AZIZA DA AZIMA 1-10

“Jarman Macizai ba wannan na yankin al’karyan jimo ba?”
Baffa ya ce
“Eh shi dai, ya ma amsa da gobe zai zo, zai taho da ruwan wani magani wanda za a ba wa kowa ya sha wanda hakan ne zai bayyana waye ba mutum ba a cikin al’umman yankin kwana, kin san titsiyeni aka yi a kan su Azima da Aziza, wai yarana basu abu irin na mutane, shi ne za ayi wannan gwajin” wani firgita Azima har ma da Azizan suka yi, suka kalli juna, ba tare da iyayensu sun san halin da suke ciki ba,tuni idon Azima ya kara komawa blue sosai, nan ta kalli fatar jikinta ta ga ta fara zama blue da sauri ta miƙe ta shige bukka, ita ma Azizan tashi ta yi, Hajja ta ce
“Dan kawai yara basu mu’amala da kowa, sannan idonsu ba baƙi ba shikenan sai a saka mun yara a gaba?” Baffa ya ce
“Amma kin san dai har da maganar aurar dasu, bisa al’ada ta wannan yanki namu yara da sun shekara 11 ake aurar dasu, yanzu kuma su Azima da Aziza su na da shekara 15 kin ga kuwa dole a saka musu ido mun ƙi aurar dasu, ga shi kullum Arɗo sai ya min magana” tabe baki Hajja ta yi ta ce
“Allah ya kyauta amma ai aure lokaci ne” ta miƙe taje duba ruwan tuwonta.
A bukka kuwa sadda Azima ta shiga nan kasanta ya koma macijiya har sai da ta cika bukka din, kalar fatarta ta koma blue, Aziza ce ta biyo bayanta ta ce
“Azima ki koma dai-dai kar Hajja ta shigo ta ganki haka fa?”
A hautsine Azima ta ce
“Dole na kashe Jarman Macizai! Nayi alkawari sai na ga bayan wanda yake shirin ya san su waye mu na asali!.”
????????????????????
*HANZARTA BIYAN NAIRA ƊARINKI KACAL???? DAN JIN CAKWAKIYAR DAKE CIKIN WANNAN LITTAFI, MOMYN AHLAN TANA KAUNAR MASOYANTA*????
COMMENTS
AND SHARE
BY MOMYN AHLAN????????
[4/13, 10:12 AM] Mom Ahlan: ????????????????????????????????????
????✨ *AZIMA DA AZIZA*????✨
(???? _Macizai ne_????)
MALLAKAR.
*ZAHRA ABDUL(MOMYN AHLAN)*
SAHIBAR KAINUWA.
Littafin kuɗi, naira ɗari kacal dan masoyana, turo da kudinki ta wannan acct din
0096035983 balaraba hassan accees bank, ko kuma hoton kati ta wannan lambar 08165550116, pls ban da vtu.
*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*
*????KAINUWA WRITERS✍???? ASSOCIATION*????????
”'{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}”’
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*domin shiga shafin mu na Bakandamiya danna nan*????????
https://bakandamiya.com/group/71/kainuwa-writers-association
*____________________________________*
*MARUBUCIYAR.*
1- _HALITTA DAGA ALLAH NE._
2- _GUDU A JEJI._
3- _SHUHADA._
4- _NIDA ƘANNEN MIJINA._
5- _WA’YA KASHE ZAHRA’U?(#200)._
6- _COLONEL UBAIDULLAH._
7- _ITA CE ZUCIYATA(#200)._
8- _SAMIMA (MACIJIYA CE._
9- _GAWURTACCEN SOJA(#300)._
10- _DA NA SANI NA._
11- _BADAWIYYAH_
12- _DEPUTY SUPERINTENDENT OF POLICE (DSP ALIYU HAIDAR)_
Now
13- _AZIMA DA AZIZA (MACIZAI NE????)_
????????????????????
*FREE..*
????️==3️⃣↪️4️⃣
“Ba ki da hankali ne Azima? Jarman macizai za ki kuma kashewa? To bari kiji! Kin ga wannan kashe-kashen shi zai sa a gane su waye mu, dan Allah Azima karki kashesa, bana son kisan da kikeyin nan” Aziza ta faɗa tana bin Azima da kallo, cikin huci Azima ta ce
“To tsammaninki me zai faru? Idan har jarman macizai ya kawo maganin gwaji dan a tabbatar da su waye ba mutane ba? Ke a tunaninki mutanen yankinmu zasu barmu a raye ne? Ina kashemu zasu yi, dan haka kafin hakan ta kasance ni nan zan kashe Jarman Macizai kuma ba ki isa ki hanani ba” Azima ta fada tana komawa mutum tare da ficewa a bukkan, tana fitowa hanyar waje ta nufa Hajja ta ce
“Azima ina kuma zaki je bayan baku jima da shigowa gidan ba?” kafin Azima ta yi magana Baffa ya fito daga kewaye yana fadin
“Ban hanaku fita sakakan ba Azima? Ina za kije?” cikin in-ina da kame-kame ta ce
“Zan duba abu na ne a nan waje” Baffa ya ce
“Ba za ki duba ba koma ciki” haɗe rai sosai Azima ta yi tare da yiwa Baffa wani irin kallo ta koma fuuu, da kallo Baffa da Hajja suka bi Azima, jiki a sanyaye Baffa ya koma ya zauna, tunanin abunda ya faru shekara ashirin shike dawo masa kwakwalwa, kar dai ace fansar da *Banju ya ce zai dawo ya daukar wa kanwarsa Bahula da kansa shine ya dawo dauka kan yaransa!?* Haqiqa shima zuciyarsa ta fara yi masa saqe-saqe a kan yaransa ba cikakkun mutane bane amma baya so zarginsa ya tabbata, rintse ido ya yi yana karanto kalmar “Innalillahi wa inna ilayhirrajiun!” kallonsa Hajja ta yi ta ce
“Lafiya kuwa Baffan Azima da Aziza?”
“Haqiqa Jumala ina jin tsoro!”
“Tsoron me fa Baffan yan biyu?”
“Inajin tsoron furucin Banju lokacin da zan kashesa maganarsa ta karshe, ko kin manta da kalman da ya ce….” Baffa bai karasa ba Hajja ta dakatar da shi
“A’a Baffan Azima da Aziza! Karka yiwa yarana baki! Taya wa inda suka mutu shekara ashiri a ce sun dawo? Azima da Aziza dai ni na haifi yarana! Kuma ni mutane na haifa, kwata-kwata wannan maganar bai kamata ace ya fito daga bakinka ba, kai da kanka ka fara zargin yaranka to ba dole jama’ar gari ma su fara zarginsu!” Hajja ta faɗa cikin sosuwar rai, girgiza kai Baffa ya yi ya ce
“Ba haka bane Jumala, amma dai jikina ya yi sanyi! Allah ya kaimu gobe jarman macizai zai zo ya warware komai” ita dai Hajja ba ta sake cewa kala ba, illa aikinta da ta ci gaba da yi, Azima kuwa tana saman bukka a macijiya tana jin maganganun Baffa, a ranta take ayyana yadda zata kawar da Baffa!.
????????????????????
Washe gari tun kafin garin Allah ya waye Azima ta sulale ta fice, hanyar yankin Jimo dai-dai kan layin shigowa yankin kwana a kan wata babbar bishiya ta kwanta ta nannaɗe idonta sun kara komawa blue, tana jiran isowar jarman macizai, awanta kusan uku kafin ta hangosa, wani murmushi ta yi mai tattare da zallar mugunta kafin ta sauko ta koma mutum, tsayuwa ta yi bayan ya gama shigowa yankin kwana.
Yana kan tafiya akan dokinsa a hankali ya hangi budurwa tsaye a hanyarsa,magana ya hau mata amma shuru, tana tsaye da lullubi, saukowa ya yi a kan dokin ya tunkaro inda take tsaye, sai da ya zo kusa da ita kafin ya ce
” *MUTUM KO ALJAN!?”*
Murmushi ta yi tana lankwasa harshe ta ce
” *RUWA BIYU!”* sannan ta juyo ta yaye mayafin da ta lullube jikinta ta jefar, jarman macizai na ganin idonta ya yi saurin ja da baya, dariya Azima ta sheqe da shi ta ce
“Na ga bai kamata ace kasha wahala ba wajan zuwa gwajin wanene wanda ba mutum ba a wannan yankin! Gani na zo da kaina dan dakatar da kai! Ba zaka shige ba sannan ba zaka koma ba!” da sauri jarman macizai ya yi baya dan dauko kayan aikinsa tsalle daya Azima ta yi ta zama macijiya ta cakume jarman macizai nan suka hau kokawa, duk yadda yaso kwace kansa daga hannun Azima ya kasa, daga karshe ta rufesa da sara, sosai ta yi masa jina-jina sai da ta ga ya daina mutsu-mutsu sannan ta sakesa ta sulale ta yi hanyar rafin jimulo, tana isa rafin ta hau kyalkyala dariya nan ta zube kusa da rafin.
????????????????????
A cikin unguwa kuwa ana nan ana jiran isowar jarman macizai, tun ana sa ran ganinsa takwas har goma, inda a karshen mai unguwa ya ce aje a duba ko lafiya a binciki hanya aka tura mutum uku.
Ai kuwa can suka gano gawar jarman macizai a yashe cikin jini, cikin tashin hankali suka juya da mugun gudu suka koma suka sanar da jama’ar gari an kashe jarman macizai.