AUREN GADO Page 41 to 50

“Ruwan nonon kakesha? Fuskar ta a yamutse, dagowa yayi ya daga mata gira Alamar what? No be my property. “Na shanye ruwan…. Bare wannan mai dadin, wow baby zan rika taya yarona shan wannan sweet milk din, meyasa ni da nakesha ba ruwa sai yaro yazo ruwan kezuwa? Hmm bazan taba bari ruwan ya koma ba zaki dauki ciki ki haihu.
“Da gaske kakeyi ko wasa? “What? ” shan nonon. Tafada tana kallon shi cikeda son gano gaskiyar zuciyar shi, “of course am serious, in naga dama ma ma ba fura zansiyo ina gutsira inashan nonon ba.
Kyalkyale wa tayi da dariya y’an da yake magana da zuciyar shi daya, kwankwasa Kofar momy yasa ya zabura ” good night momyn ki zata fara fada na rufe mata kofa. “Zakazo ka bude ko sai ranka ya baci. Tafada da karfi cikin fada. Yayi saurin budewa ta tureshi ta shigo “bani hanya uwar me kakeyi harda rufe kofa don iya shege kabarni waje yarinya ta haihu yau ma bazaka daga mata kafa ta kwanta ta huta ba. “Haba momy biki fa takeyi mezanyi mata. “Fita don ubanka mara kunya. Tafada tana kokarin kaimai jifa saboda ya fassara ta, dariya yasa yana cewa “Allah ya barmin ke momy natafi nabarki da Ahmed da momyn shi, nayiwa d’an ki takwara. Fuskar ta ta Washe “Allah yayi Albarka ya raya Ahmed. Tana share hawaye da suke kokarin zubo mata. Naziya ma saida taji jikin ta yayi sanyi ta kalli yaron a zuciyar ta tace “Allah yasa kayi halin mai sunan.
Cikin kwanakin ba karamin gata da kulawa take samu a wurin Momy ba, harma da d’an gi, har malam yazo yaga Abokin shi Inna dai taki zuwa saboda Kara momy tayi tayi tace mezan zo inyi da wani miji bana bukata nabar miki Hajiya balkisu, tace toh nagode nikam ina son Abuna, su Aunty Raliya kullum sai sunzo zuwa yamma su tafi, angon k’arni baida sakat Yanzu saboda taron mutane a kullum, saidai yasa Shukrah ta kawo mai shi yaganshi uwar tayi tsadar gani,
Har zuwa ranar taron suna daya tara d’an gi da y’an uwa da Abokan Arziki, Wanda khaleel ya gwangwaje su da shatara ta Arziki Abin ba acewa komai sai sanbarka, momy ma bakaramin kudi ta ke kashewa little Ahmed ba Wanda sukewa lakani da Nur, domin shidin hasken zuciyar sune baki daya, harda sabuwar mota ya d’an karo mata, ranar suna, Ana tsaka da taron aka kawo mai ita, sai lokacin ya shigo cikin gidan duk da taron mutanen ya Kira Aunty Zarah yace ” please ku Aramin mai jegon minti biyu, momy ta fito da fada, ” kai wai baka ganin taron mutanen nan ka ratso kana wani neman ta mezata yimaka?
Dai dai tafito cikin Adon wani d’an kareren leshi mai shegen kyau da tsada tana walwali tasha kunshi kafafu da hannu ga wani head da aka nada mata ya zauna kamar wata sabuwar Amarya ba mai jego ba, kowa idanun shi ya koma kanta, harda uban gayyar, wani irin narkewa yaji zuciyar shi nayi ganin ta, zai iya rantsuwa ba wata mace kamar Matar shi a duniya, tuni aka fara kashe mata hotuna, kallon ta takeyi da wani irin sirri Wanda tuni ya fahimci itama tana kewar shi don haka bai damu da idanun mutane ba yafara takawa cikeda kasaita dajin yafi kowa sa’a ya matsa kusa da ita tareda rikota, ya ciro dalleliyar wayar shi ya mikawa Aunty yace “snap us Aunty. Akasa shewa domin bakaramin daceew sukayi da juna ba, ga shaddar jikin shi tayi Kala da tata, yaci hula tangaran, ita kanta tasan tasamu miji, yes she can shout out loud and say this is my husband, kowa yaji, ya mugun yimata kyau kullum Kara murjewa yakeyi, she really admire him, har wani kishi taji yana d’an tabata don akwai y’an mata na family dayawa a gidan datasan wata zata iya k’yasa mata miji, don haka ta rike Abinta kam,
D’an dukowa yayi a kunnen ta ” let go out side I have a surprise. Yajata suka fita ana binsu da guda tuni momy ta kauce tana farin ciki, duk da harabar gidan akwai motoci birjik bai hanata hango wannan farar motar sabuwa dal ba taji flowers da balloons a gabanta an manna sticker katuwa mai daukeda “For you my wife.
Kafin ta ce wani Abu ya d’an ka mata key din “tank mom nur. Tareda dora mata kiss a bakinta, wasu irin hawaye na farin ciki suka fara gangarowa a fuskar ta, takasa cewa komai domin bakaramin kaya ya d’an karo masu ba, harda gwala gwalai na kece raini da batasan ta ina zata fara sakasu ba, Rungume shi tayi tareda cewa ” ina kakeso insaka kaina saboda farin ciki this is too much my love.
Kara rungume ta yayi yana murmushi mai cikeda farin cikin my love data kirashi, ” kin biya ni yanzu yanzu for calling me your love baby, I want you to love me more only me, ki nuna min so ki tarai raye ni ki maidani d’an lelenki that’s all what I want from you.
“I love you dadyn Nur,zan nuna maka duniya ma zata shaida hakan because I really do love you, you are the best husband the best father and the best son, am very proud of you Allah yakara Arziki da budi yakuma tsaremin kai.
Dagata yayi cak yana juyi da ita duk da mutane na yawo a wurin ko ajikin shi, ” Wayyo dadi kice inrika kawo miki surprise domin insamu Addu’a da wainnan sweet sweet words din. “Kai son irin wannan Abu a idanun jama’a? “Kai Aunty wallahi keda momy kunason hana ruwa gudu, sauka tayi cikin jin kunyar Aunty Zarah tace “Aunty nayi sabuwar mota. Tasa guda tareda cewa Masha Allahu Allah yasa Albarka, gaba yayi yabarsu ganin duk Anfito ana tayata murna, tabi bayan shi da Kallo, she feels like following him ganin ya shige gidan su,
Yanzu take blaming kanta na kin bashi kulawa sosai duk da suna gida daya batasan wane irin hali yake ciki ba, tasan momy na kulada cikin shi, Amma tasan halin shi ta gefen rashin hakuri ta wani wurin gashi bai samu damar complain ba,
Haka taron sunan ya ci gaba anci ansha sun samu sha tara ta Arziki, har zuwa lokacin da kowa ya watse yarage daga momy sai Shukrah domin har naman sunan ma da rana aka soyeshi aka rabe Abunka da manya, nidai nasamu naci hanji domin a cikin naman suna ba Abinda yakai hanji dadi, don haka ni acan na makale.
Tun karfe tara momy tace Shukrah ta koma dakin ta wurin Naziya tanaso tasha magani ta kwanta tagaji da yawa yau. Naziya tace “gaskiya momy kije ki huta tunda akayi haihuwar nan bakya wani hutawa. “Toh miji fa nayi badole ba, nasa sun kai muku duk kayan da kuka samu gidanku kafin sutafi. “Toh Allah yakara girma momy da lafiya. “Amen. Ta yiwa Nur Addu’a ta Kara rufeshi ta fita, tana fita Naziya ta mike tace “Shukrah zanje wurin Baban shi don Allah karkiyi bacci ya farka yayita kuka, har momy tagano bani. “Hhhhh ba ruwana idan nayi bacci yayita bare baki. “Don Allah karkiyi zandawo zuwa karfe goma nan da thirty minutes kinji. “Toh kiyi sauri. Matsawa tayi ta gyara jikinta da kyau tareda feshe jikinta da kamshi ta zunbula katon hijab ta sudada ta fice.
A zaune yake yana kallon hotunan su na dazu yana murmushi, kallon bangon falon yayi inda ya jera hotunan su a bango daya na farko nashi na tsakiya Nur sai nata a gefe, tunda aka haifeshi yamai wannan hoton yasa A gidan, bata ma sani ba,
“Allah ya jikan takwarar ka, yaya Ahmed banda kamar ka duk duniya kayimin komai kana raye katafi kabarmin Abinda zantuna dakai a kullum, Naziya itace kyautar da tafi komai da kayimin a duniya, look at your name sake he is just like you. Yafada yana danna hoton Nur ya bawa wayar kiss “I love you my family, I miss your mother soo much my son har bana iya bacci saboda kewarta. Yaji anturo kofa, a hankali yayi saurin juyawa, zabura yayi tsaye “baby!!!!, ist really you? Hijabin ta tacire tareda ratayawa a jikin hanger ta fara takowa cikin y’anga domin Kara siyemai zuciya. “Yeah nice ko sai na nemi izinin ina son ganin mijina? Jikin shi na rawa saboda tsananin farin ciki Da murna ya karaso da gudu ya rungume ta. “Wow my baby am very happy for this special visit, were is my son? ” nabar shi da Shukrah nace bari inzo in shayar da dadyn shi shima tunda shi ya koshi. Saurin dagowa yayi ya zuba mata ido domin kalmar ta tasa yaji tsigar jikin shi na wani irin mikewa da yin zillo, yafara kallon rigar bacci dake jikin ta baka ta lafe saboda silk, kirjin nan dake cike sun wani irin tsone mai ido saboda kunburi, cikin wani irin rawar murya yace “da gaske baby you are going to feed me your special milk? “Yes if you really want t….. “Ofcos I love too ya sunkuceta sai kuryar dakin, sai samata Albarka yakeyi, sanin yayi matukar kewar ta ta dage tabashi taimako sosai har yasamu natsuwa, yana lafe a jikinta sai kissing dinta yakeyi ta ko Ina yace ” tank you baby, ina momy kika zo nan? Kara rungume shi tayi tace “tayi bacci da wuri kasan tagaji dayawa, nabar wa Shukrah na gudo nan. “Naji dadi sosai baby ta damu dani sosai. “Bari in koma kar ya tashi yafara kuka Asiri na ya tonu. Tashi yayi ya zauna tareda kallon y’an take kokarin mayarda rigar ta, “kiyi wanka mana. “Sai naje can banda pad inna cire anan. “Wai yaushe wannan abun zai dauke ne yaufa sati daya. “Kai ance sai mutum yayi Arba’in fa. “What da sake fourty? “Bakowa bane fa ni bansan nawa kwana nawa zaiyi ba, “please idan ya tafi kifadamin I can’t wait, kinga yanzu kinki bari ko gogawa inyi kadan am missing it “you are shameless. Tafada tana direwa a gadon da gudu, yabita….. ????