NOVELSUncategorized

TARAYYA 37-38

37
Not edited
a gaggauce
Haske writers association
Shiru tayi tana kallonshi cikin nutsuwa, ta rasa ta inda zata fara  taimakonshi satar kallonta

yayi cikin nutsuwa, sannan ya sauke numfashi yace.

     
     Rayuwarsu a dajin wani irin rayuwa ce, mai ɗauke da soyayya da wani irin kulawa ba daga itaba har zuwa ita kanta. Mafi lokuta takan zauna tayita tunani anya ba wani kuskure bane yake shirin afkuwa na amincewa bil’adam, sai wani ɓangare na zuciyarta ya tuno mata tarin alkhairin da Jamal yake mata,
              Wani lokaci suna zaune ta kalleshi, a nutse kafin tace,
“Menene silar barowarka daga gida ka shigo wannan dajin har kake tunanin kashe kanka da rayuwarka.”
               Kirjinshine ya bada wani irin sauti, kura mata ido yayi yana qoqarin qin barinta gano yanayin daya shiga cikin daidaita  nutsuwa sai ya sunkuyar da kanshi cikin nuna baqin ciki yace,
Idan kika san abinda ya baroni da dangina sai kema kin gujeni, labarina ba labari bane sbd cike yake da bakin ciki.
  Dafe goshinshi yayi yana dauke kai yana girgizawa cikin damuwa mai tsanani sannan ya cigaba da cewa,
“Idan kika san koni waye guduna zakiyi gwara mubar maganar haka dan babu alkhairi a ciki.
         Wani irin qayataccen murmushi tasaki cikin qasaitar mulkinta dabatamasan tayiba tace,
Kayi min halacci zama tareda ni kana kula dani tamkar nauyina yana rataye akanka dan haka bazan gujekaba fadamin.
           Girgiza kai ya cigaba dayi yana cewa,
Karki so jin waye ni, karki so jin waye ni, labarina cike yake da kayan haushi da bakin ciki.
           “Ko baka  yarda dani bane, dan idan ka yarda dani ai babu abin bakin ciki a jin kai waye saima karin amintaka a cikin zamanmu.
 
Gyara zama yayi zuciyarsa cike fal da farin ciki dan abinda zai fada mata shine matakin nasararsu.
      “Kamar yanda na faɗa miki ni marayane bani da uwa bani da uba, amma akwai kawunaina, kasancewar iyayena sun mutu basu bar min ko ‘dayaba koda kuwa kaza ce yasa na zama abin tsangwama a cikin mutane, sannu a hankali na fara niman nawa na kaina sai dai…
           Kura mata ido yayi cike da jin ba daɗi da kuma hango yarda da Amana da tabashi sai ji yayi akaron farko bazai iya cika wani mugun kudiri a kanta ba, sunkuyar da kanshi yayi cikin wani irin yanayi na sanyin jiki wanda bawai dan maganar da yake mata bane sai dan akaro na farko da zuciyarsa ta hango masa  kuskure da suke shirin tafkawa ne Wanda zai iya bibiyarsu har jikokin jikokinsu na qarni mai zuwa.
         Cikin nutsuwa tasake kiran sunansa tace,
Karka damu nimai riqe sirrinkace.
   “A’a mineelik ina tsoron karki guje nine.
                “Ina tare da kai nace ka yarda dani.
    Gyaɗa kanshi yayi sannan yace,
“Nayi kokarin neman nakaina amma abu yaci tura daga nan kome na taɓa sai ya lalace kai ko kayan mutane na taɓa ya tashi aiki sbd baqin Jini da baqin qashin tsiya da’ake cewa inadashi daga nan mutane suka shiga jifana da mai kashin tsiya bani da albarka a rayuwa haka bai isheni ba sai na faɗa niman aure nanma mutane suka shiga korata a kofar gidajensu suna goranta min ynx waye zai yarda ya bani auren ɗiyar shi yanda tsiya da fatara ya kewaye rayuwata,
Qarshe ko qofar gidajen mutane sunhanani bi idan nabi qofar gidan mutum aranar saiya rafka babbar hasara tou tsangwama da qyama yasa nabar garin nashigo duniya shi yasa na shigo dajin nan sbd jin labarin ha’darinsa naso koma meyene aciki ya kasheni.
     Abin tausayi abin dariya yar karamar dariya tayi wanda ya bayyanar da jerun kyawawan hakoranta farare.
                   Ganin irin kallon da yake mata yasa ta ɗan rufe bakinta cike da qaunarsa mai qarfi dake zuciyarta tace,
“Tabbas akwai abin dariya a rayuwar bil adama sbd kamar munfisu yarda da qaddarowar Allah ne.
Kallonta yayi da sauri cikin rawar murya yace,
Mekike nufi da bil adam ke kincire kankine daga bil adaman?
Kallonsa tayi cikin takaicin zancen datayi ta girgiza kai cikin son gyara zancen tace,
Dukanmu bil adama ne saidai wasunmu kamar basuda daukar qaddara sbd banga abin gudu da qyama ananba.
       “Hmm kece kike ganin haka amma abin ba haka bane, aiku mata baku ɗauki kome da muhimmanci ba, tunda ba damunku abin yayi ba.
Girgiza kai tayi ni na amince zan aureka a duk yanda kake sile ‘daya sun wadaci sadakin auren.
     Mikewa yayi a razane tare da tsorata sbd baitaba kawo wata maganar aure atsakaniba yace,
Banda komai dazan inganta rayuwarki na kare martabarki amtsayin mijinki dan haka bazan iya lalata miki rayuwa ba.
             Jikintane yayi matukar sanyi har tana dana sanin fada masa hakan sbd har cikin ranta takejin damuwarsa sbd tausayinsa mai qarfi da yayi wasi zuciyarta kamu tareda soyayyarsa mai qarfin gaske dan haka zata inganta masa rayuwa,
Zata basa kaf arzikinta saidai zata daukesa sunkoma duniyarta rayuwa acan zaifi musu dadi.
             
Ahankali ya furta idan har kin amince da aurena a yanda nake dinnan tabbas zan sadaukar da rayuwata gurin nema dan inganta miki rayuwa.
  
Yarda dashi yasa take kwanciya tayi baccinta batareda sakin dukkanin jintaba shikuma yana ganin tayi nisa a bacci
           yasaci jiki ya nausa yamma da saurinsa da gudunsa sai tsakiyar dare sosai ya isa inda su Ajani suke tun daga nesa yake musu kukan wata tsuntsuwa dansu gane shine tafe dan karsu harbo masa hari daga nesan.
suna jiyosa cikin bacci duk suka  mike
Suka fito rumfarsu yana isowa gabansu ya zube a wahalce yana fitarda numfashi tareda sakin ajiyar zuciya.
       Amarine ya rungume shi cike da kewar kanin nashi yace,
“Da fatan anyi nasara?
                Murmushi yayi ya nemi guri ya zauna, sannan yace,
Nasara tazo ne tareda matsala sbd tace na aureta.
   Nan ya faɗa musu komai.
                 Shiru sukayi kafin Haji yace,
    Toh ba zaiyu bane mu karɓi dukiyar da karfin cin tuwo basaika auretaba.
Wani mugun kallo amari yasakar masa zaiyi magana yonas dan boka yace,
Meya hana kai kaje gurinta sauka karbo da qarfin cin zaki bama na tuwo ba.
Zaburowa haji yayi tareda fisgo takobinsa mai tsananin kaifi ya nufi wuyan yonas Jamal yayi saurin tarewa yace,
Ba yanzu zakuyi wannan ba kubari mukarba daga baya kun kashe kanku,kafin ya kalli haji din cikin ido da Wani irin kallon banza dayayi masa cikin rashin jin daɗi abinda yace,
      Lallai kusani koda barazana bazan karɓi dukiyarta ba sai da amincewarta.
   Arazane suka hau kallon juna cikin wani irin mamaki da tabbarwa da maganar da boka yafada musu bayan tafiyar Jamal din da dayansu yaje.
ganin irin kallon da sukewa juna yasa shi shan jinin jikinshi sbd kuwa ya tabbatarda akwai wani abu dasuke boyewa.
Kuna qoqarin boye min wani abune akan mineelik?
    Babu Wanda ya basa amsa sai kojo dayace masa,
Ko ‘daya kashirya gobe zamuzo amatsayin nemanka muke daga nan zamu daura auren muyi abinda yakawo mu muje wata harkar sbd idan muka tsaya sanya zamu qarasa rayuwarmu ne a wannan dajin.
     Juyawa yayi zuciyarshi bata aminta dasu ba ya fice yana tunane tunanen abinda suke boye masa dan kuwa yasan tabbas akwai abinda suke boyewa.
          Bayan tafiyarshi Kojo ya kalli  Ajani cikin bushewar zuciya da takaici yace,
   Aqoob yayi gaskiya na cewar Jamal zai iya fara sonta na hango damuwa a cikin idanunshi ba jarumta ba kuma da zaran yasan da kudirinmu akan mataqin qarshe na mallakar dukiyar toh ba zai taɓa yarda damu ba kuma komai zai lalace.
      Shiru sukayi dukkansu sbd bazasu taba bari banzar soyayyarsu ta kaisu ga rasa abinda suka sadaukar da rayuwarsu gurin nemaba.
Koda ya isa asuba tayi har haske ya’dan fara yayi saurin kwantawa yana wasi wasi akan mineelik da abinda suke boye masa,
hango wautarshi yayi da ya amince da bukatar ya yaudareta sbd yadaura ko a tsakaninsa da bil adama yar uwarsa ne haqqi baya barinka bare sarauniyar aljanu mafi hadari ko acikin sarakunan.
yana gurin har gari ya waye kafin tafito ya shiga daji nima musu abinda zasu ci.
          Koda ya dawo taga rashin walwala akan fuskarshi tambayarshi tayi ko akwai wani matsala yace,
Babu kai tsaye yana juya mata baya sbd bayason kallon fuskarta yanzu jin yake zuciyarsa na karyewa da abinda suke shirin yi yanajin kamar bazai iyaba.
         Shiru tayi ta cigaba da zama tana satar kallonshi da zaran sun haɗa idanu zata ɗauke kai tana murmushi haka shima yake qaqalo murmushin qarfin halin.
           Kusan ita tayita janshi da hira, har ya sake da ita suka cigaba da hidimarsu can suna zaune sai suka jiyo sautin muryan mutane na doso inda suke mikewa tayi ta koma bayanshi tana leka inda take jin muryan mutanen.
Shikuwa dayasan da zuwansu bai wani nuna damuwaba saidai fargaba da wasi wasin abinda sukazo ayi wato auren.
Tabbas yanajin wani irin tsoro, fargaba shakku da wasi wasin aikatawa.
Cikin nutsuwa suka tunada gargadin boka aqoob dayace saisunyi matuqar taka tsantsan karta zargi wani abu ko taganosu dan kuwa rayukansu zasu rasa dukkansu idan aka samu matsala shiyasa
       Su ajani ne suka iso har inda suke ja yayi da baya a tsorace su kuwa suka diro raqumansu da wani irin tsuma da far in ciki jikin na rawa suka qaraso gabansa cikin babbar murya kojo yace,
Jamal kasan abinda kayi da halinda kasamu ciki daka gudu aka rasaka?
Fiyeda kwana hudu muna yawo cikin dajin nan nemanka bayan mun share satittika muna yawon qauyuka nemanka mekakeyi wannan hadararen dajin….?
    Kuka ajani ya saka cike da bakin ciki yace,
“Yau da ɗan uwanmu na raye ai kafi karfin wulakacin badan haji yace mu shigo ta daji ko kazo ka rataye kanka ba,
Gidanmu ya qone qurmus bayan barowarka shiyasa muka tabbatarda zamanka a gidanma kuma wata rahamace kayi hakuri mu koma musan yanda zamu dora itace muyi wani gidan bazamu sake bari a wulaqantakaba zamu samo maka mata mu daura maka auren dakakeso.
          “Babu inda zani dan ni na sami wacce zata aureni da zuciya ɗaya bata damu da dukiya ko arziki ba.
Cikin Sauri da ‘doki yonas yace,
Zamu aura maka ita yanzu dai kazo muje gida idan munje a daura maka ita acan tunda yanzu idan anyi bakada gurin sakata.
        
    Shiru yayi alamar nazarin zancen kamar gaske.
Ita kuma cikin nutsuwa takallesa ganin yashiga tunani ta dafashi ahankali ya matsa mineelik ta bayyana daga bayanshi.
   
  A tsorace sukayi baya zuciyoyinsu na rawa saidai jaruman gaske ne bazasu bari kyawunta da kwarjininta ya rikitasu ba.
      Cikin sauri kojo yace wannan ba irin matarka bace bazata zauna dakaiba idan taga talauci zai illatata.
    
“Na rantse da abin bauta bazan barta ba ina sonta kuma zan aureta idan kuka ce bazaku barin na aureta ba zan kashe kaina na huta.
   Cikin fusata Amari yace.
“Ka daɗe baka mutu ba wannan matar tafi karfinka ka nemi wata mana kokuma mu munema maka wata.
      Ahankali ta matso kwarjininta da wata irin haiba dake fitowa daga gareta na girgiza zukatansu saidai buri da kwadayinsu yasa suke kannewa cikin jarumtarsu cikin wata irin murya mai dadi tace,
Ku auramin shi nikuma na muku alqawarin taskar arzikinda dar qarnin qarshe zuriarku bazatai talauciba,
Ina sonsa zan auresa ahaka kuma nayi alqawarin ko bayan mutuwa zan qaunace bazan barsaba wannan alqawarine daga sarauniya datafi kowace sarauniya mulki,
wannan son dayake min yafi min kome a duniya.
     Wani irin kallo sukayiwa junansu cikin gamsuwa da burinsu yazo a sauqin dabasu taba tsammaniba.
Kojo ne ya matso gabanta suna fuskantar juna cikin rashin tsoro yace,
      Mun amince zamu daura muku aure a yanxu basai anje koina ba saidai bawai dan kinada arzikin dazaki bamuba dan da alama kema nema kikeyi.
     Murmushi tasaki ahankali tareda kallonsa takalli sauran dakuma raqumansu tace.
Idan sarauniya tayi alqawari bata canxawa,
Alqawarinta kamar rubutu ne akan dutse har abada baya canxawa.
        Murmushi yonas yayi tareda kallonta cikin ido yace,
Mukuma alqawarinmu idan muka dauki burin abu kamar rubutu ne ajikin dutse baya goguwa sai muncimmasa.
Murmushi tayi tace,
Buri da alqawari basa haduwa sbd ‘daya saiya danne ‘daya yake tabbatuwa amma Ku sani zaku tuna hakan wata rana.
Kallonta sukayi a ‘dage kafin amari ya kalli Jamal daya qura musu ido cikeda tunani kala kala aransa game dasu yace,
Yanxu za’a daura aurenka da sarauniyar ranka saidai kasani soyayya gubace mai kaifin gaske kafadawa ‘yaya da jikokinka wannan.
Shigewa tayi tantinsu tana jin wani irin yanayi na farin cikinda bata taba jinsaba sbd tana yiwa Jamal wata irin soyayya da qauna mai qarfi dazata iya sadaukar da komai kansa ciki harda rayuwarta.
Atake suka rabu biyu suka wakilci ango da amarya aka daura auren da sadakin sile ‘daya.
Bayan daura auren ne sukace zasu tafi su dawo sbd boka aqoob dayace idan andaura suzo yabasu matakin qarshe.
Bayan tafiyarsu da daddare yana zaune ya kafawa wutar daya kunna ido shikadai gabaki daya zuciyarsa cikin wata irin dana sani da qunci take sbd abinda yakeji gameda mineelik bazai iya cutatar da itaba saidai kuma bazai iya fada mata komaiba ko yayi gangancin bari tagane sbd rayuwar ‘yan uwansa dan yasan shi tana masa so mai tsananinda bazata iya kashesaba ko illatasa.
Ahankali yakejin sautin qarar sarqar qafa da taku na nufosa tareda wani irin haske da niimtaccen qamshin mai tareda sanyi na shigarsa ya ‘dago ahankali ya qurawa gurin ido baiga fuskartaba sbd wani irin kyallin zinari dake fita daga wuyanta da kanta tareda damtsen hannunwanta da qafafunta sbd adon sarqunan dake jikinta.
Saidatazo gaf dashi ta tsaya cikin ainihin suffarta tana sakar masa wani irin murmushi mai qayatarwa ta miqa masa hannunta cikin wata irin murya mai dadi tace,
Ina tayaka murnar zama attajirinda babu kamarsa a wannan qarnin,
Ina taya murnar zamtowa mijin sarauniyar da babu tamkarta a wannan qarnin,
Soyayyace farko kuma soyayyace qarshe,
Zan rayu dakai na bauta maka domin Kaine sarki a masarautata saidai cin amana,qarya da yaudara basa cikin soyayyata basa cikin abinda nake dubawa amatsayin kuskure koda ga abinda nafi so ne.
Murmushin takaicin rayuwarsa yasaki sbd yasan tunda ya bari zuciyarsa takamu da soyayyarta rayuwarsa na tsaka sbd bazai iya rabuwa da ‘yayan uwansa ya 6ata musu buriba sannan bazai iya bari acutatar da itaba.
Cikin sanyin murya data nuna zallar damuwar dayake ciki yace,
Wacece ke?
Ahankali ta furta,
Sarauniya mineelik,aljanarda aljanu da mutane suka buri da fatar gani kuma matarka ta har mutuwa.
Rintse ido yayi akaro na farko yaji jarimtarsa ta 6ace ya sauke kai cikin rawar murya yace,
Meyasa kike sona har haka bayan bakida cikakken sani akan abinda yake zuciyata.
Ahankali ta ‘daga hannuwanta sama tayi budesu idanuwanta akansa tace,
Barka da zuwa masarautar mineelik.
Miqewa yayi cikin wani irin mugun tsoro da firgici yake kallon koina yana jujuyawa kamar wuyansa zai cire sbd ganinsa Cikin wata irin masarauta mafi girma da kyawun dabai taba ganiba duk yawon duniyarsu.
Adon ne zaibar zinari da wani irin gini mafi kyau da tsari
Wasu irin kujeru ne a Jere na sarauta sunsha ado wani irin ni’imtaccen kamshi na tashi daga  yanayin jerin kujerun da tsarinsu yasa ya tabbatarda nan ne asalin fadar wato dakin taron sarauta.
Wani irin qyalli yaringa gani yana hasko bayansa yayi saurin Juyawa a kidime yaja da baya tareda zubewa qasa kan qafafunsa yana kallonta cikin wani irin tsoro da firgici..
Zaune take kan karagar mineelik tafito masa Zak amatsayin sarauniyarta atake wani irin tsoronta da firgicin dabai taba jiba yasashi sauke kai yana girgizawa.
Ta bayansa yaji andafasa a zabure ya juya yaga itace yayi saurin kallon karagar yaga bata kai ya juyo yasake kallonta ta sakar masa murmushi mai sanyi tace,
Banason sanin sirrin dake zuciyarka sbd idanuwanka sun tabbarmin da abinda nake nema daga gareka wato soyayya mai qarfi dan haka masarautar mineelik takace kaima daga yau dakazama mijin mineelik.
Murmushin baqin ciki yasaki tareda miqewa ya juya mata baya cikin tsananin damuwa yace,
Idan ‘yan uwana sunzo basu ganmuba zasu…….
Masarautar mineelik ta bayyanane ga dukkanin Wanda ke wannan nahiyar sbd duk girman wannan dajin da mutum zaiyi tafiyar kwana bakwai bai gama fitaba acikinsaba ba daji bane duk girman masarautar mineelik ne dan haka ayanxu mutane na kusa da nesa suna hanyar zuwa kallon masarautar dabasu taba gani ba ta mineelik data bayyana ga kowa.
Zai sake magana taga duk cikin tashin hankali yake mai tsanani
Ahankali ta riqo hannunsa cikin nata tsananin laushi da ni’imar fatarta yasashi kasa magana yabita tamkar raqumi suka nufi turakarta datafi kowace kyawu.
#mamuhgee
[6:47 PM, 7/30/2019] +218 94-4138736: TARAYYA
wattpad@mamuhgee
   Haske writers association????
38
a gaggauce
not edited
Haske writers association.
A gaggauce
Not edited.
Zaune suke dukkaninsu gaban boka aqoob dayayi shiru cikin jinjina mataki na qarshe dazai fada musu sbd aljanun dayake aiki dasu sune suke fada masa komai gameda sarauniya mineelik sbd suna cikin maqiyan farko na sarki penya.
Kallonsu yayi ‘daya bayan daya
Dukkaninsu kowanne ashirye yakeda karbar matakin qarshe ‘din sbd yanxu sunkai iya maqurar ganin cikar burin sbd Jamal dasukaga yafara shiga hanyarda bazata bulleuba su duka.
Wasu irin qananan wuqaqe farare tas guda shida masu kamar azurfa ya fitar daga wani irin rami ya ajiye agabansu tareda kallonsu yace,
Wannan wuqar dafin jinin penya ce wadda duk duniya ita kadaice zata kashe sarauniya mineelik,
Kowannenku zai soketa da wannan wuqal agurare daban daban saidai kuma dafin zai illatatane bazai kashetaba matuqar ba masoyintane ya soketa da ita kuma ya zamto shine zaiyi mata suka ta qarshe da wannan wuqar to tabbas wannan ne kawai zai kasheta…idan Wanda takeso fiyeda komai bai soketaba to tabbas kusani sukarku zata illatane amma bazat mutuba Wanda kunsan rashin mutuwarta na nufin rayuwarmu mu duka dan haka wannan matakin na qarshe yafi kowanne hadari.
Cikin zalama da qosawa kojo yace,
Jamal bazai taba qi hakan ba koya gardama zamuyi amfani da qarfinmu mu sakasa.
To bayan wannan kuma idan ta mutu to masautarta zata bace daga duniya babu Wanda zai sake ganinta saidai idan Wanda take tsananin so ya sadu da ita to tabbas idan ta mutu masarautarta tariga ta bayyana har abada tazama ta bil adama ta tashi daga duniyarsu.
‘Daure fuska amari yayi zaiyi magana da sauri kojo ya dakatar dashi yana cewa,
Munriga munkawo yanzu babu abinda zai gagara yamaida mu baya ga wannan tafiyar Jamal dole zai sadu da sarauniya mineelik.
Wasu sabbin madaurin damtse na wani tsarin boka yabasu kowannensu ya daura tareda ‘daukar wuqa ‘daya na Jamal kuwa cikin fata amari ya nade masa ya soka qugunsa suka miqe.
Yonas dake qoqarin soka tasa cikin takalmin fatar damisarsa yaji hannunsa na wani irin qaiqayi yayi saurin dubawa zai sosa saiyaga rubutu na bayyan a hannun nasa yayi saurin kallon mahaifinsa yaga idanuwansa rufe alamar saqone yake ruboto masa dan sanar dashi wani abin.
Da sauri ya maida kallonsa ga tafin hannunsa yafara karanta saqon.
“” idan buri ya kammala kawai da datti ake ashare komai da komai””””
Jinjina kai yayi cikin rashin tausayi yakalli bayansu kojo dasuka gabansa dan yafahimci saqon meyake nufi yana nufin idan ankammala su kashesu nan take.
Suna fitowa qofar gidan boka aqoob sukaga wani irin gini mai matuqar tsawo da kyawu tareda girman dabasu taba ganiba mutanen gari sai fitowa kallo akeyi ana nufar hanyar da ake hango masarautar
Atake cikin gaggawa suka hau raqumansu suka nufi hanya sai tun daga nesa suke hango babu daji sai masarautar kawai da girmanta yasa ta zamto kamar tana cikin ganin ne.
Suna isa bakin qatuwar qofa mai girman gaske suka taru su biyar suka tura qofar tabude suka shige cikin wani irin mamaki mai rikita tunani da nustuwa sbd girma da kyawun masarautar babu kowa koina tsit saidai komai fes tamkar yaune aka ginata.
Harabar gurin suketa rarraba idanu suna kallo cikeda far in ciki mara misaltuwa sbd burinsu yacika saura qiris su mallaki sauran duniyar.
Wasu furanni masu qamshi yonas ya tsinka ya shinshina ya lumshe ido cikin farin ciki ya daka wani tsalle tareda sakin ihun farin ciki.
Kojo kuwa mahaukaciyar qofar daya tabbatar ta fadar da karagar ke cikine ya nufa ya saka hannu biyu yatura qofar ta wangale atake dukkaninsu sukai mutuwar tsaye ganin karagar dake wani irin daukar ido duk da kasancewarta kalar baqa mai adon zan zinari.
Girman fadar suka kallon cikin wani irin farin ciki madaukaki da sauri suka nufi kujerar kusan atare kowanne na burin kaiwa ya hau Jamal yasha gabansu cikin wani irin yanayi na damuwa da bacin rai.
Tsayawa sukayi dukkaninsu kallonsa saidai ganin kamar hawaye cikin idanuwansa yasasu tamvayarsa cikin gaggawa.
Yaja baya tareda zubewa kan gwiwoyinsa murya na rawa yace,
Ina roqonku da karku cutatar da ita domin kwadayin arzikinta kubari zankarbar mana ta hanya mafi lalama da yardar ta.
Wucesa amari yayi ya nufi karagar yana banzatarda zancensa sbd har abada babu Wanda zai shiga tsakaninsa da wannan taskar arzikin.
Dukkaninsu babu Wanda yabi takansa sbd babu alamar gudu ko ja da baya a wannan alamarin nasu.
Cikin wani irin gunjin kuka ya durqusa a gurin suka waiwayo suka kallesa ajani ne yadawo gabansa ya tsaya cikin kulawa yace,
Meke faruwa munyi alqawarin duba damuwarka idan kafada.
Kallonsu yayi cikin wani irin gunjin kuka mai ciwo ya girgiza kai yana cewa,
Ayau na hada shimfida da sarauniyar aljanu Wanda na tabbarda hakan wata sabuwar qaddara rayuwa ke nufi dani saidai kuma hakan y juyar da ra’ayina bazan iya cutatar da itaba sbd a duniyarsu hakan wani babban alamari mai tsananin girma yake nufi dan haka ta tafi wani gurin bauta bazata dawoba sai bayan kwana uku sbd abinda yashiga tsakanina da ita zatajene domin dawowa duniyata gaba daya dan haka nake roqonku karkuyi abinda zai barmu da masifar da bazata tsaya akanmuba kawai.
Cikin tsananin farin ciki da jin dadi suke kallonsa atake dukkaninsu suka sheqe da dariya mai qarfi cikeda farin cikin ganin komai ya tabbata qiris yarage.
Kallonsu yake daya bayan daya yana mamakin dariyarsu cikeda fargaba.
Sake kutsawa cikin masarautar mai girma sosai sukayi kowanne na taba abinda ya burgesa duk wata zalamarsu da kwadayinsu ya fito nan suka ringa shiga dakuna da gurin shaqawata da sassa daban daban babu tsoron komai aransu.
Shikuwa ke6e kansa yayi daga garesu yana zullumi da tunanin manufarsu daya kasa ganowa yadai San dole sunada qudirin cutatar da ita.
Ranar data cika kwana uku a makeken lafiyyan dakinta dake turakarta ta bayyana lokacin yana zaune tsakiyar daki cikin tsananin tashin hankali da damuwa.
Kallonsa take cikin tsananin farin ciki da wani irin yanayin jin dadi takira sunansa cikin qauna da soyayyarsa.
Da sauri ya miqe tareda juyowa bata tsaya bata lokaciba ta rungumesa da qarfi tana sake ajiyar zuciya cikin farin cikin kasancewa dashi har mutuwarsu.
Rintse ido yayi sbd tuno abinda yafaru ayau tsakaninsa da ‘yan uwansa.
Wuqar da boka yabasu suka fitar masa da yasa suka basa tareda yimasa bayani yayi saurin wurgi da wuqar yace,
Aikuwa idan har nine Wanda kawai zai iya kasheta har abada bazata mutuba.
Cikin takaici kojo ya kallesa yace,
Baka isa ka rusa mana shirinda muka share shekara da watanni muna sadaukar da rayuwarmuba.
Kabarsa yagama bulayin shirmen son wadda ba jinsinsa idan yagama shirmrn mafarkin zaidawo hayyacinsane lokacinda tagano manufarsa ta aikasa gurinsu dede”””cewar amari dayafi hasala da zancen.
Yonas ya sake dauko masa wuqarsa ya saka masa cikin hannunsa yace,
Idan bakayiba mu zamuyita sukarta harsai ta mutu koda zamu dauki shekara dari ne saidai kasani tana warkewa karasa yan uwanka dasune rayuwarka har abada sbd kashemu duka zatayi kuma harda kai aciki.
Ajani dayafi kowa qaguwa dasu mallaki masarautar ya matso gabansa ya tsaya cikin tabbarwa yace,
Zabi yarage naka kazaba ‘yan uwanka ko soyayyarda bazata doreba har abada sbd ba jinsi dayaba dan haka kashirya tana dawowa zamu qarashe aikinmu idan baka yi yanda akaceba kana kallo zata kashemu.
Tafiya sukayi sukabarsa tsaye da wuqar ahannu yana kallo cikeda wasi wasi saidai bazai iya bari yarasa yan uwansaba sbd sune rayuwarsa sunayiwa juna wani irin so da qauna mai qarfi.
Zamewa yayi daga jikinta jin kamar wani abu a gabanta kallo daya yayi mata yayi baya da qarfi  cikin wani masifaffen tashin hankali sbd ganin qaramin ciki ajikinta.
Matsosa tayi cikin farin ciki tana Murmushi zatai masa magana yasake ja baya tareda ficewa da sauri.
Dayake safiya ce sosai sauran babu Wanda yatashi suna sassansu kowanne yazabi sashensa sunacan suna hutawa tuni suka samo masu hidima.
A cikin fadar ya shiga ya tsaya jikinsa na wani irin rawa zufa na karyo masa takoina
Ta bayyana a gabansa tareda riqo hannunsa ta ‘dora akan cikin ahankali tace,
Cikine dani kuma……..cak ta tsaya da maganarta jin sukar data sauka ajikinta daga bayanta
Cikin wani irin yanayin azaba ta juyo dan ganin waye taji wata sukar a gefen cikin duka biyun.
Jajayen idanuwanta ta ‘dago cikin radadi da azaba takallesu amari ne da yonas,
Jinine ya fara fitowa daga hancinta ta ‘damqe hannun Jamal da idanuwansa suke zubarda wata irin qwalla da kuka mara sauti,
kojo da ajani tareda haji suka tsaya gabanta tareda ‘daga wuqaqensu suka soketa da qarfi aciki lokaci ‘daya.
Tasake damqe hannun Jamal tareda fitarda wani nishi mai qarfi da wata irin azaba atake Jini ya balle mata mai matuqar yawanda basu taba ganin irinsaba hakama bakinta yafara fitarda jini ta yanke jiki ta zube bakin karagar mineelik tareda kallon Jamal daya fiddo wuqarsa yana hawaye ta lumshe ido cikin tsananin baqin ciki mai tsananin gaske sbd ta tabbatarda cin amanarta da yaudararta sukayi ahankali tabude baki daqyar ta furta,
Duk iya alqawari da soyayyar danake maka meyasa kazabi cuatatar dani.,
Karka kasheni kabarni na rayu kodan cikinka dake jikina nikuma zan maka alqawarin sabuwar rayuwa,
Haryanzu zuciyata nasonka ko ka kasheni bazan daina sonkaba…….
A hankali ya ‘daga wuqar ya nufi qirjinta yana kuka yashigarda wuqar qirjinta da qarfi.
Atake tasaki wani irin azababen nishi mai qarfi daya amsa masarautar gabaki daya ta kallesa idanuwanta na fitarda wasu irin hawayen ahankali ta bude baki tace,
Meyasa????
Cikin izza ajani yace,
Sbd karagar mineelik.
Kallon Jamal tayi ya juya mata baya yana sake sakin sabon kuka ta kalli karagar tasaka hannu ta debi jininta dake zuba ta zubawa karagar ta lumshe ido sbd wata irin azaba dake ratsata cikin,
Hawayen azaba tace,
Ayau ni sarauniya mineelik ‘yarda,soyayya dakuma amincewa yasa bawa mafi soyuwa a rayuwata ya kasheni ya zubar da jinin ‘dana ko ‘yata dan haka haqqin jinana bazai taba barin bibiyarku ba har qarnin qarshe harsai ranarda jini ya maida jini maimakon jini dan haka nayiwa mineelik baki zata zame muku masifa mara magani da ganewa,,,,daga yanxu jini ya ringa zuba kenan amaimakon jinin ‘dana.
Kallon bayan Jamal tayi lokacinda taji ko maganar takasa sbd tsananin azaba ahankali ta furta nabar maka dukiyata sbd sarauniya bata alqawari ta ‘daga saidai bazakaji dadinta ba……
Cikin rashin imani yonas ya daga wuqar ya soke mata maqogoro atake ta saki numfashi da ajiyar zuciya ahankali jikinta ya saki ta bace 6at.
Zubewa agurin Jamal yayi yana wani irin kuka mai sauti.
Cikin tsananin farin ciki da murna amari ya nufi karagar zai hau boka aqoob ya bayyana gabansa cikin wani irin murmushin mugunta yace,
Nine mai hawa wannan karagar duk Wanda ya……..bai qarasaba sukaga kansa ya fille yafadi qasa.
Kojo sukaga yani a bayansa kenan shine ya fille masa kai
Cikin murna ajani ya nufi kojo zaiyi magana yonas ya sha gabansa cikin tsananin baqin ciki da zafin zuciyar ubansu da aka kashe yana ‘daga wuqarsa zai cirewa ajani kai aka soke masa zuciya daga bayansa saida takobin ta fito ta qirjinsa.
Wanda amari ne yayi wannan aikin.
Haji na ganin haka ya juya da gudu ya fice yace,
Kusani wannan gabace da masifar dazata zo har zuriar zuriar bayanmu.
Cikin zaquwa amari ya juya zai hau karaga Jamal ya buge qafafunsa tareda miqewa ya isa karagar kai tsaye ya hau ya zauna tareda kallonsu da jajayen ido yace,
Nine magajin mineelik dan haka nine zanyi sarautar duk Wanda hakan baimasaba yana buqatar hada kwanji dani.
Kallon juna sukayi ga mamakinsa saiyaga sun nuna amincewarsu.
A ranar Jamal ya karbi sarautar mineelik kuma aranar aka dauki masu hidima ‘Dari da hamsin atake masarauta ta cike da mutan gari ko sati ba’a rufa dukkaninsu sukayi auren mataye uku uku lokaci ‘daya,
Mineelik cikin qanqanin lokaci tazama masarauta mafi girma da iko a wannan qarnin musamman data zama babban gari mafi girma
Kafin mulkin Jamal yaqare saida mineelik takoma itace a tsakiyar babban birnin Ethiopia sbd cika da garuwan qasar sukayi koina ya cike tazama babbar qasar cin kasuwar jiragen ruwan dake wajen gari.
Mulkin Jamal wani irin mulkine na daukar rayuka ba abakin komaiba,
Suna arziki da yawa da girma babu kamar mineelik a wannan qarnin sbd garin da masarautar take ko zakayi wata daya kana yawo bazaka zagayesaba.
Duk wani burinsu Jamal dasu kojo yacika saidai rashin haihuwar ‘yaya maza daya addabesu daga qarshe har sultan jamal ya rasu bai samu ‘da namijiba sai mata
Bayan saukarsa sultan kojo ya hau shima duk tsawon shekarunsa harya mutu bai haifi namiji ba dukkaninsu sunyi mulki ajani kawai yasamu namiji ‘daya acikin ‘yayansa Wanda bayan rasuwarsa shima dansa sultan amed yahau bayan sultan amed sai sultan nurin,dagashi sai sultan abaass da haka mulkin yayita zuwa qarni qarni so ‘daya akayi assultana Wanda mulkinta karagar tafi ta6ata kasanewarta mace,
Alokacin mulkin assultana ankashe rayukane tamkar dabbobi sbd jini daya yawaita a mulkinta sbd iya zubar jini iya qarawa karagar qarfi qarshe abin taba kwaqwalwarta yayi ta samu tabin hankali ahaka ta rasu.
Da haka ‘daruruwan shekaru suka shide musuluncin gske yashigo cikin qasar suka karbesa sosai inda a yanxu suna cikin qasashen dasukafi yawan musulmai duk da wasu haryanxu suna aladar bin bokaye.
A yanxu muna wani lokacine na waye da ilimin zamani tareda qarni mai dadi sbd rayuwar ilimin boko dana addini daya shiga koina ya wadata.
Sultan abdulshams sarkine mai tsananin son kansa fiyeda duk wani abu a duniya har yayansa har matansa shidai arayuwa kansa yasani shiyasa yadau alqawarin karya alkadarin mineelik domin yaci gaba da mulkinta shikadai sbd shikansa yaxubarda jinin alumma fiyeda qima dan haka yanason mulkin bazai barshiba shiyasa yayi bibiyar yanda zaiyi yagano ma’anar kalmar,
“”””jini ne zai wanke jini domin jini”””” a cikin littafin tarihin masarautar mineelik.
Ma’ana soyayyace tamkar wadda takewa jamal mai hadeda jinin cikinta zata karya wannan masifar shiyasa azamansa da bawansa bulama ya fahimci wata irin qauna da soyayyarsa da matarsa yayi amfani da qarfin ikonsa yasa jakadiya ta ware musu wata ‘daya suna kebantuwa da juna ranarda Jakadiya tagano asma’u ta samu wani cikin tasanarda sultan nan yafadawa sultana zaarah nufinsa bawai danta hanaba saidanta kawo masa asma’u gaban karagar da safe daidai irin lokacinda aka kashe sarauniya mineelik.
Badan sultana tasoba saidan tsananin iko da barazanar sultan agareta ranar wata laraba da safe tashirya tace Jakadiya tasa asma’u cikin ‘yan rakata gurin sultan kai gaisuwa.
Koda suka isa tace asma’u tabita suna shiga suka rararda bulama tsaye yana jiran fitowar sultan nan sultana tashiga gurinsa tabarsu tsaye suka qurawa juna ido cikin qauna da soyayyar junansu ya kalleta cikin nutsuwa yace,
Idan kika haihu ko bananan kisawa yaron suna bilal idan mace ce kisaka mata asma’u.
Murmushi tayi zatai magana sultan da sultana suka fito sultan yakallesu kafin yayi magana Jakadiya tashigo daukeda qaton tray daukeda kofuna guda biyar takai gaban sultana da sultan suka dauka ta juyo ta miqawa bulama ‘daya asma’u ‘daya babu musu suka karba sultan yace,
Wannan taya murnace ga bawana bulama na ‘yantasa daga yau.
Cikin tsananin farin ciki suka zube qasa suna godia sbd sunsan nesa tazo kusa sunkusa komawa qasarsu kenan.
Cikin tausayi Jakadiya tace,
Kusha kyautar sultan Ku godewa Allah.
Da sauri suka kwankwade lemon suna sake godiya suka miqe suka fice sultana ta sauke numfashin damuwa da tausayinsu tareda baqin ciki da dana sani Wanda take kallon kanta amatsayin wadda takashesu shiyasa take tsananin qaunar yarsu.
Acikin daren bulama ya rasu da ciwon ciki asma’u ma ta rasu da cikinta dabata haifeba Wanda babu Wanda yasan dashi saisu dasukai aikin saidai abinda basu saniba shine kozaku sadaukar da rayukan masoya ‘Dari to masifar mineelik bazata karyeba sai masoyan dasuka kasance sunada jini da masarautar.
**
A matuqar gigice ta farka a firgice suka miqe tsaye amatuqar firgice suna watsa ruwan magani sbd basusan a yaya ta farko ba.
Maheer dake zaune hannunsa cikin na suhailat ya zare ya miqe ya nufi gadon yana kallon fuskarta dake bawa duniyarsa nutsuwa.
#mamuhgee.

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button