AUREN GADO 1-END

AUREN GADO Page 11 to 20

Dagowa yayi tareda cewa ” koyi nakeso inyi da Rayuwar da kika dora shi akai mommy, Ina ganin yadda yayi Rayuwa batareda Matar shiba, kuma kece kika sashi, ke kika hana yaya na ya sauke hakkin da ya dakko har yabar duniya, mommy kina tunanin Allah bazai tanbayi d’an uwana Wannan hakkin ba? Ta dalilin tsanar da kike yimata har tabar gidan nan bataji dadin rayuwa da mijinta ba why Mommy? Don haka itama Matar son taki tayi biyayya irin nata tagani. 

Ibrahim banson rashin kunyar ka haka kaga Ahmed…. “Mommy enough, kidaina kwatance da yaya, ribar me yaci, kinga Amfanin Abinda duk yakeyi? See to avoid you and your wife, am going back to bangkok, zanje in kulada duk wani aiki da yayana yakeyi, bana ra’ayin zama anan, I don’t need her idan tagaji tasan hanyar gidan Uban ta. 

“Ibrahim, zan hadaka da kawun ku inni bazakaji magana taba. Wucewa kawai yayi, dama so yake kawai ayi fourty days ya yi gaba Amma yanzu baijin zai iya Kara ko kwana daya a garin kano gwara yatafi ko zai dawo dai dai. 

Duk gurmin da Akeyi Fauziya ta shigo tana kallo, yana wucewa a zuciye ta nufo mommy cikin kallon tsana da kece sanadi, tace Wallahi bantaba sanin Abinda kikayi zai shafi farin cikina ba dana taka miki burki, kuma zanje in shirya inbi mijina. Ta buga mugun tsaki, “Fauziya karfa ki manta ni uwar mijin ki ce kike fadamin maganar da kikaga dama. uwar miji uwata ce ko uwar ubana ce? I beg give me a break. Ta yi gaba zuwa dakin shi dake part d’in . 

Yana hada kayan shi, tayi sallama yayi wurgi da Abinda ke hannun shi saboda haushin takurar ta, ya juyo cikeda haushi, “can’t you learn from Naziya, kintaba ganin tana bin yaya the way you are following me? Please have some shame. 

“Oh baby yazaka hanani bin mijina, you are my husband Inada right akan ka, and ka daina hadani da Wannan village and stupid girl……. Wani irin kukan kura yayi a wuyan ta, tareda shake ta ya hada da gini idanun shi kamar na bakin kumurci, “what did you said? Cikin karaji, don’t repeat that again if not kin gama numfashi a duniya, I promise you, kin ce hakki ko kinada hakkina? gani ki diba in kinada karfi, hakkin na karfi ne kizo ki kwata, useless, now get lost. Ya saketa tareda hankada ta waje, 

Da mugun kuka tafita falon Wanda mommy naji tayi Saurin tarar ta, Fauziya lafiya Me Khaleel din ya miki? karki tabani kuma wallahi sai na fadawa daddy na ke kikaja Wannan aikin da kike taka ma dashi sai kin barshi. Tafita tana kuka, hannu ta dora aka, kunga yaro zaimin salalar tsiya, Allah sarki Ahmed da kana nan kaine kadai mai iya takawa yaron nan birki, Allah ya jikan ka yaron kirki Allah yakai haske kabarin ka. 

Ta share kwalla tabi bayan shi, 

Lokacin yagama shirya jakar shi, kallon kayan tayi tareda zubamai ido, yanzu Khaleel bangama war warewa a rashin d’an uwanka ba zaka tafi kabarni bayan kasan banda kowa sai ku biyu kacal, yanzu shi yatafi kai kuma zaka tafi kabarni. 

Baice mata komai ba yayi hanyar bathroom, fita tayi tana fitar da hawaye, wayar ta ta dakko tafara kiran number wayar kawun nasu, yana dauka tasa mai kuka tareda fadamai komai akan zaman shi da Fauziya, da kuma tafiyar da zaiyi. Yace mata Yana zuwa kawai ya katse kiran. 

Bayan hour biyu kawun ya iso lokacin yaci Ado cikin manyan kaya Wanda rabon shi dasu tun kafin mutuwar yayan nashi, 

Lekowa mai aiki tayi tace Ana kiran shi a falon, ya ce tace yana zuwa, fitowa yayi, yasamu mommy gwanin tausayi gefen kawu akasa yau tunda tana neman taimakon shi. Sallama yayi yagaida shi, zama yayi a kasa kanshi akasa, fuskar shi ba annuri ko kadan, kawu yayi gyaran murya yace “Khaleel tafiya zakayi batareda sani na ba? “Aa kawu yanzu ma gidan naku nake shirin zuwa infada maka.Toh Amma me zakaje yi kabar nauyin da yake wuyan ka anan, nafarko Matar ka, na biyu mahaifiyar ka na uku company, sannan wasiyar d’an uwan ka, ko bazaka cika mai burin shi bane, domin yafadamin tun ranar da zai rasu saboda rashin natsuwa banyi maganar da kowa ba, sai Malam, dago kanshi yayi domin jin wane magana akayi harda malam zai shiga ciki, “Ya bar maka Amanar Auren Naziya, kuma munyi magana da malam tunda zance ne na wasiyya ya Amince sai dai muyi Addu’a ta fita takaba lafiya sai a daura muku Aure da ita. 

Wani irin zufa Kebin ta kowane kofa ta jikin shi, yakasa koda motsi baya iya koda daga yatsar hannun shi balle ta kafar shi, 

Kukan mommy ne yasa yadawo hayyacin shi , wallahi bazai yuwu ba, yaza ayi yaya ya Aura ya mutu kanin shi ya Aura, kuma dole ne ni sai nayi Rayuwa da Wannan yarinya mai kamar mayya, nidai ban Amince ba gaskiya bada yawuna ba. 

Kallon banza kawun yayi mata kafin yace ” ni nasan bazaki canja ba balkisu, kuma nasan ilimi yayi miki karanci da kin koma islamiyya, tunda bakisan Ibrahim zai iya Auren Naziya ba, kuma Ina so insani me yarinyar tayi miki, ko ince meye laifin ta? Ni tanada laifi A wurina kana ganin saboda soyayyar ta dana ya hadiyi zuciya ya mutu, banason ta kuma lashemin zuciyar Khaleel din da ya ragemin nidai bada yawuna ba. 

“Yawun ki basuda Amfani a wurin mu don haka Khaleel gareka idan ka Amince kafin ka wuce kaje kaga malam Allah ya taimaka ya kuma tsareka, sannan zancen Matar ka Wannan kaidai ba jahili bane kasan hakkin Aure to don haka Kayi kokari Kayi Abinda ya dace ni natafi. 

Yafada yana mikewa, tashi yayi jikin shi a sanyaye yabi kawun Saida ya shiga motar shi yadawo gidan, tana nan ta cika tayi tab. Kana jina Ibrahim, wallahi kar kasake inji kadawo min da Wannan yarinya mai farar kafa gida, karka sake ka Amince da Wannan Auren nafada maka. 

Wucewa kawai yayi cikin dakin shi, ya datse key tareda zubewa akasa, wasu irin hawaye masu zafin gaske ne suka zubo mai, wainda baisamu yinsu ba tuntuni, Ashe maganar da Ahmed kullum yake fadamai zata kasance gaskiya, Wato akwai Abinda Allah ya boye shiyasa ya cusa mai muguwar soyayyar Naziya wadda bai taba yarda da itaba domin yasan is prohibited, 

Yasha wahala yana kuma kan shan wahalar, zai iya rantsuwa da Al’qur ani yafi yayan shi son ta, Wanda baisan ya akayi soyayyar ta ta shiga zuciyar shi ba, how? when? Wani irin kuka yakeyi Am sorry yaya am sorry my brother da nasan zaka tafi kabarmin ita da na roki Allah ya cire min soyayyar ta ya barmin kai a rayuwa, Am sorry for loving your wife more than you brother, am sorry for feeling jealous idan kuna tare baka sani ba yaya, Inada kishin ta sosai yaya I use to cry behind door saboda zafin kishin ta, you are my brother but Ina kishin ganin ku tare, bansan ya akayi soyayyar ta ta shigeni ba, I love her more than the way you love her, I hate myself for that I swear to you, I control my feelings because of you. 

You’re dead because of hidden destiny, hawayen shi ya share tareda hadiye kukan, “I will make her happy yaya zancika maka burin ka, zanbata farin ciki fiyeda yanda Kayi mafarkin bata, zansata dariya fiyeda yanda take dariya idan kuna tare. Mikewa yayi ya zari key din hadaddiyar motar shi tareda goge fuskar shi da kyau ya fita cikin hanzari a falon da yabar mommy a nan ya same ta tana waya tana fadawa y’an uwan ta bakin labari, Modu ya rantse sai ya cakuda jinin ta da talaka…….. . ????

Previous page 1 2 3 4 5 6 7 8 9 10 11 12 13 14Next page

Related Articles

Leave a Reply

Back to top button