AMANA TA CE Page 11 to 20

nan take idon sady ya kawo hawaye ita kam bazata manta auta ba aminiyarta jininta, anya baba na da imani kuwa ko tausayinsu babu a zuciyarshi ko ya manta dukiyar iyayenta yake wada kansa shi, ya Allah kasanya mana tausayi da imani a zukatan mu Ameen ranan tayi kuka haka ta yini sukuku, sai yamma tayi shirin issalamiyya ta tafi ko da taje nan ta saida wa malaman su akan sutayata adu’ah ta kuma musu bayani ko mai ake ciki, tun daga ranan ya zamana kulum a makaranta bayan an gama karatu sai anyi ma auta da iyayenta adu’ah.
Futha kuwa kwana 2 taji sady shiru nan tashirya ta shiga gdnsu aiko nan sukayi karo da abban sady, tun daga nesa yasoma hararanta, tana isowa kusa yace kee wajen wa kika zo cikin ladabi tace baba kawar Auta ce nazo gun sadiya ne, yace maza ki juya kar na kara ganin lafarki a gdn nan yata batayi kawance da ke ba don ban yarda da kee ba.
ran futha in yayi dubu ya baci haka ta juya gd jiki ba kwari kuma tana tunani akan al’amarin nan,
anya ba hannu baban sady a kisan su abban auta, to tabbas ko ma miye sai na binciko ko da hakan yana nufin rasa raina ne ya Allah ka bayya na gsky.
Muta ne da ke gun duk suka soma watsewa ganin baya motsi gashi sun dakesa ba akan wani laifi ba, gudun shiga Case, auta ko in banda kuka da ihu ba abinda take sai kiran sunan Allah ga idonta har ya kubura yayi ja ga ammar shi da matatce marabansu kadan ne, wayyo Allah na ka taimaka min ka min agaji in ammar ya tafi bani da wanda zan kalla inji dadi, rayuwata zata zama abar tausayi Allah kaine gata na ka tai make ni ammar dina ya tashi, cikin kuka take jijiga Ammar ga hawaye ga majina duk sauka sukeyi, Ammar dan Allah ka tashi kar ka barni ka manta Dad ya baka “AMANA TA” ka tashi ka kula da “YAR AMANA” ka kuka take sosai mai ban tausayi tana ta surutai amma shiri ganin haka yasa takara fasa wani kuka mai ban tausayi wanda ni kaina Rasheedah ban san lokacin da na fara zubar da hawaye ba, gsky Auta da Ammar kun ga jarabawar rayuwa ga wlh Allah sarki auta abun tausayi, Allah yasa ammar dinki ya tashi Ameen.
Jumma’at Mubarak 2 all my muslim sisters n brothers.
®WISDOM HAUSA WRITERS
Rash Kardam
[7:32PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Kuka take sosai ammar ko motsi baiyi ba nan takara jin natsara su baba sani suka jefasu cikin irin wan nan halin, wani bawan Allah ne mai tausayi ya dawo yace bai war Allah daga ina kuke, cikin kuka tace ka taimaka min dan uwana ya tashi shikadai ya rage min an kashe iyayenmu, nan kukanta ya tsananta cikin tausaya wa yace ki tsaya tai mako daya zan miki yanzu ga gidan mai gari can barin je na kirashi da gudu ya tafi ko da yaje ya jima yana buga kofar kafin aka bude, masa, mai gari ya fito suka gaisa nan yasa sai damasa cikin damuwa mai gari ya dauko garensa ko da suka zo har lokacin ammar bai farfado ba, hakan yasa suka daukesa zuwa asibitin garin nan aka bashi agajin gaggawa, bayan sun dan masa treatment ne suka shin fidesa akan yar gadon asibiti, auta ko in banda kuka ba abunda take, bayan ansa masa ruwa mai gari ya musu sallama akan da safe zaizo duba su, auta kasa bacci tayi ga haddiri ya hadu nan akara walkiya da sauri ta haye karamin gadon duk tsoro ya ci kata baran data ga wajen asibitin jeji ne, nan ta kan kame ammar sosai hawayen ta na sauka a akan kirjinshi cikin barci yaji an kan kamesa, a han kali yasoma bude ido yaga duhu da kyar ya iya daga hannunsa yaji auta ne nan kuma yayi kokarin mikewa kansa ne ya masa wani nauyi ga sara masa da yakeyi, a hankali ya shafa kan yaji bandeji ne an daure, sai a lokacin ya tuna mai ya faru hawaye ne yasoma zuba masa shima tabbas yasan suna cikin wani yanayin da Allah ne kadai zai fiddasu.
Auta jin alaman na motsa hannu yasa da sauri ta shafi fiskansa nan taji hawaye a hankali ta daga hannun ta tasoma share masa hawaye tana cewa kayi hakuri Allah zai saka mana kaji kuma Allah yana tare damu yaga halin da muke ciki ba zai bar mu haka ba, nan ya karajin jikinsa ya mutu ga auta da ta kwanta masa ajiki bai san lokacin da ya sauke ajiyar zuciya ba, har azuciyansa yana son auta ko da aure zatayi ba iya bayar ta ga wani ba don bai son wani yaci Amanar da dad ya basa ko in auta tace bata sonsa to dole ya hakura don ba zai takura ta ba, gwanda ya shiga ko wani irin hali ne da ya sata a damuwa.
a hankali ya kara kan kameta a jikinsa wanda sai da itama taji wani shock ya ziyarci jikinta ajiyar zuciya tayi ahaka suka kwana yau kam bacci mai dadi tayi ajikin Ammar wanda rabonta da ta yi tun iyayenta suna da rai, sai da asuba ta mike da ta fiti kofar asibitin in da taga randar ruwa ta diba tayi alwala ta shin fida dan kwalinta tayi sallah,
bayan ta idar ne ta zo da ruwan ammar da kyar ya iya tashi sabida jikinsa yayi tsami tana zuba masa ruwan yayi alwala yana kwance yayi sallah don kansa ya masa nauyi.
Sai da gari ya waye sosai gurin karfe 9:00 mai gari yazo duba sa da yar kununsa a kwanon sha da kosai nan suka gaisa bayan sun gaisa ya ke tambayan su mai ya kawo su gari da har zasu kwana a kasuwa nan auta ta basa lbr ya tausaya musu sosai, nan ya musu sallama akan darana zai zo dubasu auta haka take kula da ammar dan kudin da malam ya basu shi suke yasan abun da ya dan musu su ci, kwanan Ammar uku a asibiti aka sallamesa jikinsa ya warke sai tabo, ko da suka fito a asibiti gdan mai gari ya nufa ya masa godiya san nan yace yana so su kara gaba don yana son cikin birni inda zai samu sana’a yayi da karfinsa, nan mai gari ya ce yanzi kana fita sai garin bauchi shine babban gari, nan yaji yana son garin don ya dade yana jin lbr garin bauchin yakubu ga Addini ka mutunta mutum ga iya karama baki, ga masa waina sai wanda kazaba, nan yayi godiya mai gari ya rakasu suka shiga motar bauchi.
Rash Kardam
[7:32PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE
By
©Rasheedah .A. Kardam
®WWA®
Mota su ka shiga, a hankali suke tafiya, haka kurum ya tsinci kansa da farin ciki, tun a hanya yaji yana son garin ya burge shi.
Auta ma haka abun yake tana gefen Ammar ta dan jingina kanta a kafadarsa, haka kurum take jin sanyi a zuciyar ta, nan ta fara tuna irin rayuwan da sukayi abaya lokacin iyayenta suna raye, ku ina zataje a mota suke tafiya mota mai AC ba hayaniya, amma yau gata a motar kasuwa, Allah sarki yarinyan da taso cikin gata da kulawa ya daya tilo yau gata a cikin gararin rayuwa Allah ya kawo masu sauki Ameen.
Karfe goma da minti sha uku, suka iso cikin garin bauchi, driver ya sauke su a waje tashar mota na winti market, nan suka sauka, kowa ya kama gabansa, Ammar ya riko hannun Auta suka bar gurin, titi suka tsallaka suka zo ta gefen stadium akwai dan guri nan suka zauna, kallo daya zakayi ka ga kamanin su auta yanda ya canza sunyi baki ga rama da sukayi sosai.
Sun dade a gurin sosai, amma sun rasa inda zasuyi can yace bari yaje ya nimo musu abinci, tace to gefen gun masu sai da jarida da gyaran mashin ya ga mai sai da shinkafa da wake nan ya saya musu roba biyu da pure water kwaya 2 ya kawo musu, haka suka ci sukayi godiya ga Allah ya mayar wa masu shinkafa ya karbi canji ya dawo, haka suka zauna sai da aka kira sallah, nan ya sake saya mata ruwa tayi alwala shi kuma ya tafi masallacin da ke gefe yayi sallah, bayan ya dawo suka zauna hira ya rinka mata yana bata dariya don ya debe mata kewa sabida yaga damuwa a idonta sosai, haka suka yini har dare agun suka kwanta.