Uncategorized

AMANA TA CE Page 11 to 20

       Baba sani ganin Sady da futha suna neman dinkrwa yasa ya baza mata kan tsaro duk inda sady tayi ana biye da ita don kar futha ta gano sirrinsu don bai yarda da ita da mahaifinta ba suna masa shigan sauri akan al’amarin, su baba isiya yanzu abun nema ya samu hankalinsa kwance ke cin kudin da bana saba har in anzo neman taimako gunsa yana ikirarin sunsan wahalar dayayi yasamu dukiyar su asama kawai suka gansa da kudi, kutaya ni ji wai har yana cewa sun san wahalar dayayi, baba isiya har wani yar tumbi yasaka yayi fresh ko mai ya dai2 har ya manta da wani alhaji Al-hassan.

             A bauchi kuwa Ammar da murnar sa ya nufo gun Zee Auta ya musu samuwa don shi ko ta kansa bayayi yafiso yaga ita taci kafin sai yaci, yazo tsallaka titi har ya kusa tsallakawa sai ga wani mai mashi ya yanko aguje ji kake kiiiii mai mashin ya shiga da Ammar da sam idonsa ya rufe baya ganin hanya.

Yan gurin nan suka dau salati suna tafa hannu wasu suka yanko da gudu suka zo ba da taimakon gaggawa Allah sarki kowa da irin jarabawar da Allah ke masa a rayuwa kamar yanda Ammar da Zee suka shiga haka wasu ke cikinta kowa da kalar nasa ya Allah ka jarrabe mu dai2 da karfin imanin.mu Ya Allah kabamu Abin da zamu iya Ameen Ya Allah.

®WISDOM HAUSA WRITERS

 

     

Rash Kardam

[7:35PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE

                        By

©Rasheedah .A. Kardam

   

               ®WWA®

                           

Kiiiii kake ji karar mashin ta tashi sama da ammar nan mutanen gurin duka dau salati, wasu da gudu sukayi gurin, abinci kam duk ya zube, nan mutane sukayi kansa cikin ikon Allah bai ji ciwo ba sai dai ya dan buge kafarsa gefen hanya aka maidashi mutane sai sannu suke masa Ammar na dawo hayya cinsa sai ya hango robar abinci ta fashe maganin kam bai san ida ya yarshi ba, nan take wasu zafafan hawaye suka soma gangaro masa a zuciyarsa yana gode ma Allah daya sa yana da sauran rai in da Allah yaso sai kafarsa ta cire ko hannu yana da kyau a kowani hali ka tsinci kanka to ka gode ma Allah sai ya kara maka, cikin ikon Allah mai mashin ne ma ya dan kurkurje nan ya ba ma ammar hakuri don yanzu fitowarsa bai da ko sisi ajikinsa Ammar yace ba komai haka ya mike ya na din gisawa ya sake zuwa chemist ya sayo paracetamol da da maganin mura na ishirin ya sayo ma auta shinkafa talatin ba ko ruwa nan ya laluba aljuhunsa ya ga biyar hamdala yayi ya sai mata pure water biyar da sauri yana din gishi ya nufi gunta.

yasamu duk ta dawo wani iri dagata yayi yana mata sannu abinci ya fara bata da kyar ta iya ci kafin tasha magani ya maida ta ya kwantar nan yaje yayi alwala yayi sallah bayan ya idar yayi nafila yana gaya ma Allah kukansa kafin ya dawo gurin auta ga yunwa tasoma damunsa sai da yaga bacci ya dan dauketa kafin ya sake komawa cikin kasuwa ya yi sharan yayi sa’ah mai shagon mutumin kirki ne ya basa dari buyu nan ya bashi sauran abinci ammar yayi godia yaci kafin ya sake suwa wani gu ya musu aiki nan ya.samo dari uku nufo hanya.

        Tun daga nesa ya hango auta rike da cikinta tana juyi da sauri ya karasa gunta,nan yasoma mata sannu yariketa kuka tasoma masa duk ya rude ya tambayeta mai ke da munta tace cikinta ganin yanda take juyi yasa ya dauketa da sauri ya nufi titi nan rake aka zuna musu ido dake haka ya nufi chemist da ita nan mai chemist ya soma dubata aiko yace Malam period dinta ne zaizo nan ammar ya zare ido yaya zaiyi ba pant ba gun wanka mai chemist ya bata magani tun agun tasha ya dan kwantar ta akan benci sun dan dade don ciwon ya dan ragu sai rashin karfi ajiki nan ya cemasa kudin magani 200 haka ta bashi nan suka mike zasu tafi kenan yaga shini ya bata gun da ta zauna nan ta zare ido yau yaga ta kansa ya zaiyi kenan Yasalam Auta ko tsaban kunya kasa daga idonta tayi sai hawaye nan ta fara Allah ya isa masu baba sani duk sune ummul aba isin sata cikin wan nan hali.

®WISDOM HAUSA WRITERS

Rash Kardam

[7:38PM, 9/20/2016] Rash Kardam: AMANA TA CE

                        By

©Rasheedah .A. Kardam

   

               ®WWA®

                           

Ammar gaba daya ya rasa mai ma zaiyi ne sun dan dade agun mai chemist daya ga basu tafi ba ya lura da matsala dake ustaz ne yasha Sunnah ya koshi cikin kulawa yace malam lfy dai ko ammar ya dago idonsa da ya cika da kwalla ya ma rasa mai zai ce, mai chemist yace ya kamata ka kaita gd don tayi wanka ta huta ammar cikin muryan sa na rawa kamar zaiyi kuka yace mu baki ne a garin nan bamu da kowa cikin tausayawa yace ayya sai a lokacin ya lura da yanda jikin auta ya baci nan ya ce masu ammar zan muku taimako daya ga gd na banisa kazo muje gun matana ta taimaka mata da kaya ta gyara jikinta ammar yaji dadi yacd ba matsala nan ya riko hannun auta suka bi mutu min nan gd sa na bayan stadium plat ne ciki da falo sai stored sai kitchen nan ammar ya tsaya daga waje shikuma sukayi sallama suka shiga da auta nan wata mata baka mai dan kyan jiki gata da sakin fuska ta fito tana musu sannu dazuwa cikin harshen fullanci ya mata bayani nan naga fuskan Rahmat ya bayya na tausayi tace yar uwa shigo dake bayinta na falon ne nan ta hada mata ruwan wanka ta kaita bayin shiko mai chemist ya kowa waje gun ammar suka dan fara hira.

Rahmat ta ciro mata sabin pant guda 4 da Alway ko amfani da shi batayi ba ta dauko mata riga da siket daya da dogon riga dake da ka dan zata fi auta ki ba nan ta samata a wata yar jakan biki mai zip da hijab daya da sabulun wanka sinki da na wanki biyu nan ta saka mata riga da siket na eglish wears wanda tasa da hijab mai hannu blue yadin plan tuyobo bayan auta ta gama wanka nan ta bata pant tasa ta bata mai da powder tasha da lip stick kai kar kuso kuga auta nan ta yi kyau abunka da farar mace ga kyau azuciyar rahmat tana yaba kyau irin na auta abinci tabata nan taci sosai ta bata zobo yasha hadi kafin ta dauko jakan ta bata lokacin har ta dauraye mata kayanta sunsha ta nuke tasa mata a hakar tace ki duba waje kice musu kin gama nan auta ta leka tun da tafito ammar ke kallonta sai murmushi yakeyi ga idonsa ya ciko da kwalla rabonsa da yaga auta fess haka tun suna gun su inna laure a kauye yau har yar kyau tayi, auta tazo da sauri tasa hannusa ta share masa kwalla tace yaya na kabar kuka nima zaka sani kuka murmushi yayi yace babyn dad yau kinyi kyau sosai tace ta gode duk abunda sukeyi mai chemist na ganinsu duk sun bashi tausayi nan ta sai dama su sakon rahmat mai chemist yashiga gd ya fito masu abinci sai da su kaci kafin Ammar ya masa godiya auta tafito suka kara gaba. Rayuwa kenan 

              * * * * * *

Sady abun duniya duk ya isheta yanzu bata isa tafita ba babanta zai dameta gashi yace matukar ta hadu da putha sai ya yanka ta kuma motar da zai bata ma ya fasa duk ita bai da meta ba sai sauyawan babanta anya yana da gsky yake haka yazama dole insan sirrin boye tana cikin wan nan tunanin pinky tazo cikin masu matsatsun kaya da kyar ta ke motsi cab su pinky an samu duniya yanda akeso rawan kai ya karu bare ga mota a hanu….lol… Hira sosai sukeyi anan sady take lbr ta ma pinky sauyin iyayensu pinky kafada tada ga alamar ko in kula cikin isa tace ni ba damuwata bane tunda zanci mai kyau insha mai kyau bani da matsala ga motar da zan shiga ko ina ba sa’ar dazata min raini kin ga ni ba damuwata bace kawai ke ma ki share kizo ayi harka dake sis sady tace ni kyale kyale baya gabana gasky nakeso tafito kuma zanyi iya kokarina pinky tace ae saikiyi ta kai nan tafice tashiga motar ta tabar gdn.

Previous page 1 2 3 4 5 6Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button