AUREN GADO 1-END

AUREN GADO Page 11 to 20

“Aunty Ahmed yatafi” Zarah tafada tana dora hannun ta saman kai, kawu wani irin zuface ta karyo mai tuni ya ciro hular kanshi yana fifita, “ya Allah” Kawai ya iya fada saboda sarkewar kalmomin bakin shi, saida zarah ta jijjiga mommy, kafin ta fasa kuka”wayyo Allah na ni balkisu Ahmed tafiya Kayi kabarni, why Ahmed why? 

Rufeshi likita yasa Akayi da farin zanin gadon, yace Alhaji sai hakuri Ahmed lokaci yayi. Dakyar kawu ya iya saita natsuwar shi yana goge gumi kamar ya hadiyi kunama, ya ciro wayar shi a Aljihu ya yakira Khaleel, ” kana Ina? “Yanzu na shiga gida kawu zan dakko Matar yaya. “Stay there muna zuwa. “Why yaya yac…. “Just do as I said, yafada cikin fada kafin ya katse kiran. 

Shi ya hada komai yayi clearing aka basu Ambulance Abunka da kudi cikin minti kadan suka tafi da gawar su, 

Mommy kamar ta haukace ji take kamar a mafarki wai Ahmed dinta ne ya mutu. Aunty zarah ido yayi Hulu Hulu. 

Naziya tun fitar su take kan dadduma, zuciyar ta bugawa takeyi da karfi takasa ko motsawa, su kuwa Amare suna hakimce kowacce taci Ado kamar masu gasar gwal. Sun hakimce a falon,

A harabar kuwa Khaleel ya kasa gaba ya kasa baya saboda tashin hankali, ga umarnin kawu, yana daskare jikin motar yaji kukan Ambulance, wani irin kallo yake wa motocin su mommy, ganin yanda Aunty zarah ta riko mommy sannan kawu shima ya fito kai ba hula, ya maida idanun shi akan Ambulance yana kallon nurses din suna bude motar, ganin sunfito da mutum rufe da farin kyalle ya zube kasa war was, domin baya bukatar Karin bayani akai. Masu aikin ne suka ruga wajen shi domin jin faduwar tashi Tim. 

Mommy ta tafi luuu itama tana shirin zubewa, shima ya mutu ko zarah? In ya mutu shima ni tawa ai takare kenan. Tafara sambatu, zarah ta riketa tana jijigata a’a Aunty bai mutuba, kai ku shiga dashi ciki, kawu dai nata gawa yasa aka shige dashi ciki, hakama Khaleel anyi ciki dashi,  

Wanda tuni hankalin kowa ya kawo kan abinda yake faruwa banda Naziya, domin Amarya Salifa ita kanta jikin ta yayi mugun sanyi, wane irin Abu ne haka Auren ta jiya miji ya mutu yau, 

Kukan da mommy ta fasa yasa Naziya fitowa jiki na tsuma da carbi, ganin mutum kwance akasa ga kawun su zaune agaba ya dafe kai yasa tafito jikin ta a mace tana sand’a kamar barauniya. 

Kukan dasu Aunty zarah dasu Salifa keyi yasa ta gano duk Abinda yake faruwa. Dabas ta baje akasa kamar kurma, kafin kace me, tuni ji da ganin ta sun dauke. 

Koda ta farko, taga dakin ta makil da mutane harda su gwaggon nin ta dasu Aunty Raliya da kuma matan kawu. 

Zabura tayi tana kallon jikewar da jikin ta yayi da ruwan da aka rika kelaya mata,

Ganin ta zaburo Aunty Raliya ta riketa, “Naziya bi a hankali ruwa ne a hannun ki. Kallon hannun tayi, tareda kallon mutanen tace mafarki nakeyi ba mutuwa yayi ba ko? Aunty bai mutuba ko? Ku fadamin Ina yake? 

Dafata kanwar malam tayi tace “ki yawaita Inna lillahi Wa Inna Ilaihir Raji’una Naziya. Tafiya takuma yi luuu. Suka kwantar da ita, kowa na share kwalla, 

Khaleel kuwa saida akayi da gaske ya farfado, lokacin angama hada gawar Ahmed, zabura yayi kawai, ko digon hawaye yakasa fitowa a idanun shi. 

Kannen shi ne yaran kawu maza suka rikeshi “yaya Khaleel bi a hankali karka fadi. “Let me go. Yafada cikin fada. Kafin ya fisge ruwan yafice cikin Sauri lokacin za adauki gawar zuwa makwanci, harda malam yazo gidan yau. 

Cikin sauri yace “kawu kubari inyi mai Addu’a, fuskar shi ba ko Alamar hawaye domin ance kuka wuri yake samu watarana zuciyar shi ta cushe ta inda bako digon hawaye dake shirin zubowa. 

Kowa yasan na zuci yakeyi Wanda ke cin zuciya, don haka malam yace “Ibrahima, ka saki zuciya Kayi kuka bakyau hadiye Abu yana illata mutum cikin sauri. 

“Malam muje akai yayana makwancin shi. Yafada yanasa hannu ya daga makarar gefe daya domin yasan idan shine yayan shi zaiyi mai har wankan karshe, Amma tunda bai samu yimai ba shine zai sakashi cikin Kabari tareda samai kasa da binshi da Addu’oi. 

Yabawa kowa mamaki yanda ya sakawa kanshi jarumta, har zuwa makabarta, inda da hannayen shi yasakashi cikin Kabari, tareda yimai kallon karshe, Wanda anan zuciyar shi ta karye ya fara fitoda hawaye, shikenan yayan shi yatafi, gatan shi Wanda saboda shi yadawo Nija, da ana dawo da hannun ago go baya da ya canja tsarin rayuwar Dan uwan shi , da ya hanashi shiga bakin ciki, Amma me komai mukaddari ne baida Wannan damar komai, yanda Allah yatsara haka zai kasance. 

Lallabo shi akayi dakyar zuwa gida malam da sauran y’an uwan su, harma da mutane gari Wanda kowa mutuwar Ahmed din ta girgiza shi, Wanda sai ka mutu ake sanin halayen ka, wasu nacewa dazufa sun gaisa a masallaci, Wanda ita rayuwa haka take yanzu kana nan Anjima baka sai wani kuma, rai bakon duniya, Allah yasa mucika dakyau da imani………. ????

“Kai jama’a bantaba k’isa ba a littafina irin Wannan don haka nikaina na koka na girgiza Wanda nasan watarana saidai labarina nima zantafi, ya Allah Kayi mana kyakkywan karshe kasa mucika dakyau da imani don darajar ma aiki, S. A. W????

*Matar Soja*

????????AUREN GADO????????

                           

*Matar soja ce*

Daga marubuciyar 

KUSKURE NA,

BARIKI AUREN SOJA,

MUK’ADDARI,

WANAKE AURE,

ZANYI BIYAYYA, Y’AY’AN GATA, And now AUREN GADO, 

Ga masu bukatar Wnn littafi ku turo kudin ku ta Asusun banki na 7304736012 nafisa sani hassan Fcmb ko katin wayar ku ta Wannan number 09011251444, sai kuma y’an ???????? Niger ku tuntubi Wannan number domin biyan naku, +225 0748153903, littafina Dari biyar ne kacal 500 sai najiku nagode, 

*my fans masu maganar Ahmed yabar k’wanshi, ai mommy zataji dadi gwara tayi nadama ta har Abada tasan Allah yabata yaro mai yi mata biyayya har bayan idon ta, kuma shine zai zamar mata tabo har karshen Rayuwar ta don haka muje zuwa dama bahaushe yace in kana mugunta bakayi wa kanka ba to baka cika mugu ba*

Last ???? page

1⃣9⃣&2⃣0⃣

………….. Naziya kuwa Abin kamar a mafarki haka take ganin shi, koda ta farfado manya suka natsar da ita sunayi mata nasiha, sai Ajiyar zuciya takeyi takasa koda fitarda hawaye, Saida Akace mata har an sallace shi an dangana shi da makwancin shi ne ta fasa kuka, shikenan yanzu bazata kuma ganin shi ba, haka rayuwar su tazama tarihi Auren ta dashi yazama tarihi, Wannan wace irin kaddara ce ta bullo a cikin Rayuwar ta? Istigifari ta farayi domin kar Imanin ta yayi rauni, Amma kowa yasan bakaramin ciwone a zuciyar taba rashin mijin da kukayi Aure wata biyu yatafi yabarka, kowa ya tausaya mata, har kanin Baban su Ahmed din na gidan sunzo, mommy kuka take tana birgima, cikin masifa Aunty Fatima tace “Wallahi bilkisu kukan ki baida Amfani ai saiki tashi kiyi farin ciki, Ahmed yatafi yabar miki duniyar, ba Auren kece raini ba! yau gashi yabar miki matan duka, kiyi Addu’a ma ko jika ace yabar miki jikin Y’ar talakar da bakyaso, kin hana yara sakat ai munsan komai kallon ki mukeyi kawai kijira Abinda zai biyo baya, wallahi sakamako na zuwa. Matar kawu ce uwar gidan tace “Aa Fatima kubarta haka rashin d’a tayi kuma kuzo ana zama kuna tada fitina. “Nayi shiru Matar yaya”. 

Kuka Momy ta fasa, yanzu take data sani mara Amfani Ina ma Ina ma, Allah yasa Naziya tanada ciki, Allah yasa zata ga Abinda zai cire mata kewar d’an ta mai hakuri, Kuka takeyi mara Amfani domin batada damar maida hannun agogo baya.

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button