Uncategorized

AMANA TA CE Page 11 to 20

 Baba sani da kawu isiya burinsu yanzu shine tayaya dukiyar dad zai dawo hannun su don kulum samun cigaba ya keyi, kuma ba abunda suka tsana irin yawan sadaka da kyautata wa mutane, acewar su baisan zafin dukiyar sa ba, sun sha zuwa su samesa gameda ya daina yawan rabar da dukiyan sa, yaki, ya ce in dai akan wan nan ne kar su sake tun karansa, tun daga lokacin suka fara kule2 na makircin kawar da Dad.

        Basu tashi razana ba sai ran da dad yace musu zan fara aiki, a gurin kuma yanzu zai bani manager a company nin, ko kuma duk wani shiga da fuce kudi yazama ta hannu nane, ko wani kayan da za’a saya duk zai dawo hannu na,

ran da dad ya sanar min bakaramin murna nayi ba har kuka nayi, asai akwai irin su dad a duniya, asai bazan yi maraicin iyayeba, dad yayi ta lalla shina,.

             Han kalin su baba sani ya tashi matuka, nan suka fara shawar su jefa dad acikin ruwa nan baba isiya yace tayaya zamu jefasa, haka sukayita shawar wari, har baba sani yace mufara masa baraza ya daura mu a kan dukiyar sa, ko ya bamu in yaki sai muje gd mukashe shi da iyalansa da dan koran da ya daura akan dukiyar, nan sukace gakan za’ayi, tun daga wan nan rana suka soma kiran dad suna masa bara zana, akan dad ya basu dukiyar sa yaki, don har nima a sha yimin barazana akan na bar gdn dad amma naki don da Allah na dogara nan da dad zai rasu ya kiramu ya bani AMANA zee san nan yasanar mana ana masa baraza, amma yaki fadan ko suwaye, bayan da ya fita ne na kirashi a waya na tambayesa da farko ya ki fada min sai da na sanar masa cewa nima ana min baraza na, na basa lbr kafin ya ban lbr komai yace da kar in sanar da xee hankalinta zai ta shi, da daddare suka zo don kashe mu gaba daya cikin ikon Allah ya kubutar da ni da Auta kuma a lokacin taga wayan da suka kashe mata iyaye, dali2 da yasa yanzu na sanar mata kenan wannan shine lbr mu, Malam da inna laure suka dago fiskansu cike da kwalla ga tausayi auta ma kukan take ni kuma hawaye ne, wani na bin wani.

     Malam yace Allah ya jikan iyayenku, san nan a duniyar nan har ana samun marasa imani irin wayan nan mutane sun ci AMANA ga bata ZUMUNCI da sukayi ba ko tausayi a ransu sai son duniya, kuyi hakuri da rashi, da sannu Allah zai toni asirin su ya kuma saka muku, Allah ya jikan su muka amsa da Ameen.

Yan uwa amin afuwa na rashin jina kwana 2 waya tace ba charged, kuma ban samu zama ba.

Luv u all my fanz

®WISDOM HAUSA WRITERS

  

Rash Kardam

[6:40PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE

                        By

©Rasheedah .A. Kardam

   

               ®WWA®

                            

Bayan sunyi sallah isha’i suka dan yi hira kasancewar lokacin damina hadiri ya hadu aka soma iska, dole yasa suka shiga dakunan su don bacci, ruwa akayi sosai washe gari da safe bayan sun karya ne, Malam yayi shirin zuwa gona nan Ammar yace zai bi shi suka tafi tare, inna da Auta sukayi aikin gd.

Haka rayuwan su ya kasance acikin kauyen cikin kwanciyan hankali, yau kwanan su 10 kafar Auta har ya warke, Ammar ma ciwonsa ya bushe har yayi bawu, nan yasoma tunanin mafita don zamansu kauyen kaduna sam baiyiba, don marasa imanin nan suna sanin yana cikin kauyen to zasu iya turowa a kashesu baki daya, malam ya samu ya masa baya ni yana so su kara gaba don in mutu nen nan suka samu lbr zasu iya turo wa a kashesu malam yace hakane jiki ba kwari ya dau ko yan kudinsa da ya tara na kayan gonan da ya sayar ya basu yace suyi guziri inna kam da taji zasu tafi har da yar kukanta don sun shaku auta ma tayi hawaye, washe gari alhamis suka fito da ga kauyen nan suka shiga motar zuwa rigiyar malam wani kauye da ke jahar bauchi, a cikin motar suka zauna shiru ba mai magana sai yan motan da suke hira duniya.

         Haka har suka iso wani kauye wai shi na bardo, nan yaga ana sauka kawai sai yace bari su sauka gurin nan suka sauka, koda suka sauka gefen rumfunan garin dake bakin hanya ne ya sayo musu fura da nono roba biyu ya ba ma zee ta amsa, tafara sha kenan sai ga hawaye, ammar na ganin haka yace Auta hakuri zakiyi shi rayuwa haka take yau dadi gobe ba dadi mukasance cikin gode ma Allah, sai ya kara wada yar mu cikinta yayi sanyi amma takasa shan nono, wai ita ce yau a titi a kuma kasuwa take cin abu, rayuw kenan Allah ya jikan su dad, ganin taki sha yasa Ammar yakasa sha shima, don baya kaunar ganin zee cikin tashin han kali, nan2 sai yashiga damuwa. 

haka suka bar gurin suka dawo gindin wata bishiya suka zauna, lokacin sallah yayi ya nufi masallaci, yayi sallah dake a gefensu yake bayan ya idar ya dawo auta tayi alwala ta shinfuda dan kwalin zanin da inna ta fata ta daura, tayi sallah, haka har dare yayi koda aka watse gashi basu san kowa ba, Ammar ya duba musu gurin wani mai shayi da benci a gun nan ya hada ma auta kwaya biyu yace ta kwanta, haka ta kwanta idonta na zubar da hawaye, tabbas tasan ammar ne kadai ya rike iyayenta da gsky, Allah ya saka masa da dawai niyar da yakeyi da ita, Allah ya jikan iyayenta da nasa Ameen, Ya Allah ka bani abunda zan saka ma Ammar da shi, kuka ne yazo mata marar sauti haka tayi mai isarta daga baya tayi shiru, ammar ko kasance wan benci biyu ne a gun mai shayi ba wanda zai kwanta yasa ya dan zauna ya jingina da jikin falangen gurin shayi haka har bacci ya daukesu.

           Cikin dare misalin karfe daya da rabi, cikin bacci Ammar ya rika jin ihu daga nesa tun abun na nesa har ya matso kusa sai auta ma taji ta tashi, ihun yayi yawa gashi gudu sukeyi sai a lokacin yaji ana cewa barawo barawo, yace ma auta ta tsaya kar ta fito jikinta sai bari yakeyi nan ya fita itakuma tana lekawa, aiko yana fitowa sai ga wani tutum da gudu yabi bayan gurin shayi ya gudu, ana haka sai ga mutanen sun yi kansa suka nan suka fara dukansa suna shine barawon, auta na ganin haka tafito da gudu ta na ihu, wayyo Ammar dina ba barawo bane, wayyo dad kuzo ku kuga halin da muke ciki zasu kashe shi kansu tayi gadan2 tana so ta kutsa, da kyar ta samu tashiga dai2 wani ya kai masa duka da dorina kenan ya sauka akan Auta nan tasaki wani razanen kara.

 ®WISDOM HAUSA WRITERS

   

Rash Kardam

[6:40PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE

                        By

©Rasheedah .A. Kardam

   

               ®WWA®

                           

Wani kara tasaki, sai a lokacin suka kula da ita, take suka haskata da toci sai sukaga macece, wani daga cikinsu yace mai ya kawo wan nan guri, sai da yace tsaya in ga barawo nan tukun don wancan gajeren wando ne ajikinsa, yana haskawa ko ah… ah.. wan nan ba barawon bane to ina yayi, sai dayan yace wan can na da kirar gutun mutum, auta ko sai ihu take, ammar ko motsi ba yayi sanadin dukan da aka masa harda bora, wasu ice haka akayita kwana masa.

         A kaduna kuwa sadiya Al’amari abban ta ya daure mata kai don yasaka dukiyar auta gaba sai ci sukeyi, a ko a jikinsu, wata ran kam ma intasoma masa zancen auta ya hauta da fada kenan, haka yasa ta soma zargin wani abu a tare da su, 

         Wani yammacin asabar sun fito gidansu futha suna tattaunawa akan batun auta da yanda zasu bi al’amarin kenan sai suka hango abban sady, tun daga nesa yasoma wurga mata wani kallon tuhuma, ganin haka yasa tayi sallama ma futha tashiga gd, aiko kamar jira yake yazo ya fara zazzaga mata bala’i akan tafita harkan futha ko ya saba mata, shi baya son kawancen su, ganin su tare ma baya so, sady tace kayi hakuri abba ina tarayya da ita ba dan komai ba sai tun auta ta nan muna tare mun kuma shaku, abban sady yace hungo nan uwaki da autan nace uwaki da auta kar ki kara kira min sunan wayan nan banza mutanen, 

Previous page 1 2 3 4 5 6Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button