosai yanda suke ɗaukar jambaki kamar wata babyn roba. 

Takalmi tasa mai ɗan tudu da igiya, sai side bag ɗinta ƙarama. A yanda 

tai ƙyau dolene ka kalleta ka sake kallo, ga ƙamshi tana bazawa dan 

Zinneerah gwanace wajen ɓarnar turare, idan ta samu batai masa da sauƙi. 

Ƴar jikkar data zuba kayanta kala biyu da tsarabar chocolates ɗin su 

Abdul ta ɗauka, dama hajiya iya ta fice ita tana falo tuni.

       Hajiya iya kawai ta samu a falon itama tana ƙoƙarin fita, samarin 

gidan tun bayan breakfast suka fice, hakama ƴammatan, su Jamal kuwa 

batasan ina suka dosaba. Hajiya iya dake ƙoƙarin fita tace, “Inno kashe 

tvn nan ki taho nasan Moddibo nacan ya cika da hasahinmu”.

     Da to Zinneerah ta amsa tana ɗaukar remote, bayan ta kashe tvn ta 

gyara labulolin sannan ta fito, ƙofar ta rufe dan masu aikin Hajiya iya 

basu dawoba, maybe sai zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu. Tafiya ta fara 

cikin nutauwarta tana ƙoƙarin ɗaura agogo data ɗakko a tsintsiyar 

hannunta da dosar inda ta hango Hajiya iya da Mommy tsaye da alama harda 

ita zasuje. Idonta bai lura da AK ba sai da tazo dab dasu tana ɗagowa da 

shi ta fara tozali yana ɓullowa daga ta gaban motar waya a kunnensa 

alamar magana yakeyi. 

     Kallon nata yayi dai-dai da saukar nasa idanun a kanta. A take ƴar 

sakewar data hango akan fuskar tasa ta ɓace ɓat, ya tsuke fuska yana 

mata kallon data nema kifawa saboda harɗewa da ƙafafunta suka shigayi. 

Saurin maida kanta tai ƙasa tana cigaba da takowa ranta fal nauyinsa da 

kwarjini, sai mita take a ranta kuwa. (Haka kawai bakama mutum komaiba 

yayta hararka, shi wai baya ganin waɗanan idanun nasa manya da ƙarfinsu 

yay yawa suna tsorata mutane)…….

     Da wannan tunanin ta ƙaraso Mommy dake kallonta tana ambaton, 

“Masha ALLAH ɗiyata irin wannan ƙyau haka”.

    Ƙasa Zinneerah ta ƙarayi da kanta tana murmushi, hakama Hajiya iya 

murmushi take tana kallonta itama. A bazata sukaji AK ya saki tsaki, 

cikin faɗa-faɗa yace, “K! Koma kisa hijjab”.

   Ba Zinneerah ba hatta su Mommy sai da suka dubesa, shiko ya fuske ya 

buɗe murfin motar ma a fusace ya shige abinsa. A sanyaye Zinneerah ta 

juya zata koma dan shi ba abin wasanta bane, waɗandama suka girmeta da 

shekaru masu yawa a gidan sunabin dukkan dokarsa balle ita ƴar jiya. 

Dakatar da ita Hajiya iya tayi ganin yanda tai ƙwalƙwal da idanu kamar 

zatai kuka, ta kamo hanunta tana matsawa saitin driver da yake zaune. 

“Haba Moddibo aimata haƙuri tunda ta rigada ta fito, ai kaga gyalen ya 

rufe mata jiki, kuma naga daga mota sai gida”.

       Shiru yay kamar baiji mi Granny ta fadaba, sai da ta ƙara leƙasa 

tana faɗin, “Oh nima yarfin daka iya zakamin?”.

    Idanunsa da suka canja launi ya ɗago ya dubi Hajiya iyan, “Amma 

Granny …….”

      “Dan ALLAH ai nace”. Tai saurin katsesa dan tasan shegen taurin 

kansa da dagiya akan abinda duk ya kafama sharaɗi. Badan yasoba ya ɗauke 

kai daga kallonta yan yima motar key. Murmushi Hajiya iya tayi da duban 

Zinneerah. “Kinga zagaya can kusa dashi ki zauna Inno, mu saimu zauna 

baya da Mommynku”.

      Kamar Zinneerah ta fasa ihu taji, dan yanda taga fuskarsa batai 

zaton ya haƙuraba, kawai dai yayi shirune dan Granny ɗin. Amma yata iya, 

dole ta zagaya tabi umarni. Zama tai maƙure jikin murfin mota, zuciyarta 

na mata hasashen ko ina little yake? Dan tayi tsammanin dashi zasuje 

itakam. Yanda AK ya figa motar da ɗan ƙarfi yasata saurin dubansa, sai 

dai da sauri ta ɗauke idonta ganin wani shegen harara daya watso mata 

laɓɓansa na motsawa tamkar mai magana komai son cewa wani abu amma ya 

gagara furtawa.

        “Kai malam wlhy karka zubar damu, dan idan ka kasheni banga sake 

ganin ɗan inno ba ALLAH ya isa mai kishin tsiya”. Hajiya iya ta faɗa da 

iya gaskiyarta tana zazzagama AK masifa. Dariya Mommy ta sanya ganin 

yanda AK ɗin ya hararo Hajiya iya ta mirror.

    Zinneerah kanta sai da zancen hajiya iya ya bata dariya, amma sai 

tai murmushi kawai tana kauda kanta gefe, dan zuwa yanzu ta fahimci 

Yayansu da Granny ba’a haɗuwa ba’ai faɗa ba. Kuma itace mai takalar 

faɗan shi kuma yayta mazurai, idan kuma ya magantu ya rama sau ɗaya yay 

mata banza.

      A nutse yake tuƙin cike da ƙwarewa da bin dokoki, sai da suka hau 

titi sosai ya fara amsama Mommy maganar da take masa daga can baya, 

hajiya iya na tayata. Zinneerah dai bakinta gum, sai strawberry sweet 

ɗin dake bakinta take ta faman juyawa tana kallon hanya, tana jiran taji 

ya tambayeta ina suka dosa taga ya ɗau hanyar anguwar kai tsaye. 

Mamakine ya kamata sai dai babu damar magana, sunyi kusan rabin tafiya 

taga ya gangara dasu wani super market, sai da ya samu waje yay fakin 

sannan yay magana batare da ya kalli kowa a cikinsu ba. “Mommy muna zuwa 

Please”.

        Cike dajin daɗi tace, “A fito lafiya”. 

    Hajiya iya kam baki ta taɓe da ɗauke kai tana maganar da su dake 

gaba ba jinta sukeba. “Muje”. Ya faɗa yana buɗe murfin ya fice. 

Zinneerah bata fahimci da ita yakeba sai da Mommy tace, “Ɗiyata fita 

kuje ku dawo kinji”.

     Sai da Zinni taɗan waro idanunta waje, tace, “Mommy amma…..”  

     “Maza kije karyayi faɗa”.

Mommy ta katseta kafinma tace komai. Dole Zinneerah ta yunƙura ta fita 

zuciyarta na dukan goma-goma. Idanunta kuwa harsun tara ruwa. Ina ita 

ina shiga irin wannan wajen da Yayansu, itakam yau tana cikin abba-tuwa, 

shikenan ya samu damar dazai cimata uwa akan ƙin bin maganarsa na saka 

hijjab duk da Granny ce tai bell nata dai. 

      Koda ta fito da birkitattun idanunsa ta fara cin karo, ga 

fuskarnan kamar zatai aman abinda kecin ransa. Ƙasa tai da kanta tana 

ƙoƙarin haɗiye rauninta dake son bayyana. Ta fiske abinta da takowa inda 

yake a hankali batare data sake yarda sun haɗa ido ba. Tana isowa wajen 

ya miƙa mata handkerchief ɗin hannunsa, “Kwashe wannan abun na bakinki”.

    Idanunta dake tara ruwan hawaye ta ɗago ta kallesa. ya zuba mata 

hararar data sakata amsar handky ɗin babu shiri, cikin ɗan tura baki ta 

fara kwashe ɗan janbakin dabai taka kara ya karya ba. Handky ɗin ta miƙa 

1 2 3Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button