AUREN GADO Page 11 to 20

Ya sumar da ita da kalaman shi, saida ya fita ta zube akasa tana hade jikinta, she can feel his presence up to now, a dakin jikinta kamshin shi duk ya Kama, kalmar shi na ko pant da breziya sai yana ra’ayi zata sa ya tsaya mata arai, lallai tantiri take gani a gaban idanun ta na bugawa a jarida, zata iya rantsuwa kalmar bazata taba futowa daga bakin shi ba, yanda yake behaving like gentle man, now she is mistaken, infact batasan me zai yi nan gaba ba, kallon tsintsiyar hannun ta tayi tanajin nashi haryanzu a nata, Wani irin Yar takeji fiyeda yanda takeji idan Ahmed ya riketa, hannun shi kamar Wanda yake massaging dinshi da baby oil, saboda softness ko ita mace hannun ta baikai nashi laushi ba, she can still feels his heart beat, lokacinda ta fada na second biyar, zuciyar shi bugawa take da mugun karfi. Tashi tayi tareda kwabe kayan jikinta ta zubar akasa, ta datse kofar ta koma zubewa akasa, kallon shape dinta nayi, ta tsaru dakyau jikinta nada tsari da Wani irin kyalli abunka da fara, juyowa tayi ta zubawa tukunyar fulanin ta ido nasan cewa yes Ahmed yayi rashi babba da bai more way’ennan Abubuwan ba, a cike suke tam a girke zaune Alamar bazasu taba kwanciya ba, tashi tayi ta kalle su tasa kuka ” am sorry Ahmed dana sani nabari kayi yanda zakayi dasu da nasan bazaka rayu da ni ba, bazan kasa kai maka hakkin kaba, yanzu tayaya zan iya bawa dan uwan ka kulawa, bazan iya ba kaine ka dace da duk wannan Abun ba kanin kaba, murje idanunta tayi tareda daura kuduri mai girma. Kiran da taji Inna nayi mata yasa ta zabura ta mike, wasu kayan tasa domin ta tsani way’ennan saboda kamshin shi da sukeyi, ta fita idanun ta sunyi ja. “Toh” Malam yace Anjima zaki tare gashi wannan Karon ko shiri ba’ayiba don haka na Kira yayar ku tace tana zuwa kije ki hada Abun bukatar ki. “Toh” tace kamar zatayi ihu saboda damuwa, gwara zama da mommy sau dubu da zama da khaleel a wurinta, a tunanin ta tagama zama a wannan gidan sai gashi rayuwa takuma juyawa da ita ta bahagon hannu.
Tunda yafita gidan su yana barin unguwar yayi tafiya mai nisa yayi parking a gefen titi wajen da ba hayaniyar komai ya Dora kanshi a jikin sitiyarin motar shi, wani irin numfashi yake fitarwa da sauri da sauri, yanajin kamshin turaren wutar da take Amfani dashi akaya, he can feel her chest a nashi har yanzu, runtse idanun shi yayi da karfi yana dukan iska, fauziya tasha rungume shi by mistake bai taba jin haka ba, wani irin racing zuciyar shi keyi, itace mace ta farko da ta fara sashi yaji shi a namiji, bayaso ya nuna mata rayuwar Aure sai yakoya mata sonshi, sai ya cire mata bakin cikin zamanta na baya sai ya bata dukkan farin ciki, so yake yazama bawan mace a Karon farko, Amma sai yayi amfani da nashi salon, “Am sorry Yaya, zuciya batada k’ashi, batada limit, I don’t know when and how? I think tun ganin ta nafarko yes that’s it, love at first sight.
“But kai take so, bana bakinciki because she love you, zan tayaka bata farin ciki I promise you bazan taba cutar da itaba that’s my promise to you my brother.
Hour guda cur ya kwashe yana tunani a wurin kafin ya wuce ya samu kawun shi yafada mai yau zata tare, yasa Albarka tareda Bashi shawara akan zaman Aure, da kuma akan mahaifiyar shi, sai kayi da gaske, ina fatan kasan halin Hajiya balkisu fiyeda ni yanzu, don haka Allah yabaka ikon sauke duk wani hakki.
Godiya yayi yatafi tareda wucewa gidan,
Bakowa duk sunfita, mommy taje wurin zarah domin neman mafita ita kuma Fauziya tayi gidan su,
Tabe bakinshi yayi ya shige dakinshi ya kwanta yana murmushi, yana hango yanda maganar shi ta sa takoma kamar gunki, “this is just the beginning baby. Tafin hannun shi ya kalla, yana jin kamar har yanzu yana rike da tsintsiyar hannun ta, yasan dole taji yanda yakeji shima, ya dauki lokaci yana tunani kafin yayi bacci mai dadin gaske,
Gefen Naziya kuwa tana zaune batada zabi Shukrah ta zana mata lalle jada baki gefe Aunty Raliya ta shirya mata lafiyayyar kaza tasata ci, zama tayi ta nagi kayarta tasan aikin banza sukeyi kawai yanda Ahmed yatafi haka shima zai gaji ya sallamo ta, ba Abinda zai shiga tsakanin su, sayi sa gama. Haka ta murjeta da dilka tas, zuwa magrib ta yi wanka da ruwan kamshi da yaji hade hade, suka bata sabon kaya ta saka, tayi sallah,
Ta dade a sujudarta tana neman Allah ya taimaketa kar ya bawa duk wani makiyinta sa’a akanta, bayan isha’i Malam ya shigo gidan ya zaunar da ita tareda yimata nasiha mai ratsa jiki.
“Naziya nasan zakiji a zuciyar ki banyi miki adalci ba, nasan bakya son wannan Auren, kuma nayi matukar mamaki da kike kokarin bujurewa hukunci na, shin kin manta bana yin Abu dakai, kin manta duk Abinda nake nema sai na nemi zabin Allah, na hango miki farin ciki Naziya idan har kin daure kin karbi kaddarar rayuwar ki, kije Kiyi biyayya Albarkar mu tare da Addu’ar mu tana tare dake, Allah yayi miki Albarka. Kuka takeyi kasa kasa hawaye sharkab a idanun ta, Inna ma tayi nata tareda sa ma rayuwar ta Albarka.
Sallamar shi ce tasa Malam ya fito tareda tarar shi cikin murna “sannu Ibrahim ka iso. “Eh Malam. “Toh Hauwa fito da ita ga mijinta, “wani irin nishadi yake jinshi a ciki, tun bayan mutuwar dan uwan shi yau ne yake jin kamar Ana wanke mai zuciya da ruwan madara.
Cikin manyan kaya yake sky blue yard na maza yanada wani kyalli kyalli kana iya hango farar singlet dinshi, gayen yasan sirrin ado, kuma duk shigar da yayi kyau take mai saboda cikar zatin shi, ko dago kai batayi ba data fito cikin katon hijabi kalar kayan jikinshi, Wanda yana kallon ta yayi murmushi cikin duhun daren, wannan fitinannen kamshin nashi duk ya cika musu tsakar gida,
Inna gaisawa sukayi tace bari insa Shukrah ta kwaso kayanta. “Abar kayan zandawo inkwashe su gobe. Yafada tareda yi musu sallama ya fita, komawa tayi ta rungume Inna tasa kuka, jikinsu duk yayi sanyi, Malam fita yayi yana cewa idan kungama Shukrah ta rakota waje,…….. ????
*Wacce wainar zamu soya a gidan khaleel my fans, wane irin rayuwa ce zatayi tareda wainnan mutane ukun fauziya momy and khaleel, meye ra’ayinku akan kudurin Naziya? Waye zaiyi nasara a wnn tafiya khaleel or Naziya? ” muje zuwa time will tell insha Allah*
*Matar Soja*
[ad_2]